Sashe 10
Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
AGE MATE'S Story & written by mommyn fareesa last free page 9&10 .......Iya k'uluwa Ahyaan ta k'ulu da irin Abinda Dr darma ke mata"ta tabbatar da yadda ya rantse d'in nan muddin bata zoba tofa bazai bata wayar ba"itama Abinda ke cikin wayar shine damuwarta idan ta rasashi"musammun contact na mutane....numfashi ta sauke sbd ba tada mafitar data wuce tabishi d'in"saidai zuciyarta tamkar garwashin wuta take sbd tsabar irin hassalar datayi"taci burin in sha Allah Adaren yau saita k'untata masa shima"kamar zatayi kuka ta mik'e tsaye ta wuce d'aki ta sami mamy zaune tana waya"ward rope ta bud'e ta d'auki sabuwar hijad'inkin jalbab red colour ta saka, ta matsa gaban mirror ta fesa turare.... d'an murmushi ta saki data kalli kanta ta cikin mirror,sbd hijab d'in ya mata kyau sosai"takan jima bata saka hijab ba sai idan sallah zatayi take sakawa kawai "wani time d'in kuma takan saka himar ko k'arama iya gwiwar hannu.....my daughter Ina zuwa haka?"cewar mamy data gama wayar tana kallonta da murmushi saman fuskarta "har cikin ranta take k'aunar Ahyaan tamkar wacce ta Haifa da cikinta"shagwab'e fuska tayi tace "mamy fita zamuyi tare da broth "na d'auka koya sanar miki ma?"eh na tuna ya sanar mun"na kuma ce idan bakyaso bazaki jeba.... Ahyaan na k'ok'arin mgn Abbas ya turo k'ofar d'akin ya shigo yana kallon Ahyaan yace"yaya nurah yace kizo karki bari yazo yasameki"harararsa mamy tayi tace"idan yazo uwar meye zai mata?"kace nace bata zuwa"no mamy barshi bara mu tafi"to shikenan Allah ya tsare kar dai kiyi magrib Awaje "ta fad'a tana kallonta da murmushi saman fuskarta harta fice rik'e da hand bag nata red irin kalar plate shoes d'in k'afarta....cikin takun nan nata dake motsa duk wata halitta dake jikinta kamar tarwad'a haka ta fito wajen get d'in"ta hangosa zaune saman mashin yana duba wristwatch d'insa yanata jan tsaki sai kuma ya hangota.....A karan farko ya saki wani makirin murmushin da aduk sanda yayisa yake tunzura ziciyarta, dan tafi kwallonsa Amatsayin murmushin rainin hankali"sarai tana Ankare da murmushin nasa saita basar Agadarance tayi tsaye gefensa tana yamutsa fuska tace"kana nufin kan mashin zamuje?"karki damu wata ran sannu sannu zamuyi motar " *Amun dago*! ya fad'a yana tada mashin d'in yace"oya ki hau mutafi kina b'ata mana lokaci"nidai wlh kana takurani"to Amma baza kayi gudu ba pls?"tayi maganar cikin muryar shagwab'a ba tare data san tayi ba.....kanafa jina?"Allah saina had'aka da Mamy kana cemun Amun dago!.....Ananne fa sai da tsigar jikin yan maza ta tashi, ya d'an lumshe idanu ya sake bud'ewa yana mai furzar da d'an huci kad'an kafin yace"meyasa bakya jin mgn *Aminatu*? ya fad'a cikin wata iriyar murya har saida ta kallesa ta zabga masa harara sannan ta gyara hijab nata cikin masifa tace" saika mik'e tsaye ko? beyi mgn ba yabita da yadda takeso"bayan ta zauna sannan ya zauna"to sai Abani wayata "tana d'akina na saka miki chargy badan halinki ba"ya fad'a yana jan mashin d'in "gaba d'aya wani iri yakeji sbd wannan ne karon farko da suka tab'a zama irin haka kan mashin.....saurin rirrik'esa tayi ta sunkuyar dakai ta rintse Ido sbd ganin yana sharara gudu" wayyo Mamy nah! na shiga ukku "in kana yiwa Allah ka rage gudun nan"murmushi ya saki Anutse yace"sai kince yaya Nura dan Allah ka rage....be rufe bakiba tace"Allah ya kiyaye nace maka yaya"kuma saina had'aka da mamy"bazan koma hawa wannan mashin d'in naka ba....wani uban gudu daya k'ara shararawa