Sashe 46
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bude baki Hafiz ya yi ze yi magana abbu ya galla masa harara yasan be wuce tsokana bace zeyi.
Ba shiri ya yi shuru.
"Nikam ina katon Gwauron gidan nan ne ko be da wo ba ne haryanzu!?",Ammi ta ce"ya dawo bari a kirasa"tafa hannu Hajjatiye ta yi,ta ce"lallai hamdiyya wuyarki ya yi kauri,yanzu jikan nawa in banda baƙin hali irin naki se na tambayi ina yake kafin za ki sa a kirawo sa,tabb dijam"cikin girmamawa Ammi ta bata hakuri.
Dawood ne yaje ya kira LTG da be ma san da zuwansu ba.
Shigowa falon ya yi yana taku na kasaita jikinsa na sanye da dogon wando da rigar me doguwar hannu.
Hajjatiye na ganinsa ta fara sakin murmushi.
"Kun ga na miji sojan yaƙi,me firgita abokan hamayya,daya tamkar da dubu, Allah de ya biya na mijin duniya". murmushin da beyi niyya bane ya subuce masa duk da se wanda ya kula sosai ze gani.zama ya yi a kusa da ita yana rike hannunta.
Farin cikin Hajjatiye yakasa boyuwa, LTG yana daya daga jikin wanda ta fi kauna acikin jikokinta daga shi kuma se Asrah,kwata_kwata bata ganin laifin sa duk abinda ze yi bata masa faɗa,bazaka tabajin Hajjatiye tana yiwa LTG Masifa ba.
Kunnesa ta kama ta yi masa magana wai batasan munafukai su ji me ta faɗa mishi,shima da ya tashi bata amsa a kunne ya sanar mata.
Kallon su kawai sukeyi,ga shi suna son yin dariya amma wanda ya kuskura ya yi ma yasan ya jawo wa kansa hakan yasa duk suka zuba musu ido kawai.
Hajiya babba ta ce "Abbie dama akwai maganar da nakeso muyi dangane da yarinyar da Tajuddeen yakawo,amma zan so mu fara jin tarihin su tukun,saboda Abida ta nuna tana ra'ayin adopting din dayar yarinyar" "to tana ina ne yarinyar!?",Abbie ya tambayeta.
Kallon Zoya Hajiya babba ta yi ta ce "je ki kira mini Sabriyah"ranta be so ba haka ta mike ta nufi part din su.
kallon anty amarya da aka ce zata zatayi adopting din Sabriyah LTG ya yi,be iya cewa komai ba se kwantar da kansa akan kujerar da yake zaune ya lumshe idanunsa.
Dawuwa falon Zoya ta yi Sabriyah na biye da ita a bayanta,tana riƙe da hannun Asmita.
Ganin yanda suke da yawa a falon, suna shigowa ciki ido ya dawo kansu nan tajita a takure saboda idonsu.
Zama Zoya ta yi ta barsu a tsaye, Abbie ya ce mata "zo ku zauna"in da su Parsa suke zaune a kan lallausan carpet su ka zauna.zaman su beda wuya Asmita ga Saghar.
Da sauri ta tashi taje wajensa ta riko hannayensa biyu"me kyau ka zo muje mu hau lilo"da mamaki suke bin Saghar da Asmita da kallo musamman wa'yanda basu san condition din da take ciki ba,dan in ba tayi magana ba babu wanda ze ce tana da Matsala,kallon su Abbu ya yi yaga yanda idanunsu yake akanshi.
"Asmee je ki zauna wajan Sabriyah anjuma kadan zamu je lilo"sa'ke sa ta yi tafara kirge da hannunta,kamar me lissafi can kuma ta sa'ke cewa"tom shikenan ai jiya da yanzu zamu tafi ko"gyada mata kai ya yi saboda ya samu yaje ta zauna.
Komawa wajen Sabriyah ta yi,cikin rada ta ce"my Jerry in kika sake tashi a wajen nan to zanyi kuka"kwabe fuska ta yi "tom ba zan kara ba".
Gyaran murya Abbie ya yi,ya soma magana"Sabriyah wannan din meye din ki ce!?",a hankali ta ce"yar uwata' ce kuma ƙawata".
Jinjina kai ya yi ya sa'ke furta"ina son ki bamu tarihin rayuwar ku". har lokacin LTG yana a yanda yake be bude idonsa ba duk abinda ake faɗa yana jinsu.
