Sashe 10
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
karo ta ci dasu umaisha suna neman ta ga zanen a hannun Zoya sun raba shi gida biyu"Asrah kinga parsa ta yaga miki drawing din ki ko?"cewar umaisha tana nunawa Asrah zanen dake hannun Zoya yana a yage,turo bakinta Asrah ta yi ta ce"i don't have your time!look at my banglesssssss" ta yi maganar tana jujjuya musu hannunta matsowa duka suka yi suna so su kalla ta ruga aguje ta barsu a wajan.
Part din su ta shiga da gudu , akwance ta samu anty amarya tana bacci dan ciwon kai ne yake damunta tashigo saboda ta kwanta , hawa kan gadon ta yi , shigewa jikin anty amarya ta yi tana ta mutsu_mutsu kamar bera , bude ido ta yi tana hararanta dakyar ta iya cewa
" Asrah kinsan Allah zan dakeki , bakisan banida lafiya bane kinzo za ki dameni tashi ki tafi gun Ammi"
Sadaf_sadaf ta mike saboda tasan halin mommynta sosai dukda yanda take matukar sonta tofa Hakan baya hana in ta yi laifi ta mata duka domin anty amarya no nonsense ne bata daukan reni tana da zafi in aka kureta .
Part din Ammi ta shiga bata samu Ammi a dakin ba hakan yasa ta ɗale kan gado ta rufe kanta acikin bargo inba mutum ya lura ba ,bazesan akwai mutum akai ba.
Shigowa bedroom din Ammi ta yi tana manne da waya akunnenta tana waya da Hajjatiye se buhun masifa take zazzaga mata , Ammi de kunshe dariyarta takeyi tana bata hakuri .
Zama Ammi ta yi akan gadonta , Asrah jin an zauneta ne yasa ta fasa kara tana kokarin tashi .
A razane Ammi ta tashi akan gadon kirjinta nadukan tara tara se "innalillahi wa'innailaihi rajuun" takeyi ko kadan batayi tunanin mutum bane awajen , tsorata iya tsorata ta yi saboda lokacin da take da cikin Tajuddeen haka yataba faruwa da ita, shine yasa hankalinta ya tashi .
Asrah jin an ɗaga ta ne yasa ta ya'ye bargon ta fito kallon_kallo suka tsaya yi ita da Ammi, tafa hannu Ammi ta yi tana sallallami " ungo naki Asrah ja'ira kawai " ta faɗa tana mata daƙuwa , ita de ba ta ce komai ba se fiki_fiki takeyi da dara_daran idanunta
" Kai yarinyar nan kin tsoratar dani wallahi Allah yashiryeki ! Yaushe kika shigo bansaniba?"
Kwabe fuska ta yi tana kwanciya akan gadon , ta ce " ai mommy ne ta koreni " kamar zatayi kuka ta yi maganar , murmushi Ammi ta yi dama tunda ta ganta tana kumbure_kumbure tasan akwai wani zama ta yi akan gadon itama cikin kwantar da murya ta ce
" Ba koranki mommynki ta yi ba , bata da lafiya ne shisaka . Idan mommynki ta yi miki faɗa kidena bata rai babu kyau kinji ko?"
Gyada kai Asrah ta yi , rungume Ammi ta yi tana gyara kwanciyarta ajikinta , kallonta Ammi ta yi cike da son yar kanwar nata sauke idonta ta yi akan hannun Asrah dake dauke da abin hannun da Tajuddeen yabata , rike hannun ta yi tana ƙare mishi kallo nan ta fahimci ta inda Asrah ta samu , ajiyar zuciya ta yi aranta tana " ya Allah kai kadai kasan karatun kurma , Allah ka tabbatar da alkhari dake tsakanin Tajuddeen da kuma Asrah "
Kallon fuskar Asrah ta yi taga har ta yi baccinta , ahankali ta kwantar da ita akan gadon ta rufe ta da bedsheet , ta mike ta nufi part din anty amarya .
" Abida anya kinsha magani kuwa ? nasanki sarai da ƙin shan magani tashi kisha " cewar Ammi da bata dade da shigowa bedroom din ba .
Mikewa zaune anty amarya ta yi tana dafe kanta ta zuro ƙafafunta ƙasa.
Magani Ammi ta dauko da ruwa a glass cup ta bata,babu musu tasa hannu ta karba tasha sannan ta jinginu ajikin , makeken gadon ta na alfarma.
