← Book details Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 69

Sashe 8

Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

AGE MATE'S Story & written by mommyn fareesa *Dominki* my beloved sister hafsat Aliyu D Allah yabaki miji na gari Free Page 7&8 .........Wani irin shegen murmushi irin na tsatstsar rainin hankali Ahyaan ta saki Akaro na farko har beauty point d'inta na lub'awa"yayinda doctor ya tab'e baki yayi tamkar be gani ba"saidai ya fassara murmushin nata da ma'anoni masu yawa"bedai ce komai ba kawai ya janye k'afarsa daga kan tata, sbd shine kawai yasan meya ji sakamakon had'uwar kafafuwan nasu"yadai dake ne kasancewarsa namijin duniya"ta gefen Ido yake kallonta yana kuma kallon TV "cikin yamutsa fuska ta bud'e ledar ice cream d'in tanata wani cika tana batsewa irin ita bata so d'in nan"roba gudace babba"ta d'an ja kwafa Aranta tace" yanzun muka fara indai nice"Anutse ta jefa spoon d'in cikin ice cream d'in bayan ta bud'e marfin, ta kalli ice cream d'in sannan ta maida kallonta garesa ta wani cinno baki gaba tana sakar masa harara tace" wai dan Allah baka jin kunyar sauke muguntarka Akaina?"Aganina Akan k'ato d'an uwanka zakayi hakan ba'a kan mace ba ustazah! saidai inaso kasani ! *ba girin girin ba tayi Mai*" ice cream zan sha kamar yadda ka buk'ata ,badan sbd wannan kurarin naka da burgan kaba"da zaka burgeni daka rabu dani kaje kayi wayar rage dare kaida budurwarka....zamansa daya gyara yana fuskantarta sosai yasaka tayi shiru"mitsssssuww parrot kawai!! Aida kin cigaba da surutun naki marar kunyar k'arya"tukun nah ma waye k'ato ?"ko Ajikin tace kai mana ustazah! ta fad'a tana b'abb'aka dariya, ta matsa nesa dashi ta fara shan ice cream d'in "cikin izzar nan tata tace"idan nagama sha zan maka bayanin dalilin daya saka nasha"beyi mgn ba, saidai matsowa kusa da ita dayake k'ok'arin yi"hakan yayi daidai da shigowar khaleel cikin parlourn yana rik'e da hannun hamza d'an 9yrs"Anty Ahyaan me kike sha?"cewar yaron yana kallonta"ice cream ne ! zomu sha"satar kallon yayan nasu yayi yaga hankalinsa na wajen TV"saiya nufi gefenta ya zauna"yayinda khaleel ya mik'a mata ledar farar da tace tana so d'azun da yamma,sai yaje yasiyo mata yanxun"godiya ta masa ta Azata saman center table"duk Dr darma dake zaune na lura Amma yayi kamar be gani ba"tas suka shanye ice cream d'in itada hamza tabar masa d'an sauran ya ida"yayinda suke fira jifa jifa da khaleel dake chats"yayinda Dr darma kamar babushi Acikin parlourn.....online Ahyaan ta hau ta fara chats da babbar k'awarta Khairiyyah ,tana sanar mata ta dawo KT yau"Ahaka kiran *uncle mustapha* ya shigo cikin wayarta "cikin murna ta d'auka ta fara zuba masa shagwab'arta, sbd tana masifar son Uncle d'in nata"shi kuma ya shagwab'ata sosai"saidai firan tasu batayi tsayiba ta fara b'ata rai sakamakon ya mata zancen Abokinsa dake sonta me suna Ahmed....nifa Uncle tamkar ka na d'aukesa "bana so girmansa ya zube Awajena"sai kuma tayi shiru"can tace"haka nan ni babu wanda nakeso ki?.....bata rufe bakiba darma ya dawo gefenta yayi tsaye sbd barin parlourn da yaga khaleel yayi"kawai saita saka kukan shagwab'a ta yanke wayar cikin jin haushi tace" kai kuma mlm lafiya zaka wani yimun tsaye Akai?"ice cream ne dai nasha sbd inaso"kuma dama can ba dena sha nayiba, nadai nuna bana sha ne sbd nasan burunka kaci zalin nawa ko?"shiyasa na nuna bana sha sbd nasan zaka siyo"to kaga na Aikeka sau biyu kenan yau"ga siyo ice cream ga kuma dakon mun troley d'in kayana da kayi"kajira sauran cikon Aiken na ukku"saita