Dogon numfashi ta ja,ta soma magana"sunana Sabriyah wannan kuma sunanta Asmita,mun taso a gidan karuwai ne wanda ni da ita anan muka taso tun muna yara kananu,bata san kowa ba haka nima babu wanda nasani, wannan dalilin yasa muka yiwa kanmu,alkawarin zamawa junanmu uwa,uba,yar uwa,kawa, magajiyar da ta siye mu ta gana mana azaba wanda se da mukaji dama bamu zo duniya,tun muna yara take aka koya mana abubuwan da zamu dinga kawo mata kudi, karuwanci,sata,damfara,rawa.dukka babu abinda bama aikatawa.tun ban kai haka ba nafara rawa a cikin gidan wasa,ban wani saba ba,in mun kayi ranar haka zamu kwana da ciwon jiki babu me bamu maganin ciwon kai,kudin da aka samu da mu a wajen rawa ko ruwa ba'a siya mana dashi,abinci ma sau daya ake turo mana dashi arana, se de wacce ta rene mu ita ce in ta fita nata wajen take samo mana abinda zamu ci,har yakai ga karfinta ya ƙare takamu da ciwo,ya zamana babu me taimakonmu wannan dalilin yasa na busar da zuciyata,na fara yin rawa,domin in samo mana abinda zamu dinga ciyar damu,domin tunda muka kai shekaru goma sha uku boss lady ta cire hannunta akan mu abinci sau daya da ake turo mana ma tadena haka zamu sha wahala muyi rawa amma kudin gaba daya zatasa a kwashe mata,ko biyar bama ci aciki.
Samarin da na fara yi ne suka fara bani kudi,nan na samu nafara biya mana buƙatar mu,nice nake ciyar damu,suturarmu duk yana kaina, in wani babu lafiya a cikinmu nice nake siya mana magani,maganin antynmu da ta rene mu nice nan nake samowa.daga zaran muyi mata laifi ko min kankantar laifi,zata haɗa mu ta mana muguwar duka,duk abinda ze same mu ita be dame ta ba,inde zamu kawo mata kuɗi to magana ya ƙare.bamu da yanci a wannan gidan,in kanason ka samu yanci shine se an maka lasisi,kafin ayi mana lasisi munsha bakar wahala, tasan sarai inada ciwo amma daga zaran na mata laifi haka zata barni a cikin ruwan sama ya mini dukkan da se ciwo na ya tashi ko kuma ta sa in yi kneel down haka zata sa a dinga diban ruwa ana shekamin.
Tunda nayi baki har na fara iya mayar mata da martani,sun riga da sun bude mini ido bana shakkan kowa,duk wanda yace ze takani to Ni se na ta kashi.daga ni har Asmita se da ta tabbatar da ta mayar damu karuwan suka fi kawo mata kudi kafin nan hankalinta ya kwanta daga nan ne ta yi mana lasisin karuwancin.
A da banijin dadin rayuwar can amma nazo na saba da komai in su naji banida in da yafi mini can,domin duk inda naje jina nakeyi kamar akan kaya nake bana samun nutsuwa se in na koma can, kullum maganar Asmita shine yaushe zamu bar wannan gida,ta tsani gidan fiye da mutuwarta.
Ita babanta ne ya siyar da ita a wajen boss lady saboda son abin duniya.da wannan abun Asmita ta taso shine a mafarkinta ta kasance cikin kunci da raɗaɗin abinda mahaifin da ya haifeta ya aikata a gare ta, kullum in tayi bacci se ta yi mafarkin lokacin da babanta ya siyar da ita,ta wannan dalilin ne yasa ta fara shaye_shaye ko zata ji saukin raɗaɗin da takeji, kullum cikin yi mata faɗa nakeyi akan shan kayan mayen da takeyi, amma ko a boye se ta sha.
A haka na haɗu da wannan a kasuwa daga nan ne rayuwar mu ya shiga cikin babban matsala,mun haɗu da wani ya bawa Asmita memory card, daga nan ita kuma ta bani shi na boye,a washe garin suka saceta sun yi zaton memory yana wajenta nikuma wancan ya sato ni, wannan shine kadan daga cikin tarihin rayuwarmu".
Sunyi matukar tausayawa yara batare da sun san komai ba aka jefa rayuwar su cikin garari,aka yi musu muguwar illa,sun yi rayuwa batare da sun san dadin ta ba,babu boko ba bu arabic,ba sallah ɓalle salati.
