Sashe 42
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki bi ta aduk yanda tazo tunda Kinga ba'a hankalinta take ba, kwakwalwarta ya koma na yarinya me shekara takwas a duniya,ki bita a hakan se mun fi samun saukin komai,karki yi kokarin tuna mata abubuwan da suka faru, hakan ze sa ta fara ganin flash wanda hakan zesa ta koma wata matsalar kuma daban.shi wannan matsalar nata baya bukatar gaggawa,kulawa da kuma magani masu kyau da manyan allurai take bukata.zan turo mata da chocolate anjuma".
"Shikenan ya Saghar zan kiyaye"a haka suka rabu shi ya fice ita kuma ta shiga bedroom din,samun Asmita ta yi zaune a tsakiyar gado daga ita se towel a daure.
Tsayawa kawai ta yi,tana kallonta har yanzu mamaki be fita a ranta ba,wai yau Asmita ce, a haka kai gaskiya rayuwa abar tsoro ne.
"My Jerry waya baki chocolate!?"ta mata tambaya tana zama a gefenta.
Washe baki Asmita ta yi seda ta ɗan yi jim kamar wata me tunani can kuma ta ce "me kyau ne yabani"dariya ta yi wato Saghar din ne me kyau,hmm lallai kam gaskiya ta faɗa domin gaba daya mazajen gidan suna da matukar kyau me tafiya da hankali uwa uba suna shigen kama da juna,haka yan matan ma.
Surutu Asmita take ta mata,ita a hakan wai labari take bayarwa,wani maganar dakyar Sabriyah take ganewa.
Wanka masu kula da ita suka mata,suka shiryata cikin dogon riga na material ɗinkin play,ta yi kyau sosai duk da akwai rama a tare da ita, dankwali za'a daura mata,ta da ka tsalle tace bata san zancen ba,ita sede a raba gashinta gida biyu a mata fakin haka kuwa sukayi mata da dogon gashinta.
Su Rameesa ne suka shigo dakin su hudu,banda Zoya dake part din Ammuh.iklas hannunta na dauke da abincin da Ammi ta turo ma Asmitan.
"Hi! Asmita yakike?"su ka faɗa tare, tana kwance ta yi filo da cinyar Sabriyah,dago kai ta yi tana kallon su,ta kuma ƙi musu magana,"my Tom inyi musu magana!?"ta tambayi Sabriyah,gyada mata kai ta yi.
"Ku ma zakuje lilo din ne!?,ni an min wanka an yi mini kwalliya ma na shirya me kyau nake jira" "eh mana duk zamuje, yanzu ki fara cin abinci tukun nan"Iklas ta yi magana tana buɗe mata plat din abincin,chips ne da miyar hanta se soyayyen kwai.
Maƙe kafaƙa ta yi alamar bazata ci ba,rike hannunta Sabriyah ta yi tana shagwabe fuska itama"to shikenan karki ci din,ni kuma bazan je lilo din ba tunda abin hakane"da sauri ta jawo plat gabanta dan bataso Sabriyah ta ce bazata je ba,"yauwwa ko kefa"ta faɗa tana fara bata abincin abaki,su Umaisha bakaramin burgesu sukayi ba,duk da ya kasance Asmita bata cikin hankalinta amma kaunar dake tsakanin su be gushe a wajenta ba,tana bata abinci abaki tana yi mata hira,suna dariya.
Tayasu hira sukayi har lokacin sallah Azhar ya yi suka tashi suje suyi.
Ya yi saura su biyu a dakin nurses dinma sun fita, Asmita bacci ya dauke ta,in ta ga Asmita sanyi takeji a ranta,yanzu mutane biyu ne ya yi saura ta ji halin da suke ciki, kwana biyun nan tana yawan mafarkin anty Teema tana ce mata yaushe zata dawo se in tana kokarin bata amsa se ta farka.
Se kuma Fu'ad da batama san ta ina zata fara binciko shi ba,fatan ta ɗaya shine Allah yasa yana cikin koshin lafiya.wayarta yana a dakin su na afafa,lokacin da suka fito ita da Asmita zuwa wajen Taheer, basu fito da wayoyinsu ba,ga shi bata rike number Fu'ad akanta ba ɓalle ta kirashi.