juya Ido tayi y'ar dariya tana koma fad'in kuma bakina daka d'allah d'azun bazai tashi Abanza ba saina rama....tunda take maganar Miskilin ke binta da kallon k'asan Ido yana danna waya"zaka d'auka kamar ba jinta da kallonta yakeyi ba"saidai beyi mamakin kalamanta ba, dama ya santa tun suna yara bata k'arya, zata fad'i gaskiyarta komai d'acinta"saidai bece komai ba shi Aganinsa yanzun za'a fara nasa lokacin"faranta data manta dazai iya d'auka yayi saurin d'auka bece komai ba....meye haka Nurahhhhhhh! ? kaga ka bani Abuna nace maka"banza ya mata ya wani had'e rai ya sakata cikin Aljihun jallabiyar jikinsa"tayi saurin mik'ewa tsaye cikin tsawa tace ka bani Abuna"saida yakai bakin k'ofar fita daga cikin parlourn kafin cike da gadara yace"Ank'i Abaki d'in, na k'arfi ne kizo ki k'wata idan zaki iya Amma "yana fad'in hakan yasa kai ya fita"k'aramar hijab d'inta dake gefenta ta d'auka da sauri ta saka ta biyosa tana kiransa" saidai yamata Nisa ,yama nufi sashensu mamah"hakan yasa itama tabi bayansa.....Ayadda darma ya tsara shine yabama Asma'u faran, sannan yayi sanadin dazai sakata Aiki"yasan dole sai tayi kuka"sbd ransa yabashi saita biyosa nan d'in...."saidai yana doso tsakar gidan yaji muryar Mubarak na rashin Arzik'i yana fad'in "duk Arasa d'an iskan Abincin da za'a zubamin sai wannan nida gidan ubanah"ni gaba d'aya gidan nan idan ba ummah keda girkiba bana ci na k'oshi.....lallai babbar mgn! to bari shi iliyasun yadawo Ina nan zaune"sai naji dalilin dayasa idan zainab tayi girki bata zuba maka wadatacce?cewar innah Asabe da har lokacin tana zaune gidan bata tafi nata gidan ba"mamah na fitowa daga cikin parlournta Darma na Ida shigowa tsakar gidan rai b'ace "sbd ya fahimci Mubarak mama yakema rashin kunya..... k'ananun maganganun mena keji Anayi ne?"cewar mamah dake tsaye fuska Ad'aure sbd ta tsani raini"ahhh dole ki tambaya mana sbd kinsan baki kyautaba "ki rasa d'an Abincin da zaki zuba masa sai wannan?"damafa innah indai ita tayi girki haka take zubamin Abinci.....you are very stupid! kanada hankali ne ko kuwa shaye shayen daka fara ya tab'a maka brain ne??"cewar darma cikin daka tsawa" yayi wata iriyar tsayuwar k'asaita irinta isassun mazan da suka Amsa sunan su maza"saidai kyakykyawar fuskar nan tasa Atsuke take"yarasa meyasa duk yaran ummah basuda tarbiya??.....cak? tunaninsa ya tsaya sakamakon shigowar Ahyaan daya gani cikin gidan ,wacce taji kuma kalaman innah dana Mubarak dana shi darma d'in "Azuciye ta nufi inda Mubarak yake tsaye"Adaidai lokacin ummah ta fito daga cikin parlournta dama, shak'e take da darma sbd ya canzawa mamah kujeru banda ita"kai kuma waye ya tsomo dakai Anan?ko kuwa waya kasa dakai balle ka d'auka?da zakazo har gida ka masa kazafin shaye shaye "ko kai can dakaje k'asar turai bamusan meye kakeyi ba ac.....shiru tayi sbd k'arar sautin gigitaccen marin da Ahyaan ta d'auke Mubarak dashi"Azuciye tace kaci kutumar ubankah! yaushe aka haifeka har kayi wayon gayama mama mgn?"cikin zafin rai yad'ago kansa da nufin ya rama"Ahyaan ta kaimasa hauri gefen ciki ta turashi iya k'arfinta "ji kake rikicah ya fad'i k'asa"yayinda kowa ke binsu da kallo"mamah tama kasa mgn"luba kuma Atsawace tace" dan ubanka zaunawa zakayi ta dakeka?"innah Asabe kuwa salati ta kamayi wai mamace ta sakata tayi hakan"yayinda uban gayyar ke tsaye beyi mamakin Ahyaan ba sbd yasanta tun suna yara tanada zuciya gata da k'arfi "da sauri ya nufeta sbd ganin Mubarak yayo kanta"ita kuma ta rik'e k'ugu bbu Alamar tsoro Atare da ita tana jiran taga meye zai