Sashe 55
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ina magana kina bani amsa ko,eh lallai nuna min irin ta ki fitsaran da khareemar ta koya miki".
Damko hannun Sabriyah dake kuka kamar ranta ze fita ga zagin cin mutuncin da ummah ta musu ga kuma faɗar da yake kokarin afkuwa tsakanin ita da Hajjatiye kuma duk ta dalilin su.
Jan hannunta ummah ta yi da karfi kamar zata ƙaryata,ta fara janta da niyar fitar da ita daga cikin Mansion din, tirjewa Sabriyah ta fara yi tana bata hakuri tana kuka.
"Dan Allah ummah kiyi hakuri Wallahi abinda kike tunani ba haka bane".
Ummah na janta tana cewa "yau ai ko gidan nan gidan uban ku ne se kun barshi dama haushin ganin ku nakeyi a gidan".
Zubewa a ƙasa ta yi amma hakan be sa ummah ta dena jan nata ba,Fatime da kaltume ne da suke kitchen suka jiyo hayaniyar dake tashi suka shigo da gudu fatime ta haura part din Hajiya babba domin sanar da ita tasan Ammi,da anty amarya suna can.kaltume kuma ta nufi part din Abbie domin sanar dashi.
Riko dayan hannun Sabriyah Hajjatiye ta yi ranta a matukar ɓace ta ce"ki sa'ke ta nace Huraira Wallahi zanyi mummunar ɓata miki rai,kar ki bari in miki rashin mutuncin da kowa se ya yi dana sani".
Idon ummah ya riga da ya rufe in bawai fitar da Sabriyah ta yi daga cikin gidan ba hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba.tana haki ta ce"Wallahi ko da zakisa Isma'il ya sakeni ne yau tofa wa'yannan tsinanun annoban se sun bar gidan nan ko kuma ni in bar musu gidan"kamar za su raba Sabriyah gida biyu haka suke janta,Ummah na ja Hajjatiye na ja,wani irin wawan fisga ummah ta mata a hannun Hajjatiye da yasa seda ta buge kanta da glass din flower dake falon nan take gefen kanta ya fara zufar da jini domin glass din irin me karfin nan ne,duk da buguwa da ta yi dashi amma hakan be sa ya fashe ba.
Azaban da ya ziyarceta ne yasa ta kwala razananniyar ƙara da seda illahirin gidan ya amsa.
Tana riƙe da wajen da ya fashe tana kuka.
Abbie da Abbu kaltume ta samesu ta sanar dasu abinda yake faruwa,da hanzari suka baro part din nashi a hanya kuma suka ki kar'ar da Sabriyah ta yi hakan yasa suka sa'ke sauri gudun kar a yi barna.
Haka su Ammi ma Fatime cikin tashin hankali ta sanar dasu abinda ya faru,suma babu shiri suka fito a hanyarsu ta zuwa downstairs ne suka jiyo ihun Sabriyah.
Rameesa da tun dazun suna jiran dawuwar Sabriyah ne suka ki wannan gigitancen kar'ar da tayi ne yasa suma suka fito da gudu har da Asmita.
Sahil da Salim da yanzu shigowar su gidan suma suka ji ihun ne hankalinsu ya tashi.suka shigo da gudu.
Suna zaune a dakin bincike su hudu suna meeting akan kidnapping din da aka fara yi ne, LTG jikinsa ya bashi kamar akwai wani abu da yake faruwa hakan yasa ya Kunno CCTV din falo nan take ya hango yanda ummah ke dragging din Sabriyah da ke durkushe a ƙasa tana tirjewa ga kanta dake zubar da jini.
"Ohh shit"LTG ya faɗa yana miƙewa da sauri ya fice a dakin binciken,kallon system sukayi suka ga abinda yake faruwa suma da sauri suka rufawa LTG baya da ya riga da ya ma bar part din.
su Ammi ne suka riga kowa shigowa falon se su Abbie da gudu Hajiya babba ta je tasa iya karfinta ta fincike Sabriyah dake kuka abin tausayi a hannun ummah.