yasaka ta saki k'ara tana k'ara rirrik'esa shi kuma yana murmushi.....Idanunta Arintse saida taji ya tsaya kafin ta bud'e manyan kyawawan idanuwanta.....na bani! ta fad'a tana saurin cikasa"sbd ganin su da tayi cikin get d'in wata islamiyar mata"yara da y'an mata nata kallonsu Anata k'us k'us "ki sakko mana"bazan sauka d'in ba"dama nan zamuzo shine kak'i fad'i?"ta k'are maganar tana koma dafa gefen kafad'arsa ta sauka har hand bag nata yafad'i k'asa"ta tab'e baki ta banko masa harara tana wani shashshan k'amshi"kafe mashin d'in yayi ya duk'a ya d'auki hand bag d'in ya matso kusa da ita Anutse yace" gashi *Aminatu babbar budurwa tana cika wondo da kashi*! ya k'are maganar yana jan karan hancinta tare da sakin sanyayyan murmushi me had'e da dariya"wanda yayi masifar yimasa kyau da d'aukar hankullan masu kallonsu matuk'a"wanda da yawa na zaton matarsa ce"dan tsabar yadda suka dace da juna har wata kama sukaga sunayi musu"musammun da fatar jikinsu ta kasance iri d'aya"Ahyaan kuwa tsabar yadda bak'in cikinsa ya kasheta k'in mgn tayi saidai Ido kawai tak'i kuma Amsar hand bag d'in "ganin idan yabiye mata zasu kwashi y'an kallo kota bashi kunya saiya tamke fuska murya Akausashe yace"last week na fara musu wa'azi duk Wednesday "yanzun ma shine zanyi"zamuje daga can cikin Assembly hall nasu ki zauna inda malamai mata ke zama...dama nace maka Ina buk'atar jin wa'azin d'an yaro sa'ata kamarka?"da kamar k'ilan su *daurawa* kace to zan tsaya saina.....bata rufe bakiba ya finciki hannunta"d'aure fuska tayi tace "wai meyasa baka tsoron zunubi ne?"kaga kana ustazah Amma kana rik'e hannun wata"nika cikani zan bika muje"kinsan Allah ?na cikaki kika gudu ranki sai yafi nawa b'aci "yaron da kika kirani dashi lokaci zai nuna tsakanin nidake waye a sama??yana fad'in hakan yacikata ,sbd shima bason yawan tab'a mata hannu yakeyiba"itace keja sbd gaddamarta....ki Amshi hand bag d'in"ya fad'a suna jerawa suka nufi hall d'in"bazan Amsaba "ta fad'a cikin masifa sbd ba k'aramin haushin shi take jiba"bece komai ba suka shigo cikin hall din yayi sallama"babu d'alibai sosai sai malamai maza guda ukku mata guda biyu"sosai kowa keta kallonsu"wasu na zaton matarsa ce wasu kuma budurwar sa,wasu kuma k'anwarsa"kowa dai da yadda ya d'auka "hannu yabama mazan sukayi musabuha"itadai ko kallo basu ishetaba tama kauda kanta tana wani shan k'amshi.....zo muje ki zaunah"batace komai ba tabishi tana b'ata rai"sai bayan ta zauna kan wani sit da wata malama ke zaune sannan ya aza mata hand d'in saman cinyarta , ya d'an sunkuyo dab da ita murya can k'asa yace "meye ne kike b'ata rai?"fad'uwar gaba taji! Amma saita dake batare data kallesa tace" bakai bane"bece komai ba ya janye ya wuce sbd yaga Anata kallonsu"shi kuwa wajen zamansa ya zauna yana duba wani littafi"tana jin Anata doka bell sai d'alibai keta shigowa suna wucewa"wasu sunsha make up sunata iyayi da zama daga sits na gaba kodan su burgesa...lolx! Ahyaan dai duk tana lura ta tab'e baki Aranta tana fatan Allah yasa ta sami Aiki da wuri gidan TV ko gidan redio"kasancewar Mass come ta karanta"tana so in sha Allah ta dinga wayarma da y'an matanmu kai Akan yadda suke nuna son maza zahiri Aransu ba Aji ko kunyar da Aka san y'a mace da ita.....cak! tunaninta ya tsaya sakamakon sautin sanyayyar muryarsa data karad'e illahirin cikin hole d'in yana mgn"wasu ba sauraren sallamarsa da Addu'ar dayake jerowaba sukeyi ,suna dai kallonsa ne dajin dad'in muryar"wasu na yaba wankansa na yau"shidai besan sunayiba"Anutse ya d'akko