Sosai Ammi ta kare mata kallo kafin ta girgiza kai
" Abida meyesa kike saka damuwa aranki yakamata ki fawwalawa Allah komai "
Wasu hawaye masu zafi ne suka gangaro mata
" Anty hamdiyya dole in damu , musamman inna tuna kan cewa bazan sake haihuwa ba , karki manta fa ancire min mahaifa , har abada bazan sake haihuwa ba. Asrah ita kadai Allah ya bamu wallahi anty hamdiyya bazan boye miki ba Abdulhameed yana matukar kaunar yara nina sani komin daren dadewa ze ƙara aure saboda yasamu yara shima kuma ni bazan taɓa shiga hakkin shi ba , bazeyu ni bana haihuwa kuma in hanashi aure ba "
Sosai tabawa Ammi tausayi jikinta ne taji ya yi matukar sanyi , riko hannunta ta yi ta ce
" Ya isa shikenan kidena kuka , kamata ma ya yi kidinga godewa Allah , wasu fa neman ko da guda dayan sukeyi su samu amma ina Allah yasa babu haihuwa a ƙaddarar rayuwar su ,amma kefa kinga jininki aduniya , se bayan kin haife Asrah fa aka cire miki mahaifa , aduk san da kika kalleta ki dinga godewa Allah wasu neman guda daya ma sukeyi sun rasa , maganar Abdulhameed ze ƙara aure kuma ki kwantar da hankalinki ko da ze Ƙara aure wallahi bazeyi ɗan yaci mutuncinki ba, ɗan saboda yana matukar sanki, kuma namiji mijin mata hudu ne karma ki ce za ki sa wannan aranki . Ni yar uwarki ce ciki daya uwa daya uba daya nasan irin raɗaɗin da kikeji , Allah yana sane dake"
Murmushi ta yi ta kwantar da kanta akan kafaɗar Ammi " Nagodewa Allah dayasa nayi aure akusa da yar uwata , aduk sanda nake cikin damuwa ke kike kwantar min da hankali ina matukar alfahari dake anty hamdiyya"
Shafa kanta Ammi ta yi tana murmushi,son kanwar nata nasake ratsa ta.
Uncle Hameed da tun lokacin da suka fara magana ya shigo bedroom din yake tsaye abakin kofa yana harde da hannu a kirji , dukkansu biyun babu wanda ya san da yana dakin , karasawa cikin bedroom din ya yi se sannan ne suka ganshi saboda hankalinsu ya yi nisa cikin maganar da suke tattaunawa.
Durƙusawa Uncle Hameed ya yi agaban anty amarya ya rike kafaɗunta da dukkan hannayenshi biyu yasa idonshi cikin nata
" Abida wallahi babu irin wannan tunanin araina , eh tabbas inason yara inason inga yarana na shawagi atare dani amma ki yarda dani bantaba sha'awar haihuwa da wata mace ba in bake ba . Kuma godewa Allah zamuyi tunda seda muka haife Asrah kafin hakan yafaru ,kinga ai muna ganin gudan jininmu tana a tare damu me ze sanyamu bakin ciki? Kuma sannan koda ace bamu haife ta ba aka cire miki mahaifa wallahi bazan taɓa auro wata matar ba ,dan saboda ta haifa min yara ba ,babu wannan burin araina dake nafara rayuwata kuma dake zan gama duk runtsi duk dadi muna atare da junanmu , fatan da zamuyi shine muyi addu'a Allah ya raya mana Asrah dinmu muga lokacin aurenta da Tajuddeen "
Uncle Hameed ya ƙarishe maganar sa yana dan jan hancin anty amarya ,duk murmushi sukayi musamman ma maganar shi ta karshe da ya yi akan Asrah da kuma Tajuddeen.
Ammi ranta fal da farin ciki ganin kanwar nata ta ɗan saki ranta ,sake godewa Allah ta yi da yasa kanwarta ta auri namiji da yasan yakamata arayuwarshi me kuma sonta, saboda uncle Hameed yana da saukin kai sosai kuma an hadu andace ne shida anty amarya,sede ita tana da zafi bata daukan reni amma kam tana da kirki sosai kusan halinsu daya ne ita da Ammi .
Juyowa uncle Hameed ya yi ya kalli Ammi ya ce " ina matukar godiya anty da yasa ko yaushe kina me nuna mata hanya da kuma faɗa mata gaskiya "
Murmushi Ammi ta yi ta ce" Allah yabarku tare bari in koma part dina na bar wancan rigimammiyar tana bacci "
Mikewa ta yi ta musu sallama tafice.