Boyeta a bayanta Hajiya babba ta yi "hurairah an ya akwai sauran hankali a tattare dake kuwa?, wannan wani irin mugunta ce dan fisabilillahi?".
Watsawa Hajiya babba banzan kallo ummah ta yi "dan Allah dakata Hajiya babba ke kinsan abinda yarinyar nan ta aikata min kuwa?".
Anty amarya da tana karasowa wajen Sabriyah ta rungumota a jiki,tana sa gyalenta ta goge mata jinin dake zuba a kanta.
Bude baki ta yi zata yi magana, Abbu ya daka mata tsawa ranshi a ɓace.
Su Asmita da shigowar su falon kenan suka ga abinda yake faruwa ta je ta rungume Sabriyah itama ta fashe da kuka duk da basu san abinda ya faru ba.
"Lallai Isma'il yau matar ka ta nuna fin ni bani na haifeta ba,tunda har ina hana Huraira aikata abinda take yi amma ta ƙi saurara na".
Su gaba daya their confused basu san abinda ya ke faruwa ga kuma Sabriyah da kanta ya fashe.
Kukan Sabriyah da Asmita ke tashi a falon.ganin Asmita ne yasa ummah dasauri tasa hannu ta cafkota,ta fara janta.
Hannun ummah anty amarya ta rike,ranta a ɓace ta ce"Huraira ki sa'ke yarinyar nan kar daga ni har ke, ran mu ya yi mummunar ɓaci kinji na faɗa miki ".
Dariyar renin hankali ummah ta yi"ai yau Wallahi yaran nan ba zasu ƙara ko awa daya a gidan nan ba barima ki gani"ta na gama fadin haka ta ture anty amarya da sauri Ammi ta riƙota.
Ji ta yi an riƙe hannun ta kallon wanda ya riken ta yi ta ga Saghar ne"Saghar ka sa'ke min hannu ko in saɓa maka".
Saghar da yanzu shigowar su falon suka tarar da abinda yake faruwa ne ya yi hanzarin rike hannun ummah.
Gently ya ce"ummah please ki sa'ke ta".
"To sannu ubana!na ce sannu ubana,to bazan sa'ke ta ba yau wa'yannan tsinannun yaran se sun bar mana gida nagaji da kallon su".
Ammi da ba ko da yaushe take saka baƙi a al'amarin gidan ba musanman ma abinda ya shafi Ammuh ko ummah ba.
Amma yau ummah ta kawo ta makura ganin abinda takeyi wa yaran .
"Babu wacce zata bar gidan nan Huraira wannan wani irin rashin imani ne haka,meye yaran nan suka tare miki,to na rantse da wanda ya halicce ni bazasu fita a gidan nan ba a yau,sede kiyi duk abinda zakiyi".
Dogon tsaki ta ja sannan ta fincike hannun Saghar da ya rike mata nata hannun.
Ransa ya ɓaci iya baci daga shi har Sudais da Abbu ganin abin kunyar da Ummah take aikatawa.
Idonsa a rufe ya ce
"Ummah ki sa'ke ta nace".
"Huraira ki sa'ke yarinyar nan,kar ki bari in sa'ke miki magana"cewar Abbu da ransa ya gama ɓaci domin ya gaji da halin Ummah yau kuma ga abinda ta bijiro dashi.
Hajjatiye na zaune akan kujera tana kukan cin mutuncin da ummah ta mata Hajiya babba na rarrashinta,Abbie ma yana tsaye ya zuba ido ya rasa menene abinda ze cewa ummah, LTG yana tsaye shima ya zuba musu ido shima be san mezece ba,ga Sabriyah da ya gani durkushe a ƙasa tana kuka.ga Asmita a hannun ummah taki sa'ke ta, Sudais in rasa ya yi dubu to seda ya ɓaci,ganin abinda ummah take yi.