Kano state
Falo ne me girma,me kyawun tsari gwanin burgewa, mutane uku ne a ciki biyu mata se na miji guda daya, dayar macen Mahaifiyar namijin da macen ne saboda kamar da sukeyi.
Fuskanta dauke da tarin damuwowi dan banace damuwa daya ba,ta kalli na mijin gabanta ta ce "Taheer har yanzu shuru babu labarin ya'yanku Lameer, shikenan ya bata kenan?, shikenan yanzu a kasar nan daga ka zama me gaskiya da riko da amana se anyi kokari an ga bayan ka?,sun salwantar da rayuwar Lameer".
Taheer shuru ya yi yana sauraran hajiyar ta su,tun lokacin da babban ya'yansu Barrister Lameer ya bata suke cikin wani hali na rashinsa,sun neme shi har sun gaji amma shuru babu labarin sa.
"Hajiya ni abun daure mini kai yake yi,su waye suke neman kashe ya Lameer,meye abinda suke bukata a tare dashi, gaskiya duniya yanzu babu gaskiya.ranar da mukayi waya dashi na ƙarshe shine ranar da ya ce min yana Lagos na yi farin ciki sosai da jin haka nan nima nake sanar dashi ina Lagos, se ya ce mu haɗu a wani restaurant akwai abinda yake so mu tattauna.mun gama waya dashi se nazo wajen yarinyar danake baku labarin inason in aureta, Asmita,ban bata lokaci a gun nata ba, na koma a hanyata na ta kiran wayarsa baya shiga har izuwa rana me kama ta yau babu labarin ya Lameer".
Yana magana ne cikin muryar me ban tausayi,domin shi da dan uwansa akwai shakuwa me karfin gaske,wasu ma har tunanin yan biyu ne su,komai din su tare aikine kawai kowa da irin nasa, Lameer lawya ne,shi kuma Taheer pilot ne,matukin jirgin sama.
Yar karamar kanwarsu me suna yusra, kyakyawa da ita daga ganin ta bazata wuce 17 yrs ba, ta yi tagumi tana kallon Hajiyar tasu da ya'yanta,dama tun can ita ba gwanar magana bace,da wannan abun ya sake faruwa kuma se ta sake zama shuru_shuru.
Hajiya ta ce"ya lamarin Asmitar da kake magana an sameta ne!?" "Ah ah Hajiya itama shuru"girgiza kai ta yi,jim kaɗan kuma ta furta"Sunan budurwar kan nan in naji se na tuna da kanwarka"
"Nima haka Hajiya".
Katsina state
Yau de Allah ya yi wa Hajjatiye ikon zuwa Nigeria,tana gidan mom Rumanatu,tunda ta zo ta sasu agaba se de su wuce Maiduguri ita ba zata iya zama anan ba, Abu Sufyan ne ya samu ya shawo kanta ta yarda kan cewa gobe da safe zasu tafi dama jiran su Abbie suke yi su dawo kuma su din ma yau da rana Flight din su ze yi landing.
Iftisan ba wani shiri suke yi da Hajjatiye ba,ba ta ma zama kusa da ita,domin inta zauna kusa da Hajjatiye tas take kare mata zagi bata rage mata, Jaleelah ce yar gaban goshinta.
Saukowa Ashman ya yi cikin shirin zuwa wajen aiki ya tadda su zaune a falo,gaida su ya yi yasa kai yafita,rike haɓa Hajjatiye ta yi ta kalli mom Rumanatu,"nikam Rumanatu wa'yannan sabga_sabgan balagaggun kam me kuke nufi da har yanzu baku musu aure ba!?,ki duba yaron nan da ya kamata ace yanzu yana da mata biyu yara takwas amma ace yana nan yana yawo fikau fiyau ba mata!"gyara zama mom Rumanatu ta yi ta soma magana"to Hajjatiye ya za muyi dasu yaran nan sunki maganar aure kwata_kwata,ko jiya seda mukayi wannan maganar nida ya'ya Isma'il,haka su Tajuddeen din ma shuru babu wacce yake da budurwa balle a yi maganar su dedeta maganar aure".