Gangarowa downstairs Ammi ta yi with full surprise taga yaran gidan gaba daya a hade awaje daya kusa da Abbie da alamar abu suke kallo ko kuma video call suke yi wani tunani ne ya faɗo mata a rai " to kodai da mom Rumanatu suke wayane?" ta ƙarishe maganar taname ci gaba da saukowa main part din.
( mom Rumanatu Bishara ƙanwa ce agun Abbie da kuma Abbu se kuma ita last born kuma shine uncle Hameed su hudu ne agun iyayensu. Mom Rumanatu tana aure a Katsina tare da ƴaƴanta hudu da kuma mijinta)
Zama Ammi ta yi tana kallon yaran nasu yanda suke ta shan waya da mom Rumanatu gwanin sha'awa hakan kadai ze nuna maka akwai kauna me tsanani a tsakanin su ta cikin laptop din ta ji muryan mom Rumanatu na tambayar ina Tajuddeen da Asrah suke Abbas yabata amsa da "Taj yana part din shi ita kuma Asrah ni yau tunda nadawo gidan nan ma ban ganta ba"Zoya ce ta ce "dazun munga tashi ga part din Ammi" haka suka dinga hira daga karshe yaran suka watse suna mata sallama.
Abbu ne ya shiga part din su saghar ya samesu suna zaune suna searching a goggle tsikayan muryanshi sukayi yana tambayar su"ina mamanku?"kallon_kallo saghar da sudais suka tsaya yi kafin Sudais ya ce"Abbu ni Wallahi bansan ina Ummah take zuwa ba kullum bata gida" girgiza kai Abbu ya yi jin abinda yaran nasu suke faɗa wato su ma gantalin da uwarsu take yi yana damunsu.
Cikin kwantar da murya Abbu ya ce "karku damu in sha Allah everything will be history, in ta dawo ku ce mata Ina da Shari'a gobe zan shiga kotu da wuri" "to Abbu Allah ya taimaka" saghar da sudais suka faɗa,amsawa ya yi sannan ya juya ya fice.
Se mun haɗu Monday in Allah yakaimu da rai da lafiya.
Kamar yanda na faɗa de yawan comments dinku yawan read more din da zan yi muku,infact ma in bakwayin comment Wallahi hutu zan tafi in yaso in kun shirya yin comments din se muci gaba amma bazeyu ina muku posting ace wai comment ya gagara ba.
Comment,like and share 🖋️🖋️
🌹🌹 *ASHE ZAMUGA JUNA *🌹🌹
Page 08
*_ story & written_*
By
*_MRS 🌹 ISHAM 🌹_*
(Yar lelen Jarumai)
*The writer of ✍️*
*NIDA PATIENT DINA*
Part din su ta shiga da gudu , akwance ta samu anty amarya tana bacci dan ciwon kai ne yake damunta tashigo saboda ta kwanta , hawa kan gadon ta yi , shigewa jikin anty amarya ta yi tana ta mutsu_mutsu kamar bera , bude ido ta yi tana hararanta dakyar ta iya cewa
" Asrah kinsan Allah zan dakeki , bakisan banida lafiya bane kinzo za ki dameni tashi ki tafi gun Ammi"
Sadaf_sadaf ta mike saboda tasan halin mommynta sosai dukda yanda take matukar sonta tofa Hakan baya hana in ta yi laifi ta mata duka domin anty amarya no nonsense ne bata daukan reni tana da zafi in aka kureta .
Part din Ammi ta shiga bata samu Ammi a dakin ba hakan yasa ta ɗale kan gado ta rufe kanta acikin bargo inba mutum ya lura ba ,bazesan akwai mutum akai ba.
Shigowa bedroom din Ammi ta yi tana manne da waya akunnenta tana waya da Hajjatiye se buhun masifa take zazzaga mata , Ammi de kunshe dariyarta takeyi tana bata hakuri .
Zama Ammi ta yi akan gadonta , Asrah jin an zauneta ne yasa ta fasa kara tana kokarin tashi .
A razane Ammi ta tashi akan gadon kirjinta nadukan tara tara se "innalillahi wa'innailaihi rajuun" takeyi ko kadan batayi tunanin mutum bane awajen , tsorata iya tsorata ta yi saboda lokacin da take da cikin Tajuddeen haka yataba faruwa da ita, shine yasa hankalinta ya tashi .
Asrah jin an ɗaga ta ne yasa ta ya'ye bargon ta fito kallon_kallo suka tsaya yi ita da Ammi, tafa hannu Ammi ta yi tana sallallami " ungo naki Asrah ja'ira kawai " ta faɗa tana mata daƙuwa , ita de ba ta ce komai ba se fiki_fiki takeyi da dara_daran idanunta
" Kai yarinyar nan kin tsoratar dani wallahi Allah yashiryeki ! Yaushe kika shigo bansaniba?"