Yan matan ma suna tsaye ganin tashin hankalin da aka tashi dashi yau a gidan nasu,suna tsaye suna hawaye,ga shi yanda ummah ta tsaya tana cin zarafin su Sabriyah abin be musu dadi ba ga faɗar da iyayen su suke yi.
Ammuh tana tsaye a gefe tana murmushin jin dadi, ummah bata taɓa burgeta ba irin yau da ta fita musu a giya.
Rike kugu ummah ta yi tana kallon cikin idon Abbu "ko zaka rabu dani ne ta dalilin wannan yaran?,se ka zaba ko ni Ko su".
Fisgo Asmita ya yi a hannun ummah ta faɗo jikinsa, jikinta har ya dau zafi ga rawan da yake abinda yake faruwa ya daga mata hankali dama ba wani isheshen lafiya ne da ita ba,yanzu kuma ga rashin mutuncin da ummah take musu.
Taɓa jikinta ya yi yaji yanda ya dau zafi rau.
"Saghar ka rabu da yarinyar nan,ko kuma...." Abbu ya ce "ko kuma me?,na ce ko kuma me ".
Tana huce da hura hanci ta ce "hmmmm.waya'nnan karuwan de se sun bar gidan nan su je can su ci gaba da rabawa yan titi,Yan iska marasa asali,yau yanda suka gama gantalewa a titi wani dan iskan ne ze aure su".
Jikin Saghar har tsuma yaƙe yi yarasa ya zeyi da maman tasu.
"Ina santa!ni nan zan aure ta"gaba daya kallon su ne ya koma kanshi jin abinda ya faɗi.
Kallon sa Asmita ta yi,maganar da yi ya da ki zuciyarta,ta rasa wani irin yanayi ta ji farin ciki ne ko kuma akasin haka.
Kamar wata mahaukaciya sabuwar kamu ta daka tsalle ta zo gabanshi ta ce"maimaita abinda kafada Saghar in ji,menene ka faɗa yanz_yanzun nan dan ubanka meye abinda kunnuwana suka ji mini, Allah yasa ba da gaske ba, ɗana da karuwa har abada baze yu ba".
Da karfi yanda kowa ze ji ya sa'ke furta "zan auretaaaaaaaa.....,ni ina son Asmee zan aure ta"kukan kura ummah ta yi ta chukumo wuyan Saghar kamar wacce ta samo tabin hankali ta soma magana"baka isa ba, baka isa ka zubar min da mutunci ba a dinga nuna ni ana cewa yarona ya auri karuwa,ina! karya kake yi,ko ubanka be isa ya sa ka aureta ba ɓalle kai".
Murmushin jin dadi da takaici Abbu da su Hajiya babba sukayi.
Abbu ya ce"dagaske Saghar kana son Asmita!?"gyada masa kai ya yi ko shakkan ummah dake rike da wuyan rigarsa be ji ba.
"To shikenan kasa a ranka kamar ka auri Asmita,baka da matar da ta wuce ta in sha Allah".
Yau in hauka ne yaci a ce ummah ta yi shi ganin abinda Saghar da Abbu suke da niyar haukata ta.
Kamar zata yi kuka ta ce "Isma'il ni zaka tozarta?to Wallahi tallahi ko zan yi yawo tsirara se na hana wannan cin mutuncin da kuke kokarin yi min, da rai na da lafiya ta bazan taɓa barin ɗana na cikina ya auro karuwa ba sauran da wani ya ci ya rage, budurwa sabuwa fil a leda zan aura masa yanda shine nan ze bude ta da kansa".
Runtse ido Sabriyah ta yi jin mummunar kalmar da ta jefesu dashi wai sauran da wasu suka ci suka rage,ina bazeyu ba,dole ne ma su bar gidan nan yau an musu irin wannan tereren tambadar basu san gobe wani kala za'a zo musu dashi ba.