Babu abinda yakai wannan cutarwa ce babu wani kyakyawar alaƙa tsakanin ka da mahaliccinka,baka ma san meye dede maye ba dede ba,hakkin su yana rataye ne akan wuyan wa'yanda sukayi sanadiyyar shigar su cikin wannan muguwar rayuwa.
Ammi,Hajiya babba,Anty amarya,mom Rumanatu hawaye ne kawai yake zuba daga idanunsu suma iyayene yau ya zasu ji idan ace ya'yansu akayi wa haka.ya zasu ji idan a ce yau ƴaƴansu aka mayar karuwai amma ance ko wani bawa da kalar tasa ƙaddara,su tasu kaddarar a haka yazo.
Yan matan kansu kuka suke yi da sukaji labarin Asmita da Sabriyah hatta Zoya se da tayi kuka ta yi danasanin abinda ta aikatawa Sabriyah.
Hajjatiye tsabar tausayinsu seda ta yi kuka itama tana tsinewa wa'yanda suka musu haka.
Su Saghar idanunsu ya yi ja sosai ran maza ya ɓaci sun dau alwashi yanda boss lady take wargaza rayuwar yara mata ita ma se sun wargaza nata rayuwar.
Me gayya me aiki kuwa yanda yake zaune kuwa ji yake yi kamar ya je gidan karuwan ya kashe boss lady y kuma kona gidan,ya tausaya musu da halin da suka tsinci kansu,be taɓa kawo tunanin cewa wannan ne dalilin da yasa suka tsinci rayuwarsu a haka ba,domin akwai ballagazazzu matan da suka watsar da kansu babu wanda ya musu dole,su suke mayar da kansu karuwai.wasu su gudu su shiga duniya suna sheka ayarsu,ga wa'yanda kwadayin abin duniya yake jawo su bariki.wasu kuma matsalolin rayuwa ce.amma koma wani matsala ne be kamata bawa ya jefa kansa cikin saɓon Allah ba.
Hakan ne yasa ya mata kallon ɗaya daga cikinsu ashe ba haka bane.ya kudurta a ransa ze dau mummunan mataki akan boss lady.
Ammuh da Ummah ko kadan basu,basu tausayi ba tabe baki sukayi suna watsa musu harara.
Su Abbie sun jinjina lamarin kuma sun tausaya musu sosai,ganin da cewa su din yara ne da kansu daya da ya'yansu.
Ba shiri ya yi shuru.
"Nikam ina katon Gwauron gidan nan ne ko be da wo ba ne haryanzu!?",Ammi ta ce"ya dawo bari a kirasa"tafa hannu Hajjatiye ta yi,ta ce"lallai hamdiyya wuyarki ya yi kauri,yanzu jikan nawa in banda baƙin hali irin naki se na tambayi ina yake kafin za ki sa a kirawo sa,tabb dijam"cikin girmamawa Ammi ta bata hakuri.
Dawood ne yaje ya kira LTG da be ma san da zuwansu ba.
Shigowa falon ya yi yana taku na kasaita jikinsa na sanye da dogon wando da rigar me doguwar hannu.
Hajjatiye na ganinsa ta fara sakin murmushi.
"Kun ga na miji sojan yaƙi,me firgita abokan hamayya,daya tamkar da dubu, Allah de ya biya na mijin duniya". murmushin da beyi niyya bane ya subuce masa duk da se wanda ya kula sosai ze gani.zama ya yi a kusa da ita yana rike hannunta.
Farin cikin Hajjatiye yakasa boyuwa, LTG yana daya daga jikin wanda ta fi kauna acikin jikokinta daga shi kuma se Asrah,kwata_kwata bata ganin laifin sa duk abinda ze yi bata masa faɗa,bazaka tabajin Hajjatiye tana yiwa LTG Masifa ba.
Kunnesa ta kama ta yi masa magana wai batasan munafukai su ji me ta faɗa mishi,shima da ya tashi bata amsa a kunne ya sanar mata.
Kallon su kawai sukeyi,ga shi suna son yin dariya amma wanda ya kuskura ya yi ma yasan ya jawo wa kansa hakan yasa duk suka zuba musu ido kawai.
Hajiya babba ta ce "Abbie dama akwai maganar da nakeso muyi dangane da yarinyar da Tajuddeen yakawo,amma zan so mu fara jin tarihin su tukun,saboda Abida ta nuna tana ra'ayin adopting din dayar yarinyar" "to tana ina ne yarinyar!?",Abbie ya tambayeta.