Kwabe fuska ta yi tana kwanciya akan gadon , ta ce " ai mommy ne ta koreni " kamar zatayi kuka ta yi maganar , murmushi Ammi ta yi dama tunda ta ganta tana kumbure_kumbure tasan akwai wani zama ta yi akan gadon itama cikin kwantar da murya ta ce
" Ba koranki mommynki ta yi ba , bata da lafiya ne shisaka . Idan mommynki ta yi miki faɗa kidena bata rai babu kyau kinji ko?"
Gyada kai Asrah ta yi , rungume Ammi ta yi tana gyara kwanciyarta ajikinta , kallonta Ammi ta yi cike da son yar kanwar nata sauke idonta ta yi akan hannun Asrah dake dauke da abin hannun da Tajuddeen yabata , rike hannun ta yi tana ƙare mishi kallo nan ta fahimci ta inda Asrah ta samu , ajiyar zuciya ta yi aranta tana " ya Allah kai kadai kasan karatun kurma , Allah ka tabbatar da alkhari dake tsakanin Tajuddeen da kuma Asrah "
Kallon fuskar Asrah ta yi taga har ta yi baccinta , ahankali ta kwantar da ita akan gadon ta rufe ta da bedsheet , ta mike ta nufi part din anty amarya .
" Abida anya kinsha magani kuwa ? nasanki sarai da ƙin shan magani tashi kisha " cewar Ammi da bata dade da shigowa bedroom din ba .
Mikewa zaune anty amarya ta yi tana dafe kanta ta zuro ƙafafunta ƙasa.
Magani Ammi ta dauko da ruwa a glass cup ta bata,babu musu tasa hannu ta karba tasha sannan ta jinginu ajikin , makeken gadon ta na alfarma.
Sosai Ammi ta kare mata kallo kafin ta girgiza kai
" Abida meyesa kike saka damuwa aranki yakamata ki fawwalawa Allah komai "
Wasu hawaye masu zafi ne suka gangaro mata
" Anty hamdiyya dole in damu , musamman inna tuna kan cewa bazan sake haihuwa ba , karki manta fa ancire min mahaifa , har abada bazan sake haihuwa ba. Asrah ita kadai Allah ya bamu wallahi anty hamdiyya bazan boye miki ba Abdulhameed yana matukar kaunar yara nina sani komin daren dadewa ze ƙara aure saboda yasamu yara shima kuma ni bazan taɓa shiga hakkin shi ba , bazeyu ni bana haihuwa kuma in hanashi aure ba "
Sosai tabawa Ammi tausayi jikinta ne taji ya yi matukar sanyi , riko hannunta ta yi ta ce
" Ya isa shikenan kidena kuka , kamata ma ya yi kidinga godewa Allah , wasu fa neman ko da guda dayan sukeyi su samu amma ina Allah yasa babu haihuwa a ƙaddarar rayuwar su ,amma kefa kinga jininki aduniya , se bayan kin haife Asrah fa aka cire miki mahaifa , aduk san da kika kalleta ki dinga godewa Allah wasu neman guda daya ma sukeyi sun rasa , maganar Abdulhameed ze ƙara aure kuma ki kwantar da hankalinki ko da ze Ƙara aure wallahi bazeyi ɗan yaci mutuncinki ba, ɗan saboda yana matukar sanki, kuma namiji mijin mata hudu ne karma ki ce za ki sa wannan aranki . Ni yar uwarki ce ciki daya uwa daya uba daya nasan irin raɗaɗin da kikeji , Allah yana sane dake"
Murmushi ta yi ta kwantar da kanta akan kafaɗar Ammi " Nagodewa Allah dayasa nayi aure akusa da yar uwata , aduk sanda nake cikin damuwa ke kike kwantar min da hankali ina matukar alfahari dake anty hamdiyya"
Shafa kanta Ammi ta yi tana murmushi,son kanwar nata nasake ratsa ta.
Uncle Hameed da tun lokacin da suka fara magana ya shigo bedroom din yake tsaye abakin kofa yana harde da hannu a kirji , dukkansu biyun babu wanda ya san da yana dakin , karasawa cikin bedroom din ya yi se sannan ne suka ganshi saboda hankalinsu ya yi nisa cikin maganar da suke tattaunawa.
