Sashe 48
Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
gama tsarawa Ahyaan make up na musammun "da yayi masifar fito da kyawun fuskarta"kallo d'aya zaka mata ka fahimci ita d'in Amarya ce"saidai Sam fuskarta ba walwala"tana sanye da shadda giznah lue, d'inkin doguwar riga"wacce Akayima bichwork da pink d'in zare"sai k'amshi ke tashi jikinta irin me kashe zuciyar nan"mutanan dake cikin parlourn su bakwai sai yaba tsarin kwalliyar tata sukeyi"Amma ita zuciyarta Acunkushe take"bayan tafiyar me make up d'in" babu yadda Khairiyyah batayi da itaba ta yadda ta mata pics sai cewa tayi ita bata so"zuciyarta na ingizata data kira Dr darma saidai tana jin rashin dacewar hakan saita hak'ura"lura da damuwa ta mata yawa yasaka Khairiyyah janta gefe sbd ga bak'i friends nata irin na cikin Anguwa sun fara zuwa be kamata su fahimci batada walwala ba "hakan yasa tad'an b'ata baki Akan ta sake sbd ga idon mutane"Adole ta k'ak'aro fara 'ar dole ta zauna tana jin sunata mata shakkiyanci"mamy kuwa tana can d'aki tana shiryawa hakama Acan side d'in su mama"harta shirya cikin sabon leshi...yyinda zuciyar ummah bayan bugawa babu Abinda takeyi"sbd ganin ba'a fasa shirye shiryen komai ba"saidai ta zuba Ido taga shin za'a d'aura Auren ko kuwa?.....tunda lokacin d'aurin Auren yayi gaban Ahyaan ke fad'uwa har tafara jin Ana bud'a Alamar Aure ya d'auru kenan...innalillahi wa inna ilaihir raju'un ! shine ta dinga fad'a Aranta Atake taji zuciyarta tad'an lafa saidai k'irjinta nata fat fat!! "mamy ta fito daga cikin bed room d'in ta wanku cikin leshi orange me zanan coffee brown"An d'aura mata d'an kwali "ta shafa jambaki "sai tayi kamar itace yayar Amaryar sbd kwalliyarta ta b'oye shekarunta.....Masha Allah my lovely daughter! ta furta tana murmushi had'e da kallon Ahyaan d'in tace"Alhamdulillah Aure ya d'auru gashi can Ana bud'a "bata rufe bakiba uncle mustapha dashi da Amininsa Alh Ahmed (wanda yaso Ahyaan Abaya) suka shigo cikin parlourn da sallama yana fad'in kai tsaye nan na iso wajen uwar biki. kece uwar Amarya kece uwar Ango....k'irjin Ahyaan ya buga! suka kalli juna itada Khairiyyah Alokaci guda"Adaidai lokacin mamy ke musu maraba tana murmushi tace"uwar dai Amaryar nake"sai yayi dariya suka zauna suka gaisa"kafin yace Ahyaan da Nurah kuma And'aura Aure?"to Allah yasa Alkhairi yabasu zaman lafiya da zuria dayyiba.....daga Mamy har Ahyaan zuwa Khairiyyah kansu ya k'ulle sun kasa gane me kalaman Uncle mustapha ke nufi?"saidai kawai mamy ta Amsa da Ameen"muryar Ahyaan A sark'e ta gaishesu"ya Amsa tare da cewa ga Abokinah yazo ya miki fatan Alkhairi"yak'are maganar yana duban Alh Ahmed"yaga gaba d'aya hankalinsa na wajen Khairiyyah dake gefen Ahyaan Azaune . d'an murmushi ya saki ya dafa gefen cinyarsa saiya kallesa yanuna masa Ahyaan"numfashi ya sauke tare da cewa" Amarya Allah yasa Alkhairi yabaku zaman lafiya "Khairiyyah ta Amsa da Ameen sbd Ahyaan tayi shiru.... Khairiyyah ki kama uncle's d'in naki drinks da snacks mana"cewar mamy tana wucwa ciki itada bak'i "ba musu Khairiyyah ta tashi ta fita"Alh Ahmed yace"Ahyaan wannan k'awarkice?"uhmm! tanada Aure ne?"ah ah"okay tunda An kasani to Ina kamunta"duk sukayi murmushi gaba d'aya"Adaidai lokacin Khairiyyah ta dire musu tray d'in gabansu"ta zauna cikin rashin sakewa sbd irin kallon data lura Alh Ahmed na Aiko mata dashi "drinks kawai suka sha suka fita"Ahyaan dai batada nutsuwar sanarwa Khairiyyah da komai sbd kalaman Uncle mustapha sun tsaya mata Arai