← Book details Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 69

Sashe 22

Age Mate's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yace" thanks"yaji haushi saidai be nuna ba"bayan sun gama cin Abincin Atare suka sha ruwan suka fita gaba d'aya sbd lokacin sallar la'asar yayi....Ahyaan kuwa itama sallah tayi ta canza sabon wanka"ta shirya cikin riga da siket na lace pink"sun kamata sosai kayan ,dan sun bayyanah suran jikinta"ta d'akko hijab me hannu tiyebo gogaggiya, ta fesheta da turare ta fito parlourn ta zaunah"mamy ta dubeta da murmushi saman fuskarta sbd ta mata kyau sosai"saidai tausayinta ne fal Aranta sbd yanzun tasan matsalar Ahyaan d'in game da k'in son Aure da nuna k'in mazama gaba d'aya data keyi."y'ar gidan mamy sai Ina kuma?"broth nake jira yazo muje gun wa'azin islamiyar su"ta fad'a tana duba time"4:5 pm"bata rufe bakiba taji k'amshin turarensa da muryarsa yayi sallama"yana sanye da shigar larabawa"farar jallabiya da rawani da b'akin glass"sai takalmi rufaffu bak'ak'e da Agogo bak'a daya d'aura "yayi wani irin masifaffan kyau tamkar bak'in balarabe"karon farko Ahyaan ta kallesa taji fad'uwar gaba "ga wani kyau daya mata wanda yafi na kullum...mamy ga shi khaleel zaizo ki bashi"ya fad'a yana mik'a mata keys d'in shagonsa"yana kuma satar kallon Ahyaan "Anan ya lura da hijab d'in dake saman cinyarta"ko Ina zataje ita kuma?"ya fad'a Azuciyarsa yana juyawa zai tafi"tashi kuje mana"cewar mamy"juyowa yayi fuska Agimtse ya kalleta ta cikin glass d'in yaga ta mik'e tsaye tana warware hijab zata saka"wai Ina zamuje mamy?"kamar ya?"ba wajen wa'azin zakajeba?"eh can zanje "to kuje mana"nifa gaskiya ban tsara zuwa da ita wannan satin ba"haba broth harfa na shirya kuma"sai da ya wani yamutsa fuska kafin yace "Ina ruwana da shiryawar taki?"ba k'aramin shak'a tayiba dama kuma d'azun ma tana hak'e dashi "saita yi shiru fuska bbu walwala ta zauna"rai b'ace mamy ke kallonsa tace"wai nurah meke damun kane?"Ahyaan tashi kuje"idan kun tafi ka yarda ita kan hanya"ta k'are maganar cikin fad'a "k'in mgn yayi ya fita"mamy na hak'ura da zuwan ya barshi kawai tunda baya so yaje dani"ah ah" tashi maza kuje kema Ai zaki samu ladan"bata yi mgn ba sbd bata son musu da ita"jikinta A sanyaye ta mik'e tsaye ta fita "saidai Aranta taci Alwashin ta gama ganin zaije wani waje tace zataje"duk kuwa ranar da yace tazo suje saiya gane kuransa "ko zuwa wa'azin shine Ai last week yaje da ita bama tare da son ranta ba.tana wannan tunanin ta hangosa bakin get ya bud'e mota ya shiga"sosai ta daure fuska Ayangace cike da izzah take tafiyar da takalminta masu tudu ,ta rataye hand bag d'inta saman kafad'a"hijab d'in bata kai har k'asa ba tadai wuce gwiwa.... Azahiri idan ka kalleta zaka d'auka tsananin yawan shekarunta baza su wuce 23 yrs ba"sosai tayi kyau na musammun"Dr darma ya dake kallonta tun d'azun ya sauke numfashi sbd ganin zata shigo"saiya maida kallonsa ga waya"bayan ta shigo ta rufe batare data tankashi ba"shi kuwa so yakeyi ta kulashi Amma ya rasa ta Ina?"sai yaja motar suka d'auki saman titi"saidai fa A zuciyarsa beson zuwa da ita wajen wa'azin sbd kar mlm tasi'u ya ganta"besan kuma meyasa yayi hakan ba?"d'an cije baki yayi daya tuna da sak'onta dake Ajiye cikin motar daga gefen k'afarsa"saiya mik'a hannunsa guda ya zaro ledar ya Ajiye mata saman cinyarta "ita kuwa hankalinta na wajen waya tana chats da Khairiyyah"saidai tana ganin ya Azo mata ledar ta harari ledar dashi