Kallon Zoya Hajiya babba ta yi ta ce "je ki kira mini Sabriyah"ranta be so ba haka ta mike ta nufi part din su.
kallon anty amarya da aka ce zata zatayi adopting din Sabriyah LTG ya yi,be iya cewa komai ba se kwantar da kansa akan kujerar da yake zaune ya lumshe idanunsa.
Dawuwa falon Zoya ta yi Sabriyah na biye da ita a bayanta,tana riƙe da hannun Asmita.
Ganin yanda suke da yawa a falon, suna shigowa ciki ido ya dawo kansu nan tajita a takure saboda idonsu.
Zama Zoya ta yi ta barsu a tsaye, Abbie ya ce mata "zo ku zauna"in da su Parsa suke zaune a kan lallausan carpet su ka zauna.zaman su beda wuya Asmita ga Saghar.
Da sauri ta tashi taje wajensa ta riko hannayensa biyu"me kyau ka zo muje mu hau lilo"da mamaki suke bin Saghar da Asmita da kallo musamman wa'yanda basu san condition din da take ciki ba,dan in ba tayi magana ba babu wanda ze ce tana da Matsala,kallon su Abbu ya yi yaga yanda idanunsu yake akanshi.
"Asmee je ki zauna wajan Sabriyah anjuma kadan zamu je lilo"sa'ke sa ta yi tafara kirge da hannunta,kamar me lissafi can kuma ta sa'ke cewa"tom shikenan ai jiya da yanzu zamu tafi ko"gyada mata kai ya yi saboda ya samu yaje ta zauna.
Komawa wajen Sabriyah ta yi,cikin rada ta ce"my Jerry in kika sake tashi a wajen nan to zanyi kuka"kwabe fuska ta yi "tom ba zan kara ba".
Gyaran murya Abbie ya yi,ya soma magana"Sabriyah wannan din meye din ki ce!?",a hankali ta ce"yar uwata' ce kuma ƙawata".
Jinjina kai ya yi ya sa'ke furta"ina son ki bamu tarihin rayuwar ku". har lokacin LTG yana a yanda yake be bude idonsa ba duk abinda ake faɗa yana jinsu.
Dogon numfashi ta ja,ta soma magana"sunana Sabriyah wannan kuma sunanta Asmita,mun taso a gidan karuwai ne wanda ni da ita anan muka taso tun muna yara kananu,bata san kowa ba haka nima babu wanda nasani, wannan dalilin yasa muka yiwa kanmu,alkawarin zamawa junanmu uwa,uba,yar uwa,kawa, magajiyar da ta siye mu ta gana mana azaba wanda se da mukaji dama bamu zo duniya,tun muna yara take aka koya mana abubuwan da zamu dinga kawo mata kudi, karuwanci,sata,damfara,rawa.dukka babu abinda bama aikatawa.tun ban kai haka ba nafara rawa a cikin gidan wasa,ban wani saba ba,in mun kayi ranar haka zamu kwana da ciwon jiki babu me bamu maganin ciwon kai,kudin da aka samu da mu a wajen rawa ko ruwa ba'a siya mana dashi,abinci ma sau daya ake turo mana dashi arana, se de wacce ta rene mu ita ce in ta fita nata wajen take samo mana abinda zamu ci,har yakai ga karfinta ya ƙare takamu da ciwo,ya zamana babu me taimakonmu wannan dalilin yasa na busar da zuciyata,na fara yin rawa,domin in samo mana abinda zamu dinga ciyar damu,domin tunda muka kai shekaru goma sha uku boss lady ta cire hannunta akan mu abinci sau daya da ake turo mana ma tadena haka zamu sha wahala muyi rawa amma kudin gaba daya zatasa a kwashe mata,ko biyar bama ci aciki.
Samarin da na fara yi ne suka fara bani kudi,nan na samu nafara biya mana buƙatar mu,nice nake ciyar damu,suturarmu duk yana kaina, in wani babu lafiya a cikinmu nice nake siya mana magani,maganin antynmu da ta rene mu nice nan nake samowa.daga zaran muyi mata laifi ko min kankantar laifi,zata haɗa mu ta mana muguwar duka,duk abinda ze same mu ita be dame ta ba,inde zamu kawo mata kuɗi to magana ya ƙare.bamu da yanci a wannan gidan,in kanason ka samu yanci shine se an maka lasisi,kafin ayi mana lasisi munsha bakar wahala, tasan sarai inada ciwo amma daga zaran na mata laifi haka zata barni a cikin ruwan sama ya mini dukkan da se ciwo na ya tashi ko kuma ta sa in yi kneel down haka zata sa a dinga diban ruwa ana shekamin.