tana son fassarasu Amma ta kasa .tana wannan tunanin Isma'il ya shigo da shirinsa na d'aurin Auren yace"Anty Ahyaan mamy tazo inji daddy yana parlourn sa"dato Khairiyyah ta Amsa taje ciki ta sanarwa mamy "kusan Atare suka fito daga cikin d'akin"ita mamyn ta fita.....bata kuma jumaba sosai ta dawo fuskarta fad'ad'e da fara'a tazo ta kama hannun Ahyaan tana fad'in taso muje daddynki da Abba na son mgn dake"jikinta na kirma ta tashi tabi mamy suka fito tsakar gidan"suna k'ok'arin shiga cikin parlourn Dr darma ya shigo tsakar gidan "wanda k'amshin turarensa kawai Ahyaan ta shak'a ta fahimci yana kusa da ita"k'irjinta na tsananta bugawa ta d'ago kanta cikin sa'a idanunsu suka sark'e cikin na juna.... wani irin kallo me nuna tsananin k'auna da kashema masoyi jiki Dr darma ya dinga jifarta dashi"saita kauda kanta tana jin fad'uwar gaba....wuce ki shiga ciki"taji muryar mamy na cika hannunta"batayi mgn ba ta shige cikin parlourn"mamy da Dr darma suka had'a Ido ya saki murmushi "itama murmushin tayi sbd tasan dama yana son Ahyaan.mamy sannu da gida ya hidima?"Alhamdulillah kaje ciki mana"ta fad'a tana yin gaba"Ahankali ya shiga ciki da sallama"daddy da Abba na zaune saman kujerah"yayinda Ahyaan ke zaune k'asa kan carpet ta sunkuyyar dakai k'asa"zuciyarta nata zillo da sak'e sak'e. Agefenta shima ya zauna yayi k'asa da kansa"daddy ya fara da cewa Alhamdulillah! muna godiya ga Allah daya nuna mana zuwan wannan rana me Albarka"hak'ik'a ikon Allah ya wuce wasa"Ada mun saka ranar Auren Ahyaan da Abdallah to gashi kuma da Allah yace takace Abubawa sun sauya ta zama mata Agareka"Ina fatan zakuyi farin ciki da mallakar juna da kukayi Amatsayin ma'aurata"ke kuma mama nah Ina fatan zaki kasance me biyayya garemu da kuma biyayya ga mijinki"wannan yaro Abdallah yaso yabamu kunya sai Allah be nufa ba"sbd haka nurah ga Amanar y'ata nan na damk'a Ahannunka...nasan mamanah kin shiga Aduhu ko?"to Atak'aice dai Abdallah yazo da kansa munga Abubawa game dashi bbu Alamar kai sarki gida yasaka muka fasa bashi ke"Ina fatan zab'in mu ya miki ko?"kanta Ak'asa cikin sanyin muryarta tace"banida ta cewa daddy komai kukayi game dani zan kasance me biyayya in sha Allah "to Alhamdulillah Allah yayi muku Albarka"Dr darma ya Amsa da Ameen tare da cewa"daddy da Abba nagode sosai Allah yasaka da Alkhairi"iyayen na murmushi suka Amsa da Ameen! Ahyaan zaki iya tafiya kinji ko?"dato ta Amsa ta mik'e tsaye kanta a sunkuye ta fita tana jin kamar ta taka rawa sbd farin ciki Allah yabata Abin k'aunarta....nurahhhhh! Daddy ya kirashi da d'an k'arfi sbd yaga gaba d'aya tunda ta mik'e tsaye yake binta da kallo babu ko k'iftawa"d'an sosa k'eya yayi yana fad'in na'am daddy"duk sukayi murmushi irin nasu na manya"dama Akan batun tarewar nakune zamuyi mgn"inaga sai mu barshi kamar bayan sati 2 zuwa lokacin mun samu inda zaku fara zama ko?"kansa ak'asa yace"ku gafarceni daddy inada gida saidai ban Ida kammala waba Akwai d'an saura"in sha Allah nanda sati biyun ko ukku sai Asamu a Ida"dama na barine saina Ida kawai nayi surprise d'in ku"Amma su Abdul Aziz da khaleel da mamah sunsan da gidan"to Alhamdulillah! Masha Allahu"sai Abarshi sati ukkun zamu Ida maka Amma ka sani dole kayi mata lefe....ah ah na soke batun lefe Alh kabeer! cewar Abbah "babu ruwanka Anan nine uban d'iya "idan be kawo lefe ba saina rik'e y'ata"shikenan saika yita ruk'o,nurah tashi kaje bbu zancen wani lefe Ai da kayanta..,be rufe bakiba Asma'u tayi sallama ta duk'a tana fad'in Abba kazo inji Ammah "saida gaban Abba ya fad'i"saidai be nunaba,ya kumaci burin muddin game da Auren Ahyaan da Nurah zata masa k'orafi wlh zaya bata mamaki.saida nurah ya fita sannan Abba shima ya fita....koda ya fita inda mu'az yake ya nufa sukaje sukayi order d'in Abinciccika irin na y'an gayu da drinks suka turo Aka kawowa Ahyaan tabama friends nata.....Acikin gida kuwa da mamah taji dawa Aka d'aura Auren "farin ciki tayi da musu Addu'ar samun zaman lafiya "sbd dama burunta be wuce Ace yaranta dana Aminiyar tata sun had'asu Aure ba kodan zumuncin nasu yak'ara d'anko.kuma da Abba ya kirata yamata bayani ta gamsu ta goyi bayan shawaran da suka yanke shida daddy....Abangaren ummah kuwa koda taji labarin dawa Aka d'auran saida ta shiga bayi sbd tsabar firgita da tashin hankali "yo ita dadai nurah ya Auri Ahyaan Ai gara ta Auri Abdallah d'in"Aikuwa da wuri gobe zatayi k'aryar mahaifiyarta ba lafiya zata fita taje wajen boka ya k'arya sihirin Amaida jikin nuran saiya saketa.itada take da burin nurah ya Auri Khadija shine za'a manna masa Ahyaan?"gaba d'aya duk yadda taso ta b'oye hassadarta kasawa tayi"ga dangin Abba sun juya mata baya sbd ganin yadda mamah keta labto musu Abin duniya irin na biki sai suka share ummah suka cigaba da hidima Abinsu"Ammah kuwa ranta yab'aci da had'in da Abba yayi"taso Ace yayi shawara dasu itada mijinta"ita Aganinta kamar Ahyaan tafi k'arfin Dr darma "sbd Ayadda ta d'auka ko gidan kansa be dashi"may be ma k'aramin likitah ne inba kyawunsa ba uban me zai bama jikarta?"hakan yasa ta tura Asma'u ta kira mata Abba"kasancewar y'an KD tun jiya suka iso zo"kuma Akwai gida a shagari low-cost da mahaifin mamah ya siya idan Ana wata hidima nan KT sai su y'an KD d'in su sauka Anan"to Acan suka sauka yau da safe suka zo gidan"Abba kuma koda ya baro side d'in su daddy sabgar gabansa yakama daga k'arshe yabar gidan ba tare da yaje kiran sarakuwar tasa ba.jin shiru be zoba ya k'ara k'ular da Ammah sai batace komai ba ta bari gobe da safe y'an biki sun watse za'a yi wacce za'a yi"Amma bazata bari jikarta tayi Auren wahala ba.....bayan k'arfe 4 na yammah Ahyaan da frineds nata na zazzaune Akan plastic chairs Atsakar gidan"An canza mata sabon make up da Alama wancan da zatayi sallah Aka wankesa"tana sanye da wani tsadaddan cotton lace me kyau purple colour d'inkin doguwar riga gownt! tayi kyau harma tafi d'azun "Khairiyyah babbar k'awa na mak'ale da ita"tunda ta tabbatar ita d'in ta zama matar Dr darma taketa tsokanarta"ita kuma Ahyaan tana cemata ta rasa wanda zata so sai k'aton tuzuru"sbd itama Khairiyyah Alh Ahmed yamata"ba kunya tacema Ahyaan Ai dama ita tafi buk'atar ta Auri tuzurun sbd sai irinsu ke iyawa da ita"friends nasu y'an mata da matan Aure sunata shewa da y'an ciye ciyen Abinciccika"Ahaka Dr darma da mu'az da Hafiz da Dr Jamaal damai photo suka shigo tsakar gidan"tun daga nesa yake jifarta da wani tsadaddan murmushin dayi masifar yi masa kyau"ya cakare cikin shadda milk colour"d'inkin me gajeran hannu "ya fito cikin coffee brown irin kalar Aikin jikin shaddar"gaba d'aya k'amshin turarensa yacika wajen.khairiya da Fatima da tun d'azun tazo suka fara fad'in ga Ango nan"gaban Ahyaan ya fad'! i tad'an d'ago kanta taga gaba d'aya ita yake kallo"murmushi ya sub'uce mata ta wani tsuke lips nata da suka sha jam baki da kwansila"ba kunya Dr darma ya nufi inda take zaune kai tsaye"wanda keson saninsa suka dinga kallonsa suna furta Masha Allah! shidai mu'az da