Gyara daurin dankwalin kanta da ta tokaro shi gaba ta yi, ta ce"ai duk ku kuka sangarta su, haba wannan abun kunya ne yara daga masu shekara ashirin da bakwai se zuwa da takwas amma a ce ba sa maganar auren to kode basu da lafiya ne!?,in yaso ni da kaina zan samo musu maganin karfin mazantaka ne!?,yoooo ina dalili,ga yaran matan ma duk sun balaga kalli kirjin yaran nan naki duk ya gama cika da kirgen dangi,har ya fara kwanciya basuyi aure ba". Hajjatiye ce ke magana amma mom Rumanatu ce take jin kunya dama Hajjatiye ita babu ruwanta ko a gaban waye duk maganar da yazo bakinta se ta fadeta sede ta barka da jin kunya,dan ma Allah yasa su Jaleelah duk suna bedroom din su.
"Shikenan Hajjatiye gobe de in mun je Maiduguri se a yi maganar".
Haka ta tashi ta shiga kitchen ta yi mata abincin da takeso da kanta.
"Kasan yanda rayuwar su yake da mahimmanci a wajena kuwa!?,kasan yanda nakeson su ne?, dalilin son da nakeyiwa Sabriyah yasa na fara kaunar Asmita jinta nakeyi kamar kanwata,da nace ku sace ta,ta baku memory in kuma baya wajanta ku sa ta ta faɗa muku a inda yake, bawai ku kusan kasheta da cocaine ba,common yanda zaku yi aikin kuma baku sani ba,bayan kunyi laifin nan kuka bari har sojojin Tajuddeen suka gano inda kuke suka kai muku hari, kun cancanci tukuici daga wajena saboda babu wanda yake wargaza mini shirina ban bashi tukuici ba"Fu'ad ne agaban Samuel da kuma dayan da suka kamo Asmita su kadai ne suka tsira daga farmakin da su major Marry suka kai musu,nan take suka zo wajen Fu'ad din.
Magana yake musu yana nuna su da bindiga daga ganinsa kasan ranshi ya yi muguwar ɓaci,har kamanin sa ya sauya ya koma boss,bazaka ce shi ne wannan Fu'ad da Asmita da Sabriyah suke yabo ba,wannan kamilin Fu'ad,bawan Allah da babu ruwansa.
A kirji ya harbi dukkansu biyu suka fadi a mace.durkusawa ya yi, ya dangwali jinin Samuel da hannu ya shinshina a hancin sa,wani irin nannauyan ajiyar zuciya ya sauke,yana jijiga kansa cikin nishadi miƙewa ya yi, ya fara rawa a wajen kamar mazari lokaci daya kuma ya dakata ya nutsu,ya sauya fuska izuwa abin tausayi kamar mutumin kirki,
Sunkuyar da kanshi ƙasa ya yi "yanzu shikenan kun mutu!?,bazaku taɓa dawuwa ba,ahhhhhh! babu abinda yakai jini kamshi,inajin dadi da tsintar kaina a farin ciki a duk lokacin da naga ina kashe mutane kururuwar neman taimako da kuma ganin zallan tsoro a cikin ƙwayar idon su yana ƙarfafa mini guiwa"ya yi maganar yana wani juyi.
Ya sa'ke cewa"my Sabriyah karki damu ina nan zuwa gareki,ke din tawa ce,zanyi faɗa da kowa domin ganin na kwato ki,my Sabriyah da taimakon ki zan ga bayan lieutenant general Tajuddeen Bishara"ya gama maganar yana kecewa da mahaukaciyar dariya.
Tabbas Fu'ad cikekken hatsabibin mutum ne da gane inda ya dosa se Allah da kuma mutum wanda ya fisa kaifin basira,ya wuce duk tunanin me tunani, yana da fuskokin da bazakayi tunanin ze iya yin muguwar muguntar da yake aikatawa ba,in ya juya mutumin kirki zakayi tunanin wani malami ne wanda yasan Allah yasan addini,amma in ya koma hatsabibinsa to ko shedan haka ya ganshi ya barsa,duk wanda ya shiga tarkon Fu'ad tofa sede ya yi addu'ar Allah ya kwacesa daga sharrinsa shine kawai.
