Sashe 4
Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
babanta ya biyama Maryam suka tafi tare....tun lokacin da Ahyaan da Nura suka fara tasawa Maryam ke nuna tafi jida Ahyaan"itama sai zainab ta janye Nura"har zainab ta k'ara haihuwar Abdul Aziz"Maryam kuma ta haifi khaleel "lokacin dangin Abba (iliyasu)suka taso zainab gaba da nuna mata k'i waita shanyesa komai takeso shi yakeyi,komai yasamu kanta yake k'arewa"yana k'ok'arin fahimtar dasu Amma sun k'i su gane "zainab naji na gani iliyasu ya Auri lubabatu d'iyar k'anwar mahaifiyarsa"ba k'aramin tashi hankalinta yayiba itada Maryam"Amma iliyasu ya kwantar mata da hankali "Ammah kuwa data sami labari tun daga Kaduna tazo har gida tayima iliyasu da Amaryar cin mutunci ta d'auki zainab ta tafi da ita"lokacin zainab nada shigar k'aramin ciki"Aikuwa Ammah taga b'acin ran mijinta irin wanda bata tab'a gani ba"gashi Abban ya kirashi yana masa kuka shifa yana son zainab ,gashi sanadin tahowarta itama maryam tace bazata zaunaba sai kabeer ya sallameta"ga Nura da Ahyaan sunata koke koken ganin basuga maman suba"sosai baba yayi fushi da Ammah "kwanan zainab biyu ta dawo katsina suka cigaba da zamansu"bata shiga harkan Amarya bata kuma yadda ta kamata raini ba"yayin da me gidan kamar ya goyata sbd so, baya son b'acin ranta"hakan kuma ba k'aramin b'acin rai da bak'in ciki yake saka luba shigaba"tama zata yadda takema iliyasun kallon yanada kud'i Awaje Ashe ba haka bane ba"komai nasa harda rufin Asirin matarsa"tana kasuwancinta ga iyayenta na taimaka mata"ko makkan dataje sun zata shine yakaita"dandanan luba ta sakama kanta hassadar zainab"lokacin da zainab ta haifi d'anta na ukku murtala(affan)"lokacin luba nada tsohon ciki na fari"bayan ta haihu ta gama wanka ta fantsama bin bokaye da malamai itada mahaifiyar ta innah salame "saidai koma sunyi Asirin be wani cika yin tasiri ba sbd zainab na tsaye kan ibada kuma iyayenta sun shirya mata jikinta ,hakama Abba"mama yaranta 5 gidan saidai yanzun hud'u ne Araye, Ahyaan, Abdul Aziz,Affan ,sai Autah husnah"Mamy nada yara biyar duk maza ,Nura, Khaleel, Isma'il,Abbas, sai Auta hamza"luba kuma tanada itama guda biyar, mata ukku maza biyu" Mubarak,Khadija ,usman,Fatima sai wacce take goyo yanzun maimoon"ba kuma ta da niyar dena haihuwar, idan son samunta ne tama k'ara biyar tafi mama y'ay'a Agidan shine burunta "wanda idan baka saniba ka shiga gidan zaka d'auka mama ce Amarya, luba (ummah) itace uwar gida"sbd yanayin jiki.... Ahyaan ta taso da wani irin masifaffan kyau"wanda An tabbatar duk layin su babu mace me kyau da aji y'ar kwalisa kamarta "wanda wannan kyawun nata ba k'aramin kona zuciyar ummah yakeba , musammun da ita nata yaron basuda wani kyau na Azo agani"ga zafin yadda mamy ta banbanta Ahyaan da sauran duka yaran dake zaune Agida biyu"wanda be saniba zai d'auka Mamy itace mahaifiyar Ahyaan sbd yadda ta shak'u da ita ta sake da ita kamar mahaifiyarta"dan k'aunar tasu daga baya data juya saima Ahyaan d'in ta koma sashen Mamy kasan cewar batada y'a mace"saidai dukda haka tana d'an zama sashen nasu"takuma koma ne sbd b'eran ta ya tafi London karatun likitah"kasancewar tunda suka fara tasawa suka zama kamar mage da b'era"Nura son girma ita kuma Ahyaan ta rainashi sai tace k'aninta ne shi"dukda sarai sunsan su Age mate ne Amma sai Ahyaan ta basar"sau tari idan suna dambe yasata kuka mamy zata rik'esa tace tazo tarama"haka zaisha kukansa da fushi dasun tafi skul yasameta yadaka"tun suna Abin wasa wasa har suka kai matakin yin SSCE basu dena fad'a da juna ba"dan ma Nura Mamy na tsawatar masa"sai Akayi sa'a yana gama secondary school yasamu scholarship daga gwabnati kasancewarsa givted sai yatafi London karatun likitah"Aranar har fad'a sukayi shida Ahyaan"ta salhesa ta gartse masa d'an yatsa harya fasa.....tun bayan tafiyarsa *Ammah* dake masifar jida Ahyaan ta turo kud'i aka sakata jami'ar ummaru Musa university"wanda dama Ammah taci buri babba akan Ahyaan"musammun da taga yarinyar nada wani irin sihirtaccen kyau "shikenan saita dinga yimata hudubar tsiya kan ta bari saita gama karatu ta sami Aiki" sannan ta samu wani me kud'i ta Aurah"bazata bari yadda mamanta ta kashe rayuwarta ta Auri talaka ba itama ta Auri talaka ba"itadai Ahyaan saidai tayi murmushi sbd bataga talauci Awajen mahaifinta ba"iya bakin gwargwado yanada rufin Asirnsa,i babu rashin ci ko sha ko surutu"har motar hawa garesa"yasiya ma Abdul Aziz mashin shida Nura "ko karatunta danma Ammah taji tagani