kansa daya Ajiye mata"hmmm! huta hararata ba wani abu bane turaren da kikeso ki fesa ne, shine na siyo miki sabo....bana so !ka rik'e Abunka"ba d'azun da nace ka bani ba mgn ka gayan?okay to saiki yadda tunda baki so *Aminatu*! shiru tayi sbd ta rasa meyasa duk idan yakira Ainahin sunanta takejin wani iri?"wai Ina zaka damu?"siyar dake zanyi"hmmm! Ai wlh daka shiga ukku ka siyarwa da mamy y'a" to yanzun zaki gani"wai mlm Ina zamuje?"gidan Hjy (mahaifiyar daddy)"shiru tayi sbd ta d'an kwana 2 batama je gidan ba, Amma da yake sarkin yab'a mgn ce sai cewa tayi dama nan mamy tace muzo?ko kuwa nace maka ka kawoni nan?"ban sani ba"wajen wa'azin ne dai bazaki jeba"in kuma kina so kiyi sabon saurayi Acan sai muje.....kaga ka dena mun irin haka bana so"d'an murmushi yayi bece komai ba "ita kuma ta maida hankalinta wajen waya"saida ya tsaya ta fahimci sun iso"bud'e k'ofar tayi saidai taji ya saka lock"fuska Atsuke ta juyo ta kallesa"kinsan Allah? na dawo na samu kin tafi saina miki Abinda baki tunani"kajima baka yimun ba"ta fad'a tana hararar sa"bece komai ba ya cire lock d'in,ita kuma ta fito tabar ledar nan"ya tab'e baki ya wuce Abinsa..... sai wajen k'arfe 6:7 pm Dr Nura Darma ya dawo d'aukar Ahyaan" "ya soma ya kirata ta fito su wuce ,saidai rashin contact nata da baya dashi Awaya ya saka bisa tilas ya nufi cikin gidan kakar tasu". Ahyaan na zaune ta tak'ark'are tana cin kwad'on zogalen da Hjy tayi mata"yaji k'uli k'uli da kayan had'i"suna zaune tsakar gidan Hjy nata bata labari tana dariya"sosai ta manta da b'acin ran da uban gayyar ya hadda mata"dukda tajima rabonta da gidan Hjy d'in Amma yau taji dad'in zuwan ta gidan"musammun yadda tsohuwar ke nuna mata k'auna da yimata Addu'ar fatan Alkhairi"suna zaune kan tabarma hijab d'inta na daga gefe ta ninke ta,ta Aza hand bag d'inta da wayarta Asama....da kallo ya bisu hannayensa zube cikin Aljihun jallabiyar sa"sau biyu yana sallama Amma basu jiba"Ahyaan ce kawai da taji k'amshin turarensa ta juyo ta hangosa yana doso inda take zaune kai tsaye..... d'an nema na d'auka Ai ba zaka shigo A yanzun ba?"meye ne kika bata ni ban dani Hjy?"ya fad'a yana duk'awa gaban Ahyaan "da sauri ta Aza hannunta saman plate d'in zogalen zata janye"shi kuma yayi saurin rik'ewa cikin nutsatstsiyar muryansa yace kefa matsalata dake marowaciya ce"Hjy kin ganshi zai cimun Abuna ko?kaga nidai ban yi dakai ba, sbd haka saika rungumi na Annabawa"ke kin fara haka Hjy kiyi Abu ki hana mai gida?uhmm! mai gidana yana lahira"kai kuma Allah ya baka mace ta gari"Ameen to tunda ke bakya sona ko?"dariya Ahyaan ta dinga musu ,yayinda shi kuma yake cin zogalen"yana binta da kallon k'asan Ido"can tace" nidai ka barmun Abuna haka mana"yi yayi tamkar be jiba "ganin zai iya cinyewa ya saka itama ta dinga ci"ita dai Hjy tayi shiru tanata kallonsu"saida suka cinye tas ya kalleta,tashi muje mu wanke hannun"batayi mgn ba ta mik'e tsaye ta saka takalminta ta nufi bakin maguji wajen tape"d'an lumshe Ido yayi bayan ta wuce shima ya mik'e tsaye ya iso wajen,saidai tana ganin ya iso ta rufe tape d'in "wlh koki bud'e kona saki kuka"idan ka sani saina barka da Allah "tunda baki iya ramawa ko?"ya fad'a yana bud'e tape d'in ya d'ebi ruwan ya d'ago zai watso mata tayi saurin matsawa tana masa gwalo ta wuce ta d'auki hijab nata ta sanya ta d'auki wayarta da hand bag d'in tace"Hjy na wuce sai Anjima"to shikenan Aminatu ki gaidasu su Hjy zainab d'in "zasuji y'ar tsohuwa"cewar