"Shikenan ya Saghar zan kiyaye"a haka suka rabu shi ya fice ita kuma ta shiga bedroom din,samun Asmita ta yi zaune a tsakiyar gado daga ita se towel a daure.
Tsayawa kawai ta yi,tana kallonta har yanzu mamaki be fita a ranta ba,wai yau Asmita ce, a haka kai gaskiya rayuwa abar tsoro ne.
"My Jerry waya baki chocolate!?"ta mata tambaya tana zama a gefenta.
Washe baki Asmita ta yi seda ta ɗan yi jim kamar wata me tunani can kuma ta ce "me kyau ne yabani"dariya ta yi wato Saghar din ne me kyau,hmm lallai kam gaskiya ta faɗa domin gaba daya mazajen gidan suna da matukar kyau me tafiya da hankali uwa uba suna shigen kama da juna,haka yan matan ma.
Surutu Asmita take ta mata,ita a hakan wai labari take bayarwa,wani maganar dakyar Sabriyah take ganewa.
Wanka masu kula da ita suka mata,suka shiryata cikin dogon riga na material ɗinkin play,ta yi kyau sosai duk da akwai rama a tare da ita, dankwali za'a daura mata,ta da ka tsalle tace bata san zancen ba,ita sede a raba gashinta gida biyu a mata fakin haka kuwa sukayi mata da dogon gashinta.
Su Rameesa ne suka shigo dakin su hudu,banda Zoya dake part din Ammuh.iklas hannunta na dauke da abincin da Ammi ta turo ma Asmitan.
"Hi! Asmita yakike?"su ka faɗa tare, tana kwance ta yi filo da cinyar Sabriyah,dago kai ta yi tana kallon su,ta kuma ƙi musu magana,"my Tom inyi musu magana!?"ta tambayi Sabriyah,gyada mata kai ta yi.
"Ku ma zakuje lilo din ne!?,ni an min wanka an yi mini kwalliya ma na shirya me kyau nake jira" "eh mana duk zamuje, yanzu ki fara cin abinci tukun nan"Iklas ta yi magana tana buɗe mata plat din abincin,chips ne da miyar hanta se soyayyen kwai.
Maƙe kafaƙa ta yi alamar bazata ci ba,rike hannunta Sabriyah ta yi tana shagwabe fuska itama"to shikenan karki ci din,ni kuma bazan je lilo din ba tunda abin hakane"da sauri ta jawo plat gabanta dan bataso Sabriyah ta ce bazata je ba,"yauwwa ko kefa"ta faɗa tana fara bata abincin abaki,su Umaisha bakaramin burgesu sukayi ba,duk da ya kasance Asmita bata cikin hankalinta amma kaunar dake tsakanin su be gushe a wajenta ba,tana bata abinci abaki tana yi mata hira,suna dariya.
Tayasu hira sukayi har lokacin sallah Azhar ya yi suka tashi suje suyi.
Ya yi saura su biyu a dakin nurses dinma sun fita, Asmita bacci ya dauke ta,in ta ga Asmita sanyi takeji a ranta,yanzu mutane biyu ne ya yi saura ta ji halin da suke ciki, kwana biyun nan tana yawan mafarkin anty Teema tana ce mata yaushe zata dawo se in tana kokarin bata amsa se ta farka.
Se kuma Fu'ad da batama san ta ina zata fara binciko shi ba,fatan ta ɗaya shine Allah yasa yana cikin koshin lafiya.wayarta yana a dakin su na afafa,lokacin da suka fito ita da Asmita zuwa wajen Taheer, basu fito da wayoyinsu ba,ga shi bata rike number Fu'ad akanta ba ɓalle ta kirashi.
Kano state
Falo ne me girma,me kyawun tsari gwanin burgewa, mutane uku ne a ciki biyu mata se na miji guda daya, dayar macen Mahaifiyar namijin da macen ne saboda kamar da sukeyi.
