← Book details Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 60

Sashe 45

Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Miƙewa ya yi yaje ya rungume Abbie yana faɗin "i missed you so much Abbie" "nayi missing dinka nima sojana "zama sukayi akan gado.
"Nayi tunanin bazaka zo ka ga Abbie dinka ba"LTG ya ce"nope ina meeting ne sorry for the delay".
"Is okay ya aiki,banyi zanton dawuwanka nan kusa ba se gashi ka dawo, amma Jawan ya sanar min bincike ne ya dawo dakai", gyadawa Abbie kai ya yi.
Sun bata kusan two hours tare suna hira,kafin ya yiwa Abbie se da safe.

Yana shiga part din sa ya tarar da Jawan, Saghar, Sudais suna jiransa.
"Very good guys,na ɗauka baku zo ba ai"ya faɗa yana wucewa dakin binciken,bin bayansa sukayi ciki suna shiga kofar ya rufe.

Suna zaune suna kallonsa ya fito da memory card din ya jona a babban system, connecting ya yi sannan ya dawo ya zauna suka fara kallo.

Fuska Barrister Lameer ne ya fara bayyana ajikin video din.yana magana murya kasa_kasa da alamu yana tsoron kar wani ya ji shine.

"Sunana Barrister Lameer muktar.ni mazaunin garin Kano ne,na samu sakon sirrine kan cewa wasu mugaye kuma hatsabibai yan ta'adda sun shigo kasar Nigeriya,wanda kasashen waje ma basu iya kawo karshen ta'adda cin su ba.sun shigo Nigeria ne da nufin kashe rayuwaka masu dimbin yawa.
Wannan dalilin yasa nasa rayuwata a cikin hatsari domin haɗa bayanai akansu nasan ba lallai in rayu ba,rayuwata dakyar ne in zan iya fita daga sharrinsu amma Allah ya fisu".
Yana gama wannan jawabin duhu ya bayyana akan screen din,duk shuru sukayi hankalinsu yana kan screen din, musamman LTG yana son yaga abinda suke shiryawa.

Mutane ne kusan su goma sha biyar zazzaune akan kujera ga tarin makamai,da bindigu,a gaban su ba iya bakaken fata bane harda turawa a cikin su.
Ogan dake zaune akan kujerar tsakiya fuskansa na sanye da mask baki irin wanda barayi suke sawa,in zasu je fashi.

Magana ya fara da turanci"babban abinda nake muradi shine zubar jini,ko da wasa wani acikin ku ya bata mana aikin da mukayi watanni goma muna shiryawa to dashi da familynsa makomarsu lahira ne,asibitoci guda ashirin ne acikin Nigeria wanda zamu dasawa boma_bomai,da Masallatai,da kuma churchs, kasuwanni,makarantu,ko ina za'a dasa bom,bayan nan kuma zamu kwashe samari mu karasu akan dakarun mu,zamu yaƙi sansanin sojaji da yan sanda,babu wa'yanda zamu kyale da rai.yan mata ɗari da daya zamuyi garkuwa dasu duk wanda yazo kawo fansar su a kasheshi,yara matan kuma zamu maida su namu,ta border za'a shigo mana da manyan makamai,da kuma sauran mutanen mu duk ta jirgin ruwa zasu zo".cikin jinjina wa da girmamawa suka fara zuba mishi tafi,hannu ya daga musu ɗan su dakata.cak suka tsaya.
"Ku tabbatar da a cikin ku duk wanda ya bata mana aiki komin muƙaminsa a cikin Italian Mafia dole ze mutu,mutuwa kuma mara dadi".
A tare suka mike tsaye sunawa kansu kirarin ƙungiya su.
"we are the mafias!, blood shed blood!,we stand with our words!,the world is ours!,we choose who to live, and we choose who to die!, mafias are the most strongest union".suna gama anthem dinsu suka fara shan giya ana shagali.
Barrister Lameer ya ce"innalillahi wainna'ilaihi rajuun,to kunji abinda wa'yannan azzaluman suke shiryawa.sunan location din da suke shine,okir......."buge wani karfen ya yi ya fadi a ƙasa yabada sauti da seda suka ji.
Da karfi" sukace waye a wajen" ku duba ko waye sannan ku kashe shi,nan take Barrister Lameer ya fara salati domin yasan tunda suka ganshi kam na shi yazo karshe.fita a inda ya buya ya yi ya fara gudu yana son barin wajen,yana cikin gudun ya cire memory cikin wayar ya jefasa cikin bakinsa.nan ne video din ya dauke gaba daya.