mata??....saidai tun kafin ya Ida isowa gareta yaji jarumar muryan darma yana fad'in wlh hannunka yatab'ata da nufin duka saika kwana Asibiti yau"ya k'are maganar yana isowa gefenta"babu wasa kan fuskarsa sbd ya lura yaron naji da rashin kunya, tunda yadawo ko gaishesa ba yayi...Ina ruwanka da fad'an su da zaka shiga?"cewar ummah cike da bala'i inna Asabe na tayata"kaga Nura! kama hannunta ku tafi wajen mamy "cewar mamah dake kallonsu"saidai kafin suyi mgn Mubarak ya matso ya cakumi Ahyaan "Aikuwa Afusace darma ya fisgosa da hannu guda ya fara bashi wasu zafafan puncher's"luba da inna Asabe suka saki kururuwa "kaga Nura dan Allah rabu dashi"mamah kibarsa ya casamun d'an iska.....duk wata y'ar iska ta wuce ke?"cewar ummah"hakan yafaru kan kunnan Abba daya shigo tsakar gidan "Adaidai lokacin kuma Nura yatura Mubarak ya fad'i k'asa da fasheshshen baki"Ahyaan ta fad'a jikinsa ta saki kuka mecin rai tana fad'in na tsani gidan nan broth KD zan koma bazan iyaba.... wallahil Azeem bazan yardaba ! saika san ka dakesa harka fitar masa da jini"cewar ummah dake duk'e gaban Mubarak"mama kuwa sallamar Abba ta Amsa tana d'aure fuska"da kallo one by one Abba ke kalle tsakar gidan da mutanan dake cikin gidan...meke faruwa ne zainab?"yafad'a yana kallon mama"to Alhamdulillah daka dawo daman zaman jiranka nakeyi....kinga yaya Asabe ban tambayeki ba zainab na tambaya"Abba ya katseta yana yin kicin kicin da fuska"Nura ya kalli Abba yamasa sannu da zuwa kafin yaja hannun Ahyaan suka fita daga cikin gidan"ummah na huci tanata zage zage"yayinda mama ta shiga yima Abba bayanin Abinda ya faru "ta d'ora da fad'in ga Abincin can gabansa Alh kaje duba ka gani"sanin kankane idan Abdul Aziz ko Affan na nan Mubarak be isa ya gaya mun mgn ba....ke dallah rufema mutane baki"tunda kin shanyesa dama ba laifi kikeyi wajen saba dole yaji maganarki....kinga yaya Asabe yanzun k'arfe 9 saura ki tashi ki tafi gida"Al'amarin gidana ki dena shiga tunda bazaki yi hukunci domin Allah ba kina biye son zuciya"Abinda Ahyaan tayi da Nura sunyi daidai"uwa ta wuce wasa"tunda nake da yaran zainab basu tab'a yima luba rashin kunya ba"ita kuwa nata yaran iya sanina sau nawa suka yiwa zainab rashin kunya "to bari kuji ku duka"gida! gidanane na Isa dashi"duk wacce bazata iya bin umarnina ba a shirye nake dana rabu da ita ba wani abu bane"shi dayake d'an iska ne har yayi girman da zai raina Abincin da aka bashi tunda shike nemowa ko?"ko buhun shinkafar dasu taliya da sauransu dake Ajiye ana girkawa,Nura dasu Abdul Aziz ne suka siya suka Ajiye cikin gidan"uban me ya iya inba sama ciki ba....yaya Asabe kin yadda da maganata ko?"cewar luba cikin k'unar rai"tabbas na yadda ,bara na tafi gida tun kafin Akoma korata"ke kuma zainab inaso kije ki canza sabon shiri...wlh wlh !! bazan yadda ba" kotu zata rabamu da matsiyacin yaron nan"ki duba ki gani kofa numfashin kirki yaron nan baya yi....cikin b'acin rai Abba yace" kisan yadda zakiyi dashi tunda shi yakama kansa"saidai inaso ki sani muddin kika jema kabeer da zancen Nura yadaki Mubarak ko kika yima Nura wata mgn bakin Aurenki"kuma duka nake nufi"yak'are maganar yana shigewa parlourn mamah"ba b'ata lokaci tabi bayansa "inna Asabe fita kawai tayi batace komai ba, tana tunanin ya zatayi da Abin hawa tunda batada kud'i?"ga yana yin yadda Abba yake ba halin tace yabata wani Abu"ummah kuwa tamkar k'aramar yarinya haka takama kukan bak'in ciki"tanajin Aranta saita kassara rayuwar Ahyaan data mamah"tana zaune tana cin mugun k'udurinta"Affan
Chapter 8 · 0% Book details