doctor yana yin gaba....tun kafin ta fito ya dinga danna mata horn, ta yamutsa fuska tana fad'in nida sabon shiga"ta k'are maganar tana fitowa daga cikin gdn ta bud'e gefen me zaman banza ta shiga"saidai taga babu ledar daya bata"Ina ledata?"yayi shiru Ak'ule tace "kana fa ji?kefa kikace bakya so?"wai meyasa kake son b'ata mun rai da maido Abinda ya wuce??"shikenan gashi nan"ta Amsa tace na gode tana bud'a ledar"turaruka ne guda biyu"broth shower jal d'infa?"bara muje na siya miki"ya fad'a suna hawan saman titi"shi yana driving ita tana chats"saida suka iso wata had'ad'd'iyar super market sannan ya tsaya yayi parking"ki jira zanje sashen kayan shafa na duba miki saina dawo"be jira cewar taba ya fita dg motar"tana hangosa ta glass d'in motar ya shiga wajen ta kauda kai"saidai befi mintina 2 da shigaba taji Ana mata knocking "ta zuge glass d'in motar Ahankali ta d'an lumshe Ido sbd wani irin k'amshi shigen na Dr darma da taji me sanyi da kashe jiki"Assalamu Alaikum! saida taji gabanta ya fad'i ta d'ago Idanunta Atake suka nutse cikin idanun *Abdallah Aliyu mashi*! matashin saurayi tuzuru d'an gayu"da sauri ta yamutsa fuska ta kauda kanta"saidai Ayadda ta kallesa da irin dressing jikinsa data gani ya tabbatar shid'in gogaggen d'an boko ne! pls madam ki d'an janye motar zan fita da tawa idan ba damuwa ko?"yafad'a yanata kallonta"kin tankashi tayi "ta fito daga cikin motar"ya zuba mata Ido yana kallo"saurayine da zaiyi 35yrs Aduniya bak'i dogo....tana k'ok'arin mishi mgn Dr darma ya iso wajen cike da shan k'amshi yayi kicin kicin da rai"meye kika fito kiyi Anan?"ya fad'a murya Adake "AA mashi ya bishi da kallo bece komai ba, ya d'auka yayenta ne"dama broth yazone sbd mud'an gyara parking ko zai wuce ne"kin mgn yayi ya mik'a mata ledar hannunsa yanufi gefen driver ya bud'e ya shiga"itama saita bud'e zata shiga....ranki ya dad'e babu sallama sai tafiya kuma?"banza ta masa ta shigo"Dr darma yaja wani kakkauran tsaki ya fisgi motar suka bar wajen"da mamaki Ahyaan ta kallesa tana son sanin meyasa yayi tsakin?"saidai ganin yadda ya had'e girar sama data k'asa ya saka yamata wani irin masifar kwarjini saita kasa masa mgn"ga wayoyinsa nata ruri ya musu banza kawai....tunda ta fahimci zafin kansa da izzarsa sun motsa sai itama nata suka motsa tayi biris dashi"suna isowa layinsu yayi parking "kallo be ishetaba ta bud'e k'ofar zata fito"...ita wannan ledar waye kika barmawa ya d'aukar miki?bana so ka rik'e Abinka "in sha Allah na gama cewa ina son wani Abu naka balle kamun yadda kakeso"tana fad'in hakan ta buga k'ofar da k'arfi ta wuce"ba k'aramin hassala shi tayi ba"sai kawai shima ya fito ya bud'e get ya koma ya shigo da motar ya wuce masjeed......tun mamy na zaton Dr darma zai shigo da dare harta cire rai"Ahyaan kuwa ko Ajikinta da k'in shigowar tasa, sbd ba k'aramin k'ullatarsa tayi ba..... ***************** zaune take gaban wani malamin tsubbu cikin wata bukka"kansa Aduk'e ya d'ukufa yana bugun k'asa"yayinda tayi tagumi tana jiran jin Amsar bayanin data kora masa Ayanzun"can ya d'ago kansa yace"wanene likitah ?"da mamaki ummah luba ke saurarensa tayi shiru"sai kuma ta tuna da Dr darma "Atake gabanta yafad'i tace"cikin gidanmu yake ,yaron Abokin Mai gidanane"to shine ya b'ata mana Aiki"sannan ya saka Aka maida Aikin k'aik'ayi koma kan mashek'iya"bi ma'ana Abin ya dawo kanki"kai Amma matsiyacin yaron nan taya yasan meye mukayi?"to gashi nan dai
Chapter 22 · 0% Book details