Damko hannun Sabriyah dake kuka kamar ranta ze fita ga zagin cin mutuncin da ummah ta musu ga kuma faɗar da yake kokarin afkuwa tsakanin ita da Hajjatiye kuma duk ta dalilin su.
Jan hannunta ummah ta yi da karfi kamar zata ƙaryata,ta fara janta da niyar fitar da ita daga cikin Mansion din, tirjewa Sabriyah ta fara yi tana bata hakuri tana kuka.
"Dan Allah ummah kiyi hakuri Wallahi abinda kike tunani ba haka bane".
Ummah na janta tana cewa "yau ai ko gidan nan gidan uban ku ne se kun barshi dama haushin ganin ku nakeyi a gidan".
Zubewa a ƙasa ta yi amma hakan be sa ummah ta dena jan nata ba,Fatime da kaltume ne da suke kitchen suka jiyo hayaniyar dake tashi suka shigo da gudu fatime ta haura part din Hajiya babba domin sanar da ita tasan Ammi,da anty amarya suna can.kaltume kuma ta nufi part din Abbie domin sanar dashi.
Riko dayan hannun Sabriyah Hajjatiye ta yi ranta a matukar ɓace ta ce"ki sa'ke ta nace Huraira Wallahi zanyi mummunar ɓata miki rai,kar ki bari in miki rashin mutuncin da kowa se ya yi dana sani".
Idon ummah ya riga da ya rufe in bawai fitar da Sabriyah ta yi daga cikin gidan ba hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba.tana haki ta ce"Wallahi ko da zakisa Isma'il ya sakeni ne yau tofa wa'yannan tsinanun annoban se sun bar gidan nan ko kuma ni in bar musu gidan"kamar za su raba Sabriyah gida biyu haka suke janta,Ummah na ja Hajjatiye na ja,wani irin wawan fisga ummah ta mata a hannun Hajjatiye da yasa seda ta buge kanta da glass din flower dake falon nan take gefen kanta ya fara zufar da jini domin glass din irin me karfin nan ne,duk da buguwa da ta yi dashi amma hakan be sa ya fashe ba.
Azaban da ya ziyarceta ne yasa ta kwala razananniyar ƙara da seda illahirin gidan ya amsa.
Tana riƙe da wajen da ya fashe tana kuka.
Abbie da Abbu kaltume ta samesu ta sanar dasu abinda yake faruwa,da hanzari suka baro part din nashi a hanya kuma suka ki kar'ar da Sabriyah ta yi hakan yasa suka sa'ke sauri gudun kar a yi barna.
Haka su Ammi ma Fatime cikin tashin hankali ta sanar dasu abinda ya faru,suma babu shiri suka fito a hanyarsu ta zuwa downstairs ne suka jiyo ihun Sabriyah.
Rameesa da tun dazun suna jiran dawuwar Sabriyah ne suka ki wannan gigitancen kar'ar da tayi ne yasa suma suka fito da gudu har da Asmita.
Sahil da Salim da yanzu shigowar su gidan suma suka ji ihun ne hankalinsu ya tashi.suka shigo da gudu.
Suna zaune a dakin bincike su hudu suna meeting akan kidnapping din da aka fara yi ne, LTG jikinsa ya bashi kamar akwai wani abu da yake faruwa hakan yasa ya Kunno CCTV din falo nan take ya hango yanda ummah ke dragging din Sabriyah da ke durkushe a ƙasa tana tirjewa ga kanta dake zubar da jini.
"Ohh shit"LTG ya faɗa yana miƙewa da sauri ya fice a dakin binciken,kallon system sukayi suka ga abinda yake faruwa suma da sauri suka rufawa LTG baya da ya riga da ya ma bar part din.
su Ammi ne suka riga kowa shigowa falon se su Abbie da gudu Hajiya babba ta je tasa iya karfinta ta fincike Sabriyah dake kuka abin tausayi a hannun ummah.