Durƙusawa Uncle Hameed ya yi agaban anty amarya ya rike kafaɗunta da dukkan hannayenshi biyu yasa idonshi cikin nata
" Abida wallahi babu irin wannan tunanin araina , eh tabbas inason yara inason inga yarana na shawagi atare dani amma ki yarda dani bantaba sha'awar haihuwa da wata mace ba in bake ba . Kuma godewa Allah zamuyi tunda seda muka haife Asrah kafin hakan yafaru ,kinga ai muna ganin gudan jininmu tana a tare damu me ze sanyamu bakin ciki? Kuma sannan koda ace bamu haife ta ba aka cire miki mahaifa wallahi bazan taɓa auro wata matar ba ,dan saboda ta haifa min yara ba ,babu wannan burin araina dake nafara rayuwata kuma dake zan gama duk runtsi duk dadi muna atare da junanmu , fatan da zamuyi shine muyi addu'a Allah ya raya mana Asrah dinmu muga lokacin aurenta da Tajuddeen "
Uncle Hameed ya ƙarishe maganar sa yana dan jan hancin anty amarya ,duk murmushi sukayi musamman ma maganar shi ta karshe da ya yi akan Asrah da kuma Tajuddeen.
Ammi ranta fal da farin ciki ganin kanwar nata ta ɗan saki ranta ,sake godewa Allah ta yi da yasa kanwarta ta auri namiji da yasan yakamata arayuwarshi me kuma sonta, saboda uncle Hameed yana da saukin kai sosai kuma an hadu andace ne shida anty amarya,sede ita tana da zafi bata daukan reni amma kam tana da kirki sosai kusan halinsu daya ne ita da Ammi .
Juyowa uncle Hameed ya yi ya kalli Ammi ya ce " ina matukar godiya anty da yasa ko yaushe kina me nuna mata hanya da kuma faɗa mata gaskiya "
Murmushi Ammi ta yi ta ce" Allah yabarku tare bari in koma part dina na bar wancan rigimammiyar tana bacci "
Mikewa ta yi ta musu sallama tafice.
Gangarowa downstairs Ammi ta yi with full surprise taga yaran gidan gaba daya a hade awaje daya kusa da Abbie da alamar abu suke kallo ko kuma video call suke yi wani tunani ne ya faɗo mata a rai " to kodai da mom Rumanatu suke wayane?" ta ƙarishe maganar taname ci gaba da saukowa main part din.
( mom Rumanatu Bishara ƙanwa ce agun Abbie da kuma Abbu se kuma ita last born kuma shine uncle Hameed su hudu ne agun iyayensu. Mom Rumanatu tana aure a Katsina tare da ƴaƴanta hudu da kuma mijinta)
Zama Ammi ta yi tana kallon yaran nasu yanda suke ta shan waya da mom Rumanatu gwanin sha'awa hakan kadai ze nuna maka akwai kauna me tsanani a tsakanin su ta cikin laptop din ta ji muryan mom Rumanatu na tambayar ina Tajuddeen da Asrah suke Abbas yabata amsa da "Taj yana part din shi ita kuma Asrah ni yau tunda nadawo gidan nan ma ban ganta ba"Zoya ce ta ce "dazun munga tashi ga part din Ammi" haka suka dinga hira daga karshe yaran suka watse suna mata sallama.
Abbu ne ya shiga part din su saghar ya samesu suna zaune suna searching a goggle tsikayan muryanshi sukayi yana tambayar su"ina mamanku?"kallon_kallo saghar da sudais suka tsaya yi kafin Sudais ya ce"Abbu ni Wallahi bansan ina Ummah take zuwa ba kullum bata gida" girgiza kai Abbu ya yi jin abinda yaran nasu suke faɗa wato su ma gantalin da uwarsu take yi yana damunsu.
Cikin kwantar da murya Abbu ya ce "karku damu in sha Allah everything will be history, in ta dawo ku ce mata Ina da Shari'a gobe zan shiga kotu da wuri" "to Abbu Allah ya taimaka" saghar da sudais suka faɗa,amsawa ya yi sannan ya juya ya fice.
Se mun haɗu Monday in Allah yakaimu da rai da lafiya.
Kamar yanda na faɗa de yawan comments dinku yawan read more din da zan yi muku,infact ma in bakwayin comment Wallahi hutu zan tafi in yaso in kun shirya yin comments din se muci gaba amma bazeyu ina muku posting ace wai comment ya gagara ba.
Comment,like and share 🖋️🖋️
🌹🌹 *ASHE ZAMUGA JUNA *🌹🌹
Page 08
*_ story & written_*
By
*_MRS 🌹 ISHAM 🌹_*
(Yar lelen Jarumai)
*The writer of ✍️*
*NIDA PATIENT DINA*