Tunda nayi baki har na fara iya mayar mata da martani,sun riga da sun bude mini ido bana shakkan kowa,duk wanda yace ze takani to Ni se na ta kashi.daga ni har Asmita se da ta tabbatar da ta mayar damu karuwan suka fi kawo mata kudi kafin nan hankalinta ya kwanta daga nan ne ta yi mana lasisin karuwancin.
A da banijin dadin rayuwar can amma nazo na saba da komai in su naji banida in da yafi mini can,domin duk inda naje jina nakeyi kamar akan kaya nake bana samun nutsuwa se in na koma can, kullum maganar Asmita shine yaushe zamu bar wannan gida,ta tsani gidan fiye da mutuwarta.
Ita babanta ne ya siyar da ita a wajen boss lady saboda son abin duniya.da wannan abun Asmita ta taso shine a mafarkinta ta kasance cikin kunci da raɗaɗin abinda mahaifin da ya haifeta ya aikata a gare ta, kullum in tayi bacci se ta yi mafarkin lokacin da babanta ya siyar da ita,ta wannan dalilin ne yasa ta fara shaye_shaye ko zata ji saukin raɗaɗin da takeji, kullum cikin yi mata faɗa nakeyi akan shan kayan mayen da takeyi, amma ko a boye se ta sha.
A haka na haɗu da wannan a kasuwa daga nan ne rayuwar mu ya shiga cikin babban matsala,mun haɗu da wani ya bawa Asmita memory card, daga nan ita kuma ta bani shi na boye,a washe garin suka saceta sun yi zaton memory yana wajenta nikuma wancan ya sato ni, wannan shine kadan daga cikin tarihin rayuwarmu".
Sunyi matukar tausayawa yara batare da sun san komai ba aka jefa rayuwar su cikin garari,aka yi musu muguwar illa,sun yi rayuwa batare da sun san dadin ta ba,babu boko ba bu arabic,ba sallah ɓalle salati.
Babu abinda yakai wannan cutarwa ce babu wani kyakyawar alaƙa tsakanin ka da mahaliccinka,baka ma san meye dede maye ba dede ba,hakkin su yana rataye ne akan wuyan wa'yanda sukayi sanadiyyar shigar su cikin wannan muguwar rayuwa.
Ammi,Hajiya babba,Anty amarya,mom Rumanatu hawaye ne kawai yake zuba daga idanunsu suma iyayene yau ya zasu ji idan ace ya'yansu akayi wa haka.ya zasu ji idan a ce yau ƴaƴansu aka mayar karuwai amma ance ko wani bawa da kalar tasa ƙaddara,su tasu kaddarar a haka yazo.
Yan matan kansu kuka suke yi da sukaji labarin Asmita da Sabriyah hatta Zoya se da tayi kuka ta yi danasanin abinda ta aikatawa Sabriyah.
Hajjatiye tsabar tausayinsu seda ta yi kuka itama tana tsinewa wa'yanda suka musu haka.
Su Saghar idanunsu ya yi ja sosai ran maza ya ɓaci sun dau alwashi yanda boss lady take wargaza rayuwar yara mata ita ma se sun wargaza nata rayuwar.
Me gayya me aiki kuwa yanda yake zaune kuwa ji yake yi kamar ya je gidan karuwan ya kashe boss lady y kuma kona gidan,ya tausaya musu da halin da suka tsinci kansu,be taɓa kawo tunanin cewa wannan ne dalilin da yasa suka tsinci rayuwarsu a haka ba,domin akwai ballagazazzu matan da suka watsar da kansu babu wanda ya musu dole,su suke mayar da kansu karuwai.wasu su gudu su shiga duniya suna sheka ayarsu,ga wa'yanda kwadayin abin duniya yake jawo su bariki.wasu kuma matsalolin rayuwa ce.amma koma wani matsala ne be kamata bawa ya jefa kansa cikin saɓon Allah ba.
Hakan ne yasa ya mata kallon ɗaya daga cikinsu ashe ba haka bane.ya kudurta a ransa ze dau mummunan mataki akan boss lady.
Ammuh da Ummah ko kadan basu,basu tausayi ba tabe baki sukayi suna watsa musu harara.
Su Abbie sun jinjina lamarin kuma sun tausaya musu sosai,ganin da cewa su din yara ne da kansu daya da ya'yansu.