Fuskanta dauke da tarin damuwowi dan banace damuwa daya ba,ta kalli na mijin gabanta ta ce "Taheer har yanzu shuru babu labarin ya'yanku Lameer, shikenan ya bata kenan?, shikenan yanzu a kasar nan daga ka zama me gaskiya da riko da amana se anyi kokari an ga bayan ka?,sun salwantar da rayuwar Lameer".
Taheer shuru ya yi yana sauraran hajiyar ta su,tun lokacin da babban ya'yansu Barrister Lameer ya bata suke cikin wani hali na rashinsa,sun neme shi har sun gaji amma shuru babu labarin sa.
"Hajiya ni abun daure mini kai yake yi,su waye suke neman kashe ya Lameer,meye abinda suke bukata a tare dashi, gaskiya duniya yanzu babu gaskiya.ranar da mukayi waya dashi na ƙarshe shine ranar da ya ce min yana Lagos na yi farin ciki sosai da jin haka nan nima nake sanar dashi ina Lagos, se ya ce mu haɗu a wani restaurant akwai abinda yake so mu tattauna.mun gama waya dashi se nazo wajen yarinyar danake baku labarin inason in aureta, Asmita,ban bata lokaci a gun nata ba, na koma a hanyata na ta kiran wayarsa baya shiga har izuwa rana me kama ta yau babu labarin ya Lameer".
Yana magana ne cikin muryar me ban tausayi,domin shi da dan uwansa akwai shakuwa me karfin gaske,wasu ma har tunanin yan biyu ne su,komai din su tare aikine kawai kowa da irin nasa, Lameer lawya ne,shi kuma Taheer pilot ne,matukin jirgin sama.
Yar karamar kanwarsu me suna yusra, kyakyawa da ita daga ganin ta bazata wuce 17 yrs ba, ta yi tagumi tana kallon Hajiyar tasu da ya'yanta,dama tun can ita ba gwanar magana bace,da wannan abun ya sake faruwa kuma se ta sake zama shuru_shuru.
Hajiya ta ce"ya lamarin Asmitar da kake magana an sameta ne!?" "Ah ah Hajiya itama shuru"girgiza kai ta yi,jim kaɗan kuma ta furta"Sunan budurwar kan nan in naji se na tuna da kanwarka"
"Nima haka Hajiya".
Katsina state
Yau de Allah ya yi wa Hajjatiye ikon zuwa Nigeria,tana gidan mom Rumanatu,tunda ta zo ta sasu agaba se de su wuce Maiduguri ita ba zata iya zama anan ba, Abu Sufyan ne ya samu ya shawo kanta ta yarda kan cewa gobe da safe zasu tafi dama jiran su Abbie suke yi su dawo kuma su din ma yau da rana Flight din su ze yi landing.
Iftisan ba wani shiri suke yi da Hajjatiye ba,ba ta ma zama kusa da ita,domin inta zauna kusa da Hajjatiye tas take kare mata zagi bata rage mata, Jaleelah ce yar gaban goshinta.
Saukowa Ashman ya yi cikin shirin zuwa wajen aiki ya tadda su zaune a falo,gaida su ya yi yasa kai yafita,rike haɓa Hajjatiye ta yi ta kalli mom Rumanatu,"nikam Rumanatu wa'yannan sabga_sabgan balagaggun kam me kuke nufi da har yanzu baku musu aure ba!?,ki duba yaron nan da ya kamata ace yanzu yana da mata biyu yara takwas amma ace yana nan yana yawo fikau fiyau ba mata!"gyara zama mom Rumanatu ta yi ta soma magana"to Hajjatiye ya za muyi dasu yaran nan sunki maganar aure kwata_kwata,ko jiya seda mukayi wannan maganar nida ya'ya Isma'il,haka su Tajuddeen din ma shuru babu wacce yake da budurwa balle a yi maganar su dedeta maganar aure".