da shine zai biya mata"Ayanzun haka Mubarak yana Aji biyu FCE"wanda luba taso y'ar Adu'a university aka sakashi Amma Abba yak'i ya yanuna beda halin sakashi"yanzun kuma Khadija na SS3 Tasha Alwa shin kota halin k'ak'a sai An kaita y'ar Addu'a university...tun tasowar Ahyaan masoya sukayi mata caaa"saidai Abin mamaki duk mesonta shine mak'iyinta"zata rufe Ido taci mutumcin mutum"shiyasa wasu badan sunsoba suke ja baya da ita"mama da mamy sunyi fad'an sun gaji"Amma Ammah dake Kaduna goyon bayanta takeyi"da k'ara shagwab'a ta"komai budurwa y'ar gata ke buk'ata sai Ammah da Mamy da daddy(mahaifin Nura) sunyiwa Ahyaan"shiyasa idan ta fita waje zaka d'auka y'ar wani hamshak'in me kud'i ce ita"sbd kyawun jiki da manyan suturu datake sakawa"yanzun haka data gama service nata uncle mustapha k'anin mama yasiya mata mota me tsada zai turo mata da ita data samu Aiki zata dinga hawan Abinta "wannan gatan da Ahyaan ke samu ba k'aramin zafinsa luba da sauran dangin Abba keji ba"dasu kansu y'ay'an luba d'in da itace ta hure musu kunne basu ganin kowa da gashin Arzik'i "wai Abba yana son kai yafi son mama sbd ita y'ar masu kud'i ce umman su kuma y'ar talakawa ce"haka su Mubarak ke fad'a......ummah taso ta had'e kai da mamy su zalinci mama sai mamy tayi mata tas ta nuna ita ba haka take ba"saima k'ara Jan mama tayi suna cigaba da Amincinsu"ummah taso itama Mamy Ayi mata kishiya kodan ta had'e kai da kishiyar"sai kuma Allah yasa ba'a yi mata ba.....Nura tun yanada 15 yrs yayi saukar Alkur'ani me girma"yanada 17 yrs ya haddacesa"lokacin da yake da 20 yrs yasan littattafai na Addini da dama"kuma koda yakoma London be fasa neman ilimi ba"yanada ilimin Addini sosai dukda be cika nunawa ba"yakuma kammala karatunsa na likitanci cikin samun nassara"Wanda takaranci fannin mata"yanzun Aiki ya rage masa"shima kuma takardunsa da komai na gidan gwabnati kira kawai yake jira"tunda yadawo yasami sabon mashin d'in da Abba yasiya masa"daddy kuma yabud'e masa babban chemist"acewar su gara ahada' da kasuwanci"tunda yadawo yaje yaga filinsa daya turo ma mu'az kud'i yasiya masa"bayan yaje ya gani,yafara zaton yanzun ginashi zai farayi"dukda yanaso yayi surprise na iyayen nasu saidai kawai su ganshi ga gidansa "yana jin tausayin su ,yanada burin ya kyautata musu da guminsa kodan sbd su huta suma"yadda ya d'auki daddynsa haka ya d'auki Abba"Mamy ma yadda ya d'auketa haka ya d'auki mama"ummah kuwa iyakarsa da ita gaisuwa tunda yadawo sbd ya fahimci ba mutuniyar kirki bace matar"befi 5 days da dawowa ba mu'az ya rok'esa Alfarma ya dinga koyarwa Ajin matan Aure na islamiyar da mahaifinsa ya bud'e"saiya nuna bazai iyaba"kawai dai zai dinga yin wa'azi duk ranar Wednesday,ya kuma Amsa tambayoyin addini"yayi hakane sbd yayi baya da mata"kuma zata yuyu idan yafara Aiki bazai samu lokaci ba"ko wa'azin ze yine sbd A, Amfana da iliminsa"tunda ya dawo ya saka Aka gyara d'akinsa"Aka saka soma sbd tasu ta lalace"ya kuma canzawa Mamy da mama kujeru saidai banda ummah "ta kuma shak'a sbd har Abba tayima mgn"saidai bece komai ba" kasancewar daya tafi can yana kasuwan cinsa ta online yaturo kaya zuwa nan"tunda ya dawo Nigeria be tambayi Ina Ahyaan ba? babu kuma wanda yamasa zancenta"saidai sarai yasan tana KD can take service nata"ta kuma zauna gidan ka kanninta"sau guda yayi wa'azi sati na farko saida ya gwammace dama beyiba sbd matan da suka dinga kiransa da turo masa tambayoyi"wasu da yawa cewa suke suna sonsa"saidai yaja tsaki"dan shi bema fara soyayya ba"yana dai da friends mata kawai "har turawa da yawa suna nuna suna sonsa koda zasu dinga Aikata Alfasha"duk wacce ta masa irin wannan zancen saita gane kuranta"tun yana can Aka saka ranar bikin mu'az babban Abokinsa wanda shima tare sukayi primary school har zuwa secondry skul "zuwansa London ya rabasu"shi yanzun mu'az Aikin banki yakeyi kuma iyayensa nada kud'i...... wannan kenan Anan gaba zakuji wani abun.. Cigaban labarin....... wannan book d'in na kudine ! Regular grp 500 Vip grp 1000 Special grp 2k wato 3pages in a day zaku biya kud'in ku ta wannan acc number 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251 500 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kira Y'an nijar kutuntub'i wannan n +227 88 01 90 50 Regular 300f Vip 700f Special grp 1500f dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya ba #Mommyn fareesa #Dr Nura Darma #Ahyaan #mr Mahuta #AA mashi #mu'az #Khairiyyah #Ammah #Ummah #ikkhee 7/21/24, 11:01 - Buhainat: