Sashe 3
Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
AGE MATE'S Story & written by mommyn fareesa *dominki* my beloved sister hafsat Aliyu D Allah yabaki miji na gari *Tukwici ne* gareki raudah mohd sokoto *sadaukarwa* ne gareki zainab hamisu wada in yinki irin sau babu Adadin nan tawan Free page 3&4 .......A hankali ya d'ago fararen idanunsa masu girman gaske da yake yawan lumshe su, karan farko ya saukesu A kanta ba tare daya furta komai ba.....*wato har yanzun fitsararriyar yarinyar nan bazata dena jin kai da izza ba?* yafad'a Azuciyarsa yana matsota sosai har tana iya jin hucin numfashinsa daga gefen bayanta"tsabar miskilan cinsa da jin kai irin nasa k'in tankata yayi"saidai kawai taci An finciki hannunta da k'arfin gaske har saida tasaki k'aramar k'ara"wanda yayi hakanne sbd ganin zata shige cikin nafef d'in bayan ta saka troley nata ciki...A wani irin harzuk'e ta juyo ta balla masa harara tare da jan tsaki ta fara k'ok'arin k'wace hannunta"hakan kuma yayi daidai da isowar Mr mahuta gefensu ,yayinda mu'az dake zaune cikin mota da wasu masu wucewa suka fara kallon su....mlm Akan meye zaka kama tab'ata, harka hanata shiga nafef??"cewar mahuta cikin hura hanci"saidai DARMA da yafishi zafin kai saima ya nuna kamar ba dashi yakeba"be kuma cika tan ba saima troley d'in kayan yake k'ok'arin fitowa dashi daga cikin nafef d'in da gudan hannun sa"yayinda gudan hannun nasa yake rik'e da hannunta...ganin da mahuta yayi beda Alamar nuna yasan dashi yasaka shi kallonta yace"baby ko kin sanshi ne?"mlm wai Ina ruwanka dani ne dallah?"ta fad'a Amasife "me makon yaji haushi saima murmushi yasakar mata"ita kuma ta saci kallon k'afar Darma dake cikin takalmi boot"saita Aza k'afarta me tsakalmi masu tsinin gaske ta take masa tasa k'afar "tabbas yaji rad'ad'i Atsakkiyar k'afarsa Amma da yake inbgarman namijin duniya ne koma a fuska be nuna mata yaji zafin ba"har k'ara rintse Ido takeyi tana take masa k'afar Amma yamata banza yana Ida ciro troley d'in daga cikin nafef ya finciketa da k'arfi suka nufi wajen motarsu....mahuta kuwa be hak'ura ba saima ya biyosu Abaya"sai'a lokacin mu'az ya gane fuskar Mr mahuta....wai bazaka cikani ba?"ta fad'a cikin tsawa tana kiciniyar fisge hannunta"Amma isheshshan kamar badashi take mgn ba, ya bud'e back sit yaturata ciki da k'arfi"sai hannunsa ke rad'ad'i na dama sbd yagin data masa da farcenta"be tanka taba ya sako troley d'in kayan cikin motar yayi tsaye yak'i rufewa"yakoma binta da wani irin kallo fuska Ad'aure "ita kuwa k'in yadda ta kallesa tayi"sai yaja tsaki yana fad'in marar kunyar banza"yana fad'in hakan ya rufe k'ofar back sit d'in da k'arfi"kafin ya juyo ya kalli Mr mahuta dake tsaye yana kallonsu"cike da Isa da izzah ya matso gabansa! Ido cikin Ido ya kallesa yana sakin wani shed'anin malalacin murmushi yace"meya hana ka hanani na shigar da ita cikin motar ne?"Amsa itace babu! sbd baka Isa ba"zan baka shawarah guda biyu"na farko kadena shiga shirgin da banaka ba"sannan kasan da waye yaka mata kayi fito na fito"domin da kura kawai Ake wasa"zaki kuwa saidai kallo daga nesa ,ko shafar jikinsa sai An had'a da dubara akeyi....yana fad'in hakan ya juya idanunsa yana koma sakin k'aramin murmushi ya shafi lallausan sajensa yayi gaba yabar masa daddad'an k'amshin turarensa....*miye gadararsa?* cewar Mr mahuta da yayi suman tsaye kalaman Darma na Amsa kuwwa Acikin kunnansa"saidai bashida Amsar wannan tambayar"saidai yasha Alwashin bincikar yasan waye shi,meye matsayinsa wajen wannan zuk'ek'iyar yarinyar?? "da lokaci guda yakejin kwad'ayi kasancewa da ita(wa iya zubillah )......yallab'ai zamu iya tafiya komai na boot mun shirya....yaji muryar wani body quard d'insa "bece komai ba yabi bayansa.....tunda DARMA ya nufi gaban mahuta suna mgn mu'az gabansa ke fad'uwa"yasan Darma kaifi d'aya ne baya tsoro balle shakka"saidai bayaso ya had'a wasansa da irinsu mahuta, sbd shed'anu ne kuma tsageru"masu tak'ama da shiyasa da nera kuma.....saidai Abin nan daya faru yanzun yasaka ma zuciyarsa kokonto game da Abokin nasa"juyowa yayi ya saki murmushi sbd jin Ahyaan na waya da Mamy tanata shagwab'a da had'ama *darma* bom Awajenta"tana cikin wayar ya shigo cikin motar Afusace ya wani tsuke fuska yanata ciccin magani"shi dariya ma muaz yaji ya bashi Amma saiya basar ya juyo ya kalli Ahyaan data kashe wayar suka had'a Ido"y'an matan Mamy! yaya mu'az Ina wuni? lafiya qlau Ahyaan"An gama service ko?"Eh wlh"to Allah yakawo babban rabo ,ta Amsa da Ameen"tana d'an murmushi domin tana ganin girman mu'az "musammun data san ya girmesu suna dai Abota ne kawai da darma Amma ya bashi 3yrs shi yanzun kusan 31yrs garesa......uban gayyar kuwa ba k'aramin haushi yaji ta koma bashi ba "wato shine marenin wayonta take kiran sunansa tsagaga"koma da take gadarar shida ita *Age mate ne* Ai ya girmeta tunda 8days yabata ko?"shine zata girmama Abokinsa shi kuma marainin wayonta"idan ada ya k'yaleta tana masa Abinda ta gadama yanzun ya tattakata k'aramin Aikinsa ne wlh"sai kuma ya saki murmushin mugunta daya tuna yadda take masifar tsoron allura Abaya "ga kuma bata son ta hau mota ko mashin Ana sharara gudu da ita"wannan tunanin yasaka yak'ara wani irin gudu"ta d'ago kanta cikin fad'uwar gaba fuska Ad'aure tace"mlm meye haka kake sharara irin wannan gudun?"sai lokacin mu'az yayi mgn gun fad'in, haba Darma! ka sassauta mana tunda bamu kad'ai bane"kuma nina d'auka sai mun fara Ajiyeta gida sannan zamu tafi inda zamuje"ya d'auki kusan second 5 kafin Anutse yace"Acan zamu fara zuwa"gudu kuma bazan rage ba"sai me idan bazaka rage ba?"na lura har yanzun yaron nan rainin daka mun yana nan Amma wlh daidai nake dakai.....ba k'aramin hassala gogan naku yayiba da kalamanta, musammun da mu'az yakama dariya"saurin cin burki yayi sbd ganin sun kusan bangazar wata mota"Ahyaan ta saki k'ara tana rintse Ido had'e da salati....wai Darma kashemu kake so kayi ne?"tsaki yaja yana gangara gefen hanya yazaro waya yana danawa "wai meye haka muje mana sha biyu da rabi ta kusa fa?"babu inda zamu tafi sai naga k'arshen rashin kunyar yarinyar nan "Ashema yarinya? Ina yayar taka zaka.....juyowar da yayi yasaka tayi shiru sbd ba k'aramin tsorata tayi ba da irin kallon dayake jifarta dashi"saidai dayake itama ba baya bace wajen jin kai saita nuna kamar kiran wani ya shigo cikin wayarta"saita kama kara wayar gefen kunne tana yamutsa fuska.....pls Abokinah yaka mata ku dena irin wannan kufa ba yara bane kaja mota mu tafi pls"kwafa Darma yaja sannan yaja motar suka d'auki hanyar Anguwar *sha gari low-cost* ......rai b'ace Ahyaan ke fad'in wai dama ba gida zamuje ba?"idan har bacan zamuje ba ka saukeni na hau adaidaita"ko kuma wlh na kira Mamy na sanar mata"Akanme daga dawowata zan fara da takaicinka?"sai kuma ta saki kuka sbd ba k'aramin zafinsa taji ba"Tasha Alwashin saita masa Abinda shima zaiji b'acin rai da damuwa"shi kuwa fuska yasaki sbd yaji dad'in kukan daya sakata"mu'az na lura dashi ya girgiza kansa ya juyo Anutse yace "kiyi hak'uri Ahyaan pls"dama zamuje gidansu Fatima ne yarinyar dazan Aurah zasu gaisa da ita ne sbd bata....look mu'az! dole saika mata bayani da wani bata hak'uri ne?"kar Allah yasa ta hak'ura d'in"zuwa bbu fashi k'afarmu k'afarta har cikin gidan su saita shiga idan munje kice bazaki shigaba ni kuma kiga yadda zanyi dake "yafad'a cikin fad'a kamar wani ubanta"tsabar mamakin kalaman sa k'asa mgn mu'az yayi"ita kuma tana rantsuwar be isa yasata tayi Abinda batayi niyaba "sai yaja kwafa be koma mgn ba har suka iso bakin get d'in gidan su Fatima"yana jin Ahyaan na masa rashin kunya "saidai maganar k'asa k'asa take yinta banza yamata yayi parking bakin get....... *Asalin labarin* Alh kabeer *Darma* da Alh iliyasu Abokan junane tun suna yara har zuwa girmansu"haifaffun garin katsina ne kowa nasu na'a can"kabeer iyayensa na zaune Awata Anguwa me suna *DARMA* ! yayinda iliyasu ke zaune da iyayensa a Anguwar *sabon layi*".....tun daga primary school har zuwa secondry skul tare sukayi har zuwa jami'a"sun shak'u da juna da wani irin sabo da juna, kuma da wuya aji kansu saidai halin yau da gobe"suna zumunci tamkar y'an uwan juna ne"ga wani irin had'in kai suna dashi"duk sun taso suna kasuwancinsu da kuma Aikin gwabnati"har Allah yasa kabeer ya tashi Aure da matar da zai Aura wacce ke y'ar Kaduna"lokacin kuma harma sun kammala ginin gidajensu dake jere"sai suka zagayesa da get babba"lokacin shi iliyasu be fidda wacce zai Aura ba"saidai shima yanada niyar yayi idan yasamu wacce yakeso"kwatsam da aka tashi hidimar bikin kabeer da kyakykyawar matarsa Maryam(Mamy)" sai Allah ya had'a jinin iliyasu da babbar k'awar Maryam me suna zainab(mama)"Aikuwa Ana gama hidimar bikin kabeer da Maryam soyayya me zafi ta k'ullu tsakanin iliyasu da zainab"saidai iyayen zainab masu kud'i ne matuk'a"mahaifiyarta taci burin bayan gama secondary school nata taci gaba da karatu"sai mahaifinta ya Ankara da zainab na soyayya yace ta turo da wanda takeso yazo zasuyi mgn"Hjy Amina (Ammah) itace mahaifiyar zainab"macece me nuna Isa da gadara akan dukiya bata son had'a zuri'arta da talaka "saidai bata cika wulak'anta mutane ba"tunda ta fahimci iliyasu bamai dukiya bane shikenan ta nuna bata son Auren Amma mahaifin zainab Alh murtala yafi k'arfinta,kuma zainab nason iliyasu,gashi beda matsala mutumin kirki ne"hakan yasa Akayi wannan Aure"yazo daga baya yace"bazata cigaba da karatu ba"Abin yayima Ammah ciwo matuk'a ta kuma k'ullaci iliyasu"saidai baban bece komai ba"zaman farin ciki da kwanciyar hankali su zainab da Maryam suka cigaba dayi Agida Jen Auren su"dukda zainab tafi Maryam komai na kayan d'aki Amma Maryam bata tab'a damuwa ba suna zamansu tsakani da Allah"zamansu Awaje guda yasaka mutanan Anguwar ke kiran gidan nasu da suna *gida biyu*" Maryam data samu ciki saiya b'are tun kafin zuwan Zainab "sai gashi cikin ikon Allah bayan zuwan Zainab gidan ta fahimci tanada ciki"bata jumaba da fara laulayi itama zainab ta fara"haka sukayi zamansu su girka wannan su su girka wancan duk Abin kwad'ayi"sannu A hankali cukun nan nasu suka fara girma saidai cikin Maryam na gaban na zainab da wata guda"sai Akayi sa'a Maryam ta k'ara sati biyu sannan ta haifi santalelen d'an ta namiji kyakykyawa (Nura)"kwanansa 8 Aduniya zainab itama ta haifi y'arta mace kyakykyawar gaske(Ahyaan)"sati na zagayowa iliyasu yasaka mata suna *Aminatu*"sai mamy ta dinga kiranta da Ahyaan"dukda Ammah Ammata takwara ba taji iliyasu ya burge taba kullum kushesa takeyi.....yara suka taso cikin gata da kulawa"har sukayi shekara biyu"lokacin iliyasu da kabeer suka biyawa kansu makka"sai mahaifin zainab yabiya mata"kuka ta kamayi ita bazata jeba sai tare da Maryam"sai kuwa