Gyara daurin dankwalin kanta da ta tokaro shi gaba ta yi, ta ce"ai duk ku kuka sangarta su, haba wannan abun kunya ne yara daga masu shekara ashirin da bakwai se zuwa da takwas amma a ce ba sa maganar auren to kode basu da lafiya ne!?,in yaso ni da kaina zan samo musu maganin karfin mazantaka ne!?,yoooo ina dalili,ga yaran matan ma duk sun balaga kalli kirjin yaran nan naki duk ya gama cika da kirgen dangi,har ya fara kwanciya basuyi aure ba". Hajjatiye ce ke magana amma mom Rumanatu ce take jin kunya dama Hajjatiye ita babu ruwanta ko a gaban waye duk maganar da yazo bakinta se ta fadeta sede ta barka da jin kunya,dan ma Allah yasa su Jaleelah duk suna bedroom din su.
"Shikenan Hajjatiye gobe de in mun je Maiduguri se a yi maganar".
Haka ta tashi ta shiga kitchen ta yi mata abincin da takeso da kanta.
"Kasan yanda rayuwar su yake da mahimmanci a wajena kuwa!?,kasan yanda nakeson su ne?, dalilin son da nakeyiwa Sabriyah yasa na fara kaunar Asmita jinta nakeyi kamar kanwata,da nace ku sace ta,ta baku memory in kuma baya wajanta ku sa ta ta faɗa muku a inda yake, bawai ku kusan kasheta da cocaine ba,common yanda zaku yi aikin kuma baku sani ba,bayan kunyi laifin nan kuka bari har sojojin Tajuddeen suka gano inda kuke suka kai muku hari, kun cancanci tukuici daga wajena saboda babu wanda yake wargaza mini shirina ban bashi tukuici ba"Fu'ad ne agaban Samuel da kuma dayan da suka kamo Asmita su kadai ne suka tsira daga farmakin da su major Marry suka kai musu,nan take suka zo wajen Fu'ad din.
Magana yake musu yana nuna su da bindiga daga ganinsa kasan ranshi ya yi muguwar ɓaci,har kamanin sa ya sauya ya koma boss,bazaka ce shi ne wannan Fu'ad da Asmita da Sabriyah suke yabo ba,wannan kamilin Fu'ad,bawan Allah da babu ruwansa.
A kirji ya harbi dukkansu biyu suka fadi a mace.durkusawa ya yi, ya dangwali jinin Samuel da hannu ya shinshina a hancin sa,wani irin nannauyan ajiyar zuciya ya sauke,yana jijiga kansa cikin nishadi miƙewa ya yi, ya fara rawa a wajen kamar mazari lokaci daya kuma ya dakata ya nutsu,ya sauya fuska izuwa abin tausayi kamar mutumin kirki,
Sunkuyar da kanshi ƙasa ya yi "yanzu shikenan kun mutu!?,bazaku taɓa dawuwa ba,ahhhhhh! babu abinda yakai jini kamshi,inajin dadi da tsintar kaina a farin ciki a duk lokacin da naga ina kashe mutane kururuwar neman taimako da kuma ganin zallan tsoro a cikin ƙwayar idon su yana ƙarfafa mini guiwa"ya yi maganar yana wani juyi.
Ya sa'ke cewa"my Sabriyah karki damu ina nan zuwa gareki,ke din tawa ce,zanyi faɗa da kowa domin ganin na kwato ki,my Sabriyah da taimakon ki zan ga bayan lieutenant general Tajuddeen Bishara"ya gama maganar yana kecewa da mahaukaciyar dariya.
Tabbas Fu'ad cikekken hatsabibin mutum ne da gane inda ya dosa se Allah da kuma mutum wanda ya fisa kaifin basira,ya wuce duk tunanin me tunani, yana da fuskokin da bazakayi tunanin ze iya yin muguwar muguntar da yake aikatawa ba,in ya juya mutumin kirki zakayi tunanin wani malami ne wanda yasan Allah yasan addini,amma in ya koma hatsabibinsa to ko shedan haka ya ganshi ya barsa,duk wanda ya shiga tarkon Fu'ad tofa sede ya yi addu'ar Allah ya kwacesa daga sharrinsa shine kawai.