← Book details Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 69

Sashe 24

Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

da haske sbd gyaran fuskar da yayi"tamkar baya so haka yayi sallama Atsakar gidan"k'irjin Ahyaan ya buga! saidai bata d'ago kanta ta kallesaba"yayinda sadeeq ya juyo ya kallesa yana furta masha Allah Azuciyarsa"shi kansa dake namiji yaji ya burgesa inaga mace??"shi kuwa uban gayyar dakewa yayi sbd lura da sadeeq ya gansa" sai kawai ya iso gefensa yayi tsaye yana jin kamar yadinga bashi puncher's "sbd ganin yadda ya zage yanata zuba mata surutu Amma ta masa banza....yanda yayi tsayiwar k'asaita ya hard'e k'afafuwansa waje guda, idanunsa na'a kan waya yana danna"saika rantse da kamar baya a wajen.....likitah bokan turai! yanzun gaisawa zamuyi ko da wayar zan barka?"d'an sakin fuska yayi k'ok'arin yi ya bashi hannu sukayi musabuha "ya Aiki?"Alhamdulillah "to Allah ya taimaka"Ai jiya naga firanku A tv "game da matsalar k'oda....."karon farko Ahyaan dake saurarensu ta d'ago kanta da mamaki "sai Akayi sa'a shima Dr darma ya waigo da nufin yabar wajen ma"sai suka had'a Ido "saurin d'auke kanta tayi "ya yamutsa fuska zai nufi parlourn mamy zai shiga "Adaidai lokacin wani yaro ya shigo yace Ance Ahyaan tazo"kace bata nan kana jina?cewar Ahyaan tana zarema yaron da aka Aiko Ido "kai je kace gata nan zuwa"cewar mamy data lek'o daga cikin parlourn "fasa shiga cikin parlourn Dr darma yayi saima ya fita daga sashen"Ahyaan nata b'ata fuska ta Ajiye Abinda takeyi ta wuce ciki ta d'akko mayafi ta Aza saman kular kanta ta yane kanta dashi "tunda ta fito sadeeq ke kallonta yana jin inama ya mallaketa Amatsayin matar Aurensa....yana zaune yana danna waya kan resting chairs zaka d'auka bema san da wad'anda ke wucewa ba"Amma sarai yana kallonta ta k'asan Ido ta wuce ta gabansa ta fita.....gaban Ahyaan ya fad'i da taga Mr mahuta tsaye shida Amininsa honorable rabiu "ko wane yayi shiga ta Alfarma"kallo d'aya zaka musu kasan masu dashi ne"yamutsa fuska tayi had'e da yi musu sallama....ikon Allah! sai kace Aljannah"lallai dole mahuta ya gigice A kanta"cewar honorable rabiu Azuciyarsa "sakamakon tunda Ahyaan ta fito yake kallonta"ranki ya dad'e barkanki! Ayangace cike da Aji tana wani shashshan k'amshi tace "sannunku da zuwa"yauwa baby"wani banzan kallo ta jefi honorable rabiu dashi sbd babyn daya kira"Ina yininku?"lafiya qlau yasu mamah?"Alhamdulillah! to Masha Allah" kwana 2 ban koma dawowa ba Ahyaan "naso na hak'ura dake saidai zuciyata ta kasa hak'ura"yanzun haka tafiyar gaggawa ta sameni zuwa k'asar Ghana "zanyi kusan 3 month Acan"so pls inaso ki samun contact naki mu dinga waya"ki kuma Amshi sak'on ki ko?"nasoma mud'an fita dake ko zuwa shopping ne to nasan da wuya ki Amince.....tunda yake surutunsa Ahyaan ke yamutsa fuska cike da masifa sbd ba k'aramin haushi da k'insa tajiba" ka gama bayanin naka?"gaba d'aya suka bita da kallo" ta yamutsa fuska tare da cewa Abu biyu zan rokek'a"idan kak'i zan nuna maka Ainahin kalata"na farko kayi hak'uri ka fita daga rayuwata"na biyu ka cireni daga zuciyarka sbd ba'a yin dole....ke kuwa taya zakiyi haka?"komai sannu Ake binsa fa"yanzun ga wannan yace Abaki....shiru yayi sbd turo k'ofar get d'in da Akayi "ke kije inji mamy"cewar Dr darma daya fito fuska bbu Annuri "ita kanta Ahyaan d'in kasa yi masa musu tayi "saidai batace komai ba ta nufi gefensa ta wuce "Dr darma ya kallesu ya saki wani makirin murmushi had'e da