Ransu ya matukar ɓaci lokaci daya kuma ya tashi,suna son kashe rayuwakan al'umma da basu ji ba ,basu gani ba.
Da Karfi LTG ya daki table din gabanshi da karfi ,idon sa ya yi jajir.
Furzar da iska me zafin gaske ya yi daga bakinsa.
Sudais shafa gashin kansa ya ce"wa'yannan sun riga da sun gama shirin su,babban abin takaici shine bamu san ya kamanin sabon shugaban nasu yake ba, yana da wayo yaƙi yarda a san fuskar sa,ba musan a wani lokaci ne zasu tayar da bom din ba yakamata mu dakatar da su".
"Duk wayon sa baze taɓa kaucewa tarkona ba,koma wanene shi se na kamosa na mishi hukunci dede da Abinda yake aikatawa"LTG ya faɗa yana miƙewa tsaye.yana kallonsu"Sudais dakai zan fara, suna kokarin shigo da mutanen su da mugayen mukamai ta border,you're comptroller General,nauyin dakatar dasu ya rataya a wuyanka kabada umarni duk wani abinda za'a tsallakar dashi border daga yanzu zuwa end of this month, ka sa a rufe border babu abinda za'a shigo dashi har se da sa hannunka,saboda you're comptroller General Sudais"jinjina kai Sudais ya yi.
Maida kallonsa kan Jawan ya yi "kai mataimakin commissioner of police ne,ka zuba jami'o'i ta ko ina bama iya garin nan ba da duk sauran state. communicate with your co assistant commissioner of police".

Gyada masa kai Jawan ya yi.pointing din Saghar da hannu ya yi"Saghar make sure ku ankara a hospital daga zarran kaga wa'yanda baka yarda dasu ba don't hesitate to inform me".

Yaci gaba da magana"bana son kowa yasan da shirin da muke yi so becarefull".

"In sha Allah LTG,zamuyi nasara akan su" "very good,nasanku bakwa wasa da aikin ku, rayuwakan al'umma shine muka shiga wannan aikin akai with any cost we have to save their life's"ya ƙarishe maganar yana rike kansa dake sara mishi.yana jin kan ya fara ciwo,amma bayanin da zeyi yana da matukar muhimmanci hakan yasa yaci gaba da maganar ba tare da ya dakata ba,amma shi kadai yasan yanda yake ji,abun a jininsa yake rashin dogon magana in ba ya zama dole ba,baya dogon magana.

Kallo ɗaya suka mishi suka fahimci kansa ya fara mishi ciwo.hannu Saghar ya sa a aljihunsa ya fito da maganin ciwon kai ya basa karba ya yi ya jefa abaki ya haɗiye.

"LTG!,make sure you drink water saboda maganin ya yi melting "hararansa ya yi"ba zan sha din ba,kufa doctor's din nan ko..."ya yi shuru yana zama,dariya sukayi Jawan da Saghar suka tafa.
"Ku de anyi yan air,yanzu de kunji maganar da LTG ya yi so concentrate"
"In sha Allah ".

karfe goma na dare kafin suka bar part din nasa cike da tunanin yanda zasu kawo karshen Italian Mafia.

Se 11:00pm suka baro wajen abbu nan ma seda Hajiya babba ta korasu,kafin suka tafi.

Basu shiga bedrooms din su ba suka
shigo nasu Sabriyah suna kwance suna bacci.
"Ayyah yau nasan sun yi missing din mu"gobe se mu haɗu.
Suka faɗa yana barin dakin, Parsa kashe musu wuta ta yi kafin ta bi bayan yan uwanta.

Washe gari bayan sun karya babu wanda ya fita aiki saboda su mom Rumanatu ana hanya sun kusan sauka.