maudu'in tsabta! minene ita kanta tsabtar?"ya kuma Akeyinta miye Amfaninta?"yana so mutum guda ya tashi yamasa bayani"kusan budurwa sama da 20 suka d'aga hannuwan su"tsabar takaici kamar Ahyaan takai musu duka haka taji"saidai ta fahimci wasun su Akwai yarinta, da wuya ka samu wacce tayi sama da 20 yrs Acikinsu "wata yarinya dake daga gaba ya nuna"cikin jin dad'i ta mik'e tsaye tana far da Ido ta fara bayani kamar haka"tsabta wani Abu ce da kowane mutum yaka mata yayi"yaka mata kowa ya kula da tsabtace jiki da muhalli..... Alamar ta zauna ya mata"Anutse fuska bbu yabo bbu fallasa yace" waye zayamun cikakken bayani?"Amamakinsa Ahyaan ta d'aga hannu"duk yadda yaso ya dake saida murmushi yasub'uce masa saiya nunata"saida ta zabga masa harara kafin ta mik'e tsaye, Ahankali ta fara da sallama kafin Anutse tace"*menene tsabta?* tsabta wani Abu ce me matuk'ar mahinmanci ga rayuwar d'an Adam! tsabta tana daga cikin Imani"ba tsabtar jiki kawai bace tsabta"Akwai tsabtar zuciya,Akwai ta Abinci data tufafi. Akwai kuma ta muhalli"yanada kyau mutum musulmi ya tsabtace zuciyarsa yayin mu'amalarsa ta yau da kullum tsakaninsa da mutane"sannan mu mata yafi kyau ace mune muka fi kowa tsabta"ita kanta ibadar da mukeyi dole saida tsabta Acikinta"Ayanzun haka Ana yawan samun matsala ga rayuwar wasu matan Aure ko y'an mata da kazanta ke taka rawar gani ga rayuwarsu"Amatsayinki na mace kamilah, muminah Akwai ci baya d'a namiji ya kalleki ya miki korafin tsabta"more especially muma mata"zakiga mace tas Awaje kafin tayi Aure "Amma da zarar tayi Aure shikenan zata koma wata iri , ba gayu ba k'amshi jiki na tsami"Atak'aice tsabta dai itace k'inshik'in rayuwar d'an Adam" kodan sbd kiyaye lafiyar jikin mu....iya nan Dr darma daya tsareta da Ido ta cikin black glass nasa yama ta Alamar ta dakata! yana lura gaba d'aya kowa ita yake kallo, musammun malaman maza"... mlm tasi'u da tunda ya ganta ya tsareta da Ido yana sauraren zazzak'ar muryarta har lumshe Ido yakeyi" ya mik'e tsaye yana fad'in *jamilun jiddan,shukran barikallahu fik'i*! gaba d'aya hall d'in tafi Ake mata"darma ya mata Alamar jinjina da hannu"ta d'auke kanta ta zauna....ustaz Dr Nura Darma ya d'ora daga inda ta tsaya"musammun kan matan da Ayanzun suke k'ok'arin Aure "ya fara nuna illar rashin tsabtar jiki"hakan yasa wasu matan kek'in samun kulawa daga mazajensu"itadai Ahyaan yamutsa fuska tayi Aranta tana gulmar wai Dr Darma beda kunya..... k'arfe 6 pm daidai yayi Addu'a da bada hak'urin rashin tambayoyin dabai Amsaba"bayan An shafa Addu'a mlm tasi'u ya mik'e tsaye yana fad'in Alhamdulillah ! muna godiya da wannan gudun muwa da sabuwar malamanmu ta bada" dukda bamu san sunan malamar ba"hukumar makaranta na mata godiya da karramawa"ga wannan inji hukumar makaranta Abata "Allah yasaka da Alkhairinsa"ya fad'a yana d'ago wani Abu cikin leda bak'a"kafin ya nufi inda Ahyaan ke zaune"ya mutsa fuska tayi sbd lokaci guda taji mutumin na bata haushi, sai wani kallonta yakeyi"saidai kafin ya iso wajenta Dr darma ya tari numfashinsa wajen fad'in ,zaka iya badawa saina bata"ya fad'a fuska bbu walwala "mlm tasi'u na murmushi yace to shikenan"ke malama muna koma gayyatarki zuwa sati na gaba"kanta kawai ta gyad'a masa batayi mgn ba tayi zaune batada niyar tashi"har saida Dr darma ya iso gefenta cike da Isa yace" kina jiran nace kizo ne?"banza ta masa ta mik'e tsaye ta rataye hand bag nata gefen kafad'arta"tana lura wad'anda basu Ida fita daga cikin hall d'in ba sunata kallonsu suna k'us k'us"bata tsaya