d'allar yatsunsa guda biyu "ya wuce cikin gidan ba tare daya furta komai ba.....Mr mahuta ya sauke numfashi yana sakin murmushi me ciwo babu wani d'ar yace"kota halin k'ak'a saina ja yarinyar nan k'asa"shi kuma wannan k'aramin d'an iskan zai gane ba'a ja dani"Allah yakaimu nadawo daga tafiyar"yanzunma sbd babu lokaci ne shiyasa zan barku.....muje ciki mu Ida mgn"cewar honorable suna shigewa cikin motar da sukazo da ita.....har cikin ranta Ahyaan ta d'auka da gaske mamy ke kiran nata"tana shigowa ta sami sadeeq zaune inda ta barsa yana shan fruit da mamy ta zuba masa."kallo be ishetaba ta wuce cikin parlourn"har bak'on yatafi ne?"Eh"gani broth yace kince nazo"d'an shiru mamy tayi ,sai kuma tace"naga ko ruwa baki d'auka ba da nufin kaima bak'on, shine nace yakiraki "to Ashema ya tafi"uhmm kawai ta Amsa ta wuce d'aki ta cire mayafin..... ************ Ahaka rayuwar taci gaba da wakana"Al'amarin cikin gidan su mamah saidai hak'uri kawai"ummah dai ta rasa taya zata yima Dr darma mgn ya tone Abinda ya binne?"saidai tana ganin yi masa mgn tamkar tayi ihu ta d'auki wuk'a ne ta dab'ama kanta"gaba d'aya Abba yayi mugun yin baya da ita"sai ya zama dole yake tankata"idan kwananta ne bema dawowa gidan tun safe idan yafita sai dare zai dawo"girkinta baya ci,kud'in cefane kullum da safe idan Khadija tazo gaisheshi in har kwanan luban ne zai bata yace ta kai mata"hakan ya koma k'ona ranta"duk mama na lura bata dai shiga Abinda be shafe taba "sai tayi kamar bata ganiba"idan kuma ita ke Aiki normal suke itada Abba "saidai kullum ummah ita y'ar sakin habaici ce,wani zubin su innah Asabe suzo gidan su had'u suyita yadama mama habaici"sai tayi kamar bata san me suke cewa ba"ko kuma ta kunnah wa'azi Abinta ta waya"gefe guda kuma kullum da safe sai mama ta bama Ahyaan rubutunta da ruwan magani me Addu'a"wanda Dr darma ke badawa duk dare a Ajiye da safe Abata "batare data san shine ke yowaba"dukda irin zaman da suke shida ita na rashin kula juna da kin shiga sabgar juna saiya kama"hakan be hanashi yi mata rubutun ba"Alhamdulillah zuwa yanzun kowa yaga canji Atare da Ahyaan "dan har littattafai na soyayya take zama ta d'an karanta"gefen AA mashi Atsarinsa beso yayima mace dole ta soshi"kawai ya fahimci kamar yarinyar bata sonsa ne"shiyasa be tab'a gigin ko sau guda yazo gidan suba"ya bari wata ran k'ilan su koma had'uwa da ita"dukda farar d'aya yaji ya kamu da soyayyar yarinyar Amma bayaso yayima mace tilas ta soshi"shi dama be tab'a soyayyaba "saima Akanta ya fara..... Ab'angaren me gayya me Aiki kam saidai muce Alhamdulillah"sbd Acikin wata biyu ya k'ara canzawa"Albashinsa 700k ne duk wata"ga chemist Alhamdulillah yanata zuba magunguna sbd ana samun k'aruwa sosai"Albashin farko daya Amsa iyayensa mazan ya kamawa yace" duk yadda sukace Ayi haka za'ayi"Abba yaji dad'in hakan sosai"ya yadda ko bayan ran Alh kabeer nurah na masa kallon ubah"sai cewa yayi ya d'auki 500k yak'ara a shagonsa ya zuba magunguna"sauran kud'in yarabama dangi da y'an uwa"ko mama 50k aka bata"tak'i Amsa saida mamy ta nuna fushinta"ko Ahyaan daba mgn yake mataba 20k mamy ta bata injishi"kamar tace bata so, saidai ganin idon mahaifiyarsa ya saka batace ba ta Amsa ta Ajiye kud'in"to Ahaka aka cigaba da tafiya"sadeeq na zaryar zuwa Amma daga gaisuwa Ahyaan bata koma kulashi"jefi jefi maza na yawan Aikowa taje "sai Mamy tayi mata Jan Ido"sannan take fita, saidai ita bataga zab'inta Acikin suba"izzarta da yangarta da Ajinta , had'e da kwalliyarta sai Abinda yayi sama"gefe guda kuma Abba dama daddy nata k'ok'arin ganin An sama mata Aiki"Ahaka har Dr darma yayi wata biyu da fara Aiki harma yashiga cikin na ukku"bbu ruwansa da Ahyaan "suna iya sati basuyi mgn ba"idan kuma ya zama dole suyi maganar da k'yar suke Amsa juna"idan Azumi yakeyi restorent yake shan ruwa"in kuma yana marmarin Abu zai kira mama yace Abu kaza yakeso"idan ta gama yaje yaci koya tura a Amso masa"gaba d'aya girkin Mamy yadena ci sbd yasan Ahyaan ce keyi"daga shi har ita ko wane baya jin dad'in hakan"kafaffiyar zuciyarsa ta hanashi yakoma su cigaba da shiri"tun mu'az be fahimci ya samu matsala da Ahyaan ba harya fahimta, sbd zancen Anko daya masa mgn yasiya mata sbd bikin befi saura 10 days Ayanzun ba "ita kanta Ahyaan d'in bata jin dad'in zaman k'in kula juna da sukeyi"saidai itama zafin kanta ya hanata jansa Ajiki sud'an shirya"ita kodan fad'an da sukeyi tana so suma dawo yi"Ana cikin hakan kyakykyawan labari ya sami Ahyaan Ashekaran jiya da yamma Abba ya dawo da labarin ta sami Aiki Agidan TV "ranar monday zata fara zuwa....tun jiya Friday taje gidan tv d'in, duk wasu tsare tsare da shirye shirye da za'a fara yi wanda ya kama da ita Aciki da kuma lokacin zuwanta da tashinta saida ta gani"saidai lokacin data fito shi kuma AA mashi na kawowa zai wuce"sukayi kallon kallo ita dashi"saiya sakar mata murmushi kawai"Abayanta taji wani na cewa *AA mashi* kayi latti sai mun cika Tara"Atake ta fahimci nan yake Aiki kenan"sai kawai tabar wajen......tun wayewar garin yau satday bayan sun gama break fast take zaman jiran isowar uncle mustapha shida Ammah zasu zo mata tare da sabuwar motarta.dama tace" sai z ata fara Aiki za'a kawo motar"gaba d'aya yau cikin farin ciki take"saidai kuma ta lura da darma tun jiya da safe rabon da ta gansa ya shigo cikin gidan " tana ma zaton kamar be san ta samu Aiki ba"tana wannan tunanin Isma'il ya shigo cikin parlourn yana fad'in Mamy koda Akwai ruwa marar sanyi?"ah ah gaskiya duk suna a fridge"meye zakayi dasu?"yaya nurah ne zaisha magani"baya lafiya ne?"cewar mamy"Eh yanzunma haka magani da Allura na kamasa zai yiwa kansa ,jikinsa ringis da zazzab'i"shine zai sha magani"to kuma khaleel shine zai sha magani beyi kari ba?"wlh kuwa Mamy"Allah ya sawak'a"shiyasa koda dare naga be shigoba da Asuba ma haka be shigo ba"saina d'auka sbd yana week end ne ko baccin gajiyane yakeyi"ah ah gaskiya baya lafiya yana jin jiki ma"Ahyaan tashi maza had'a masa wani abun ki kai masa yad'an ci saiya sha magani"ta fad'a tana kallonta"dato ta Amsa ta mik'e tsaye ta wuce kitchen "khaleel ya kalli mamy yace"bara naje bakin hanya na Amso masa ruwan marar sanyi"daga haka ya fita....cikin mintina goma sha biyar Ahyaan ta dafa masa indomie da taji serdine da Attarugu da Albasa "sai tashin k'amshi takeyi,gata tayita da ruwa ruwa"sai kuma ta juye masa ruwan zafi masu citta da karanfani da Lipton da na'a na'a Acikin flux"indomie d'in kuma saita Aza plate sama ta kife ta fito daga cikin kitchen d'in"mamy na zaune inda ta barta ta kalleta tace sannu da k'ok'ari "murmushi kawai tayi ta Ajiye ta koma bed room,bata jumaba ta fito sanye da rober hijab milk wacce iya karta gwiwar hannunta"ta saka ne sbd doguwar rigar Atamfar jikinta ta kamata sosai"plate da flux d'in ta d'auka gaba d'aya tace mamy bara naje na kai masa"to shikenan saikin dawo.... kwance yake saman lallausan royar bed nasa ya rufe jikinsa da
Chapter 24 · 0% Book details