Duk wani abinda ya dace da za'a karbesu an yi sa.

Karfe sha biyu na rana suka shigo gidan,bayan yan gaisa ne suka wuce masaukinsu, Ashman da Dawood a part din Sudais suka sauka.jaleelah da Iftisan part din su parsa suka sauka.

Sauka sukayi sukayi sallah sannan suka huta,bayan sun gama cin abinci ne aka dawo falo ana hira.
Hajjatiye da a jirgi tazo ba'a motar ba amma se bala'in ta gaji takeyi,su Hajiya babba suna mata sannu,Ammuh dake hakimce akan kujera tunda suka zo sannu da zuwa ta yi musu ba ta sake ce musu komai.

"Bak'ar annamimiya,dama nasan tsinannen bakin halinki be ze bari kice mini sannu,yau da zan faɗi in mutu da kin fi kowa murna,ke kam khareema kin yi asarar rayuwa.babu yanda kika iya dani nan gidan ƴa'ƴa nane se in sa ya sake ki inga tsiyar tsinantakar da ze faru,ni maye ma haka yaganni ya barni,bare kuma ke yar adama,mara mutunci kawai". shuru wajen ya yi babu wanda ya isa yace ta yi hakuri ta hakura, mutum na sa baki zata dawo kansa.
Su Ammi de ido suka zuba musu,tun lokacin da Abbie ya auro Hajiya khareema haka kurum basa shiri saboda girman kan Hajiya khareema.shisa Hajjatiye bata santa.

"Hajjatiye wai Ni kadai kika tsana a gidan nan ne!?,duk lokacin da kika zo se kin kwashemin albarka meye na miki da zafi haka ga su hamdiyya da Badeeya,ga Abida su baƙi tsane su ba se ni!?", Bude baƙi Hajjatiye ta yi alamar mamaki"lahaula wala quwata illabilah!, khareema yanzu zagina kike yi saboda ni ba uwarki bace shine zaki za ge kina zagina ko, tabbas Mubarak yau ni matarka take zagi saboda lalacewa yakai lalacewa"ta fashe da kuka,abinda suke gudu kenan da ace Ammuh ta yi shuru batace mata komai ba da Hajjatiye shuru zatayi in ta gaji dan kanta.
Dawuwa kujerar da take zaune Abbie ya yi ya hau bata hakuri,mom Rumanatu da abbu, uncle Hameed suka sa baƙi suka bata hakuri, dakyar ta yi shuru.
Ta goge fuskarta da gefen gyallenta ta ce "nadawo kanku,yanzu meye abinda kuka ribantu dashi da kuka bar yaran nan zabga_zabga dasu babu aure cikin su babu wanda baze iya yiwa matarsa ciki ba, ɓalle a ce basu kai aure ba,dubi yan matan. duk kun haɗa yara kun barsu a gantale se anyi magana a ce wannan soja ne, wannan likita,wannan kustam,wannan police, wannan yan kasuwa,yara duk sun kosa amma kunki aurar dasu se an kawo muku jarirai daga waje a ce wani ya dirkawa wata ciki ko"duk se da sukaji kamar su nitse kasa tsabar kunya, miƙewa da sauri Hajiya babba da Ammi sukayi.
"To Ku kuma ina zakuje,anyi maganar ku aurar da yara kun wani miƙe zaku gudu,wato kun fi so ku gansu jere da ku a rasa waye uwar waye yar,to dawo ku zauna "simi_simi suka dawo suka zauna,babu yanda suka iya amma kunya kam sun sha shi.
Masifar Hajjatiye kam sun sha,ta yi hatta gaji ta yi shiru,se kuma aka dawo hirar Sudan da ita kamar ba ita ce ta gama Masifa ba.

Saghar ya ce"Hajjatiye ni fa da kince zaki samo mini mata a Sudan yanzu ya ake ciki"washe baki ta yi "yaron kirki ai matan aure kam akwai su zan sa akawo maka guda uku se dirje ka zaɓi daya a cikinsu musha biki"dariya ya yi"to ai kuwa hakan za'a yi".
Chapter 45 · 0% Book details