Boyeta a bayanta Hajiya babba ta yi "hurairah an ya akwai sauran hankali a tattare dake kuwa?, wannan wani irin mugunta ce dan fisabilillahi?".
Watsawa Hajiya babba banzan kallo ummah ta yi "dan Allah dakata Hajiya babba ke kinsan abinda yarinyar nan ta aikata min kuwa?".
Anty amarya da tana karasowa wajen Sabriyah ta rungumota a jiki,tana sa gyalenta ta goge mata jinin dake zuba a kanta.
Bude baki ta yi zata yi magana, Abbu ya daka mata tsawa ranshi a ɓace.
Su Asmita da shigowar su falon kenan suka ga abinda yake faruwa ta je ta rungume Sabriyah itama ta fashe da kuka duk da basu san abinda ya faru ba.
"Lallai Isma'il yau matar ka ta nuna fin ni bani na haifeta ba,tunda har ina hana Huraira aikata abinda take yi amma ta ƙi saurara na".
Su gaba daya their confused basu san abinda ya ke faruwa ga kuma Sabriyah da kanta ya fashe.
Kukan Sabriyah da Asmita ke tashi a falon.ganin Asmita ne yasa ummah dasauri tasa hannu ta cafkota,ta fara janta.
Hannun ummah anty amarya ta rike,ranta a ɓace ta ce"Huraira ki sa'ke yarinyar nan kar daga ni har ke, ran mu ya yi mummunar ɓaci kinji na faɗa miki ".
Dariyar renin hankali ummah ta yi"ai yau Wallahi yaran nan ba zasu ƙara ko awa daya a gidan nan ba barima ki gani"ta na gama fadin haka ta ture anty amarya da sauri Ammi ta riƙota.
Ji ta yi an riƙe hannun ta kallon wanda ya riken ta yi ta ga Saghar ne"Saghar ka sa'ke min hannu ko in saɓa maka".
Saghar da yanzu shigowar su falon suka tarar da abinda yake faruwa ne ya yi hanzarin rike hannun ummah.
Gently ya ce"ummah please ki sa'ke ta".
"To sannu ubana!na ce sannu ubana,to bazan sa'ke ta ba yau wa'yannan tsinannun yaran se sun bar mana gida nagaji da kallon su".
Ammi da ba ko da yaushe take saka baƙi a al'amarin gidan ba musanman ma abinda ya shafi Ammuh ko ummah ba.
Amma yau ummah ta kawo ta makura ganin abinda takeyi wa yaran .
"Babu wacce zata bar gidan nan Huraira wannan wani irin rashin imani ne haka,meye yaran nan suka tare miki,to na rantse da wanda ya halicce ni bazasu fita a gidan nan ba a yau,sede kiyi duk abinda zakiyi".
Dogon tsaki ta ja sannan ta fincike hannun Saghar da ya rike mata nata hannun.
Ransa ya ɓaci iya baci daga shi har Sudais da Abbu ganin abin kunyar da Ummah take aikatawa.
Idonsa a rufe ya ce
"Ummah ki sa'ke ta nace".
"Huraira ki sa'ke yarinyar nan,kar ki bari in sa'ke miki magana"cewar Abbu da ransa ya gama ɓaci domin ya gaji da halin Ummah yau kuma ga abinda ta bijiro dashi.
Hajjatiye na zaune akan kujera tana kukan cin mutuncin da ummah ta mata Hajiya babba na rarrashinta,Abbie ma yana tsaye ya zuba ido ya rasa menene abinda ze cewa ummah, LTG yana tsaye shima ya zuba musu ido shima be san mezece ba,ga Sabriyah da ya gani durkushe a ƙasa tana kuka.ga Asmita a hannun ummah taki sa'ke ta, Sudais in rasa ya yi dubu to seda ya ɓaci,ganin abinda ummah take yi.
Yan matan ma suna tsaye ganin tashin hankalin da aka tashi dashi yau a gidan nasu,suna tsaye suna hawaye,ga shi yanda ummah ta tsaya tana cin zarafin su Sabriyah abin be musu dadi ba ga faɗar da iyayen su suke yi.
Ammuh tana tsaye a gefe tana murmushin jin dadi, ummah bata taɓa burgeta ba irin yau da ta fita musu a giya.
Rike kugu ummah ta yi tana kallon cikin idon Abbu "ko zaka rabu dani ne ta dalilin wannan yaran?,se ka zaba ko ni Ko su".
Fisgo Asmita ya yi a hannun ummah ta faɗo jikinsa, jikinta har ya dau zafi ga rawan da yake abinda yake faruwa ya daga mata hankali dama ba wani isheshen lafiya ne da ita ba,yanzu kuma ga rashin mutuncin da ummah take musu.
Taɓa jikinta ya yi yaji yanda ya dau zafi rau.
"Saghar ka rabu da yarinyar nan,ko kuma...." Abbu ya ce "ko kuma me?,na ce ko kuma me ".
Tana huce da hura hanci ta ce "hmmmm.waya'nnan karuwan de se sun bar gidan nan su je can su ci gaba da rabawa yan titi,Yan iska marasa asali,yau yanda suka gama gantalewa a titi wani dan iskan ne ze aure su".
Jikin Saghar har tsuma yaƙe yi yarasa ya zeyi da maman tasu.
"Ina santa!ni nan zan aure ta"gaba daya kallon su ne ya koma kanshi jin abinda ya faɗi.
Kallon sa Asmita ta yi,maganar da yi ya da ki zuciyarta,ta rasa wani irin yanayi ta ji farin ciki ne ko kuma akasin haka.
Kamar wata mahaukaciya sabuwar kamu ta daka tsalle ta zo gabanshi ta ce"maimaita abinda kafada Saghar in ji,menene ka faɗa yanz_yanzun nan dan ubanka meye abinda kunnuwana suka ji mini, Allah yasa ba da gaske ba, ɗana da karuwa har abada baze yu ba".
Da karfi yanda kowa ze ji ya sa'ke furta "zan auretaaaaaaaa.....,ni ina son Asmee zan aure ta"kukan kura ummah ta yi ta chukumo wuyan Saghar kamar wacce ta samo tabin hankali ta soma magana"baka isa ba, baka isa ka zubar min da mutunci ba a dinga nuna ni ana cewa yarona ya auri karuwa,ina! karya kake yi,ko ubanka be isa ya sa ka aureta ba ɓalle kai".
Murmushin jin dadi da takaici Abbu da su Hajiya babba sukayi.
Abbu ya ce"dagaske Saghar kana son Asmita!?"gyada masa kai ya yi ko shakkan ummah dake rike da wuyan rigarsa be ji ba.
"To shikenan kasa a ranka kamar ka auri Asmita,baka da matar da ta wuce ta in sha Allah".
Yau in hauka ne yaci a ce ummah ta yi shi ganin abinda Saghar da Abbu suke da niyar haukata ta.
Kamar zata yi kuka ta ce "Isma'il ni zaka tozarta?to Wallahi tallahi ko zan yi yawo tsirara se na hana wannan cin mutuncin da kuke kokarin yi min, da rai na da lafiya ta bazan taɓa barin ɗana na cikina ya auro karuwa ba sauran da wani ya ci ya rage, budurwa sabuwa fil a leda zan aura masa yanda shine nan ze bude ta da kansa".
Runtse ido Sabriyah ta yi jin mummunar kalmar da ta jefesu dashi wai sauran da wasu suka ci suka rage,ina bazeyu ba,dole ne ma su bar gidan nan yau an musu irin wannan tereren tambadar basu san gobe wani kala za'a zo musu dashi ba.