Sashe 53
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 7 min read
***Sabuwar shadda ce a jikin sa wadda tayi matukar dacewa da fatar sa, kansa babu hula ya ajiye ta a gefen sa, ya dauki turare yana fesawa MD ya turo kofar jikinsa sanye da wando 3quarter da riga armless, ta cikin mirror ya kalle shi ya cigaba da abinda yake yi yana kallon sa yana duba babbar rigar da ke ajiye a saman gadon sa.
"Are you for real!?"
"What?"
"Kai kadai zaka je!? Ba zan raka ka ba?"
"Bana bukata, ni kadai na isa."
"Allah sai naje, bari kaga." Ya haura ta saman gadon ya isa gaban wardrobe dinsa ya ciro sabuwar shaddar sa shima ya hau sakawa, be kula shi ba ya cigaba da shiryawa bakin sa na bitar suratul bagra, agogo ya daura a tsintsiyar hannun sa ya kafa hular yana gyara mata kari, nan da nan MD din ya shirya ya zo ya tsaya kusa dashi yana budawa.
"I'm ready, muje ko?"
"Shuganan yan naci da sa ido." Ya wuurga masa car key din yana ficewa daga dakin, dariya ya saka ya bishi suka jera gwanin sha'awa.
Afwan pls, yau nayi baki ne.
RM
42-43
****Cikin gidan suka nufa kai tsaye maimakon su tafi, MD na gaba yana bin bayansa, babbar rigar ta zauna a jikinsa, yayi kyau ainun sai kamshin turare ke tashi daga jikinsa masu dadi kamshi. Gud'a su Anty Faty suka saki suna shigowa, yayi murmushi yana zama a daya daga cikin kujerun dake falon, su ya su ne yan gidan a falo ya kalli wajen da su Amira suke zaune, daya bayan daya suka zame daga falon sukayi daki cike da tsoron abinda zai biyo baya, tunanin su ko zai fadawa su Anty Faty abinda sukayi, duk sai suka tsure suka kasa zama a dakin da suka koma suna tsoron yadda zata kasance.
"Dauko amaryar tamu za'a tafi ne!? Wannan wanka haka."
"A'ah, zance zan rakashi kinsan ya kyello wata fa, biyu zai hada."
"Banda sharri Mudan, wai haka Abuya?"
"Indirectly yake fad'a muku aure yake so ba wani abu ba."
"Haka nace maka oga?"
" Action speaks louder than voice, action dinka ya nuna."
" Naji, is it a crime? After all ai na girma ko Anty Asy?"
" Ba ruwana a cikin wannan maganar, ni team Abuya ce."
" Duk bakwa sona kenan?"
" Gaskiya, ga latest ango wa zai bi bayan gauro."
"Ni kuma potential ango ba, ku jira IV."
" Kamar gaske, muje karka cinye time Malam."
Yace yana mikewa
" Ina munafukan yaran nan suka shiga?"
" Su Amira wai?"
" Su, ko kafar su na gani a part dina ku shaida sai na kakkarya su na zubar."
" Me sukayi maka?"
" Sunfi kowa sani, muje bari mu dawo Anty Faty."
" Ok Ango, muna nan muna jiranku."
" Wai moctail din ne? Ba za'a hakura ba?"
" Ai har na kira tribes din, sun gyara mana wajen ma, we just eat and snap, nothing more, tunda ka hana mu biki sosai."
" Shikenan, zan fada miki idan mun kusa isowa. "
" Owk sai kunzo, zamu shirya muma kafin nan. "
" Ki fad'a ma su Mom. "
" Owk. " Tace tana mikewa
***Wanka tayi da ruwan turare me kamshi cikin kayan da Amaryar Kb ta aiko mata dasu na tafiya gidan aure, ita kanta tasan ta sauya ta zama wata ta musamman, ga fatar ta da ta zama kamar ta jarirai dan taushi. Kayan da aka turara su da turaren kaya wani material ne me sulbi da akayi masa dinkin doguwar riga fitted, daga kasa ta dan bud'e, ta saka ya kamata sosai daga sama, wuyan sa me v shape hakan ya sake fiddo da kyawun dinkin da kuma zaman da yayi a jikinta das kamar ma material ba. Mayafi madaidaci ta yafa a saman kanta tare da taimakon ya Hadiza ta gama shiryawa, ta kama hannun ta, ta kaita dakin Abba, sannan ta fito ta barsu a ciki yana yi mata nasiha me ratsa jiki, kuka ta samu kanta da yi wiwi, sai ga Abbati ya shigo yace wa Abban Abdallan ya karaso, cewa yayi ya shigo dashi ciki, ya koma yayi masa iso suka shigo a tare, har zuwa dakin Abban wanda shine karon sa na farko na shigowa har ciki sosai haka, zama yayi ya tankwashe kafarsa cike da girmamawa ya gaida Abban kansa a k'asa, amsawa Abban yayi sannan ya cigaba daga in da ya tsaya
"ABDULLAHI kaine shugana, kai Allah ya dora ma nauyin kula da hakkin iyalinka, sannan dole ne sai kayi hakuri da sha'anin mata ka dauke kai a abubuwa masu yawa sannan zaman ku zai yi dadi, ga Asma'u na amana ce a gareka, dan Allah karka ci amanar ta, ka kula min da ita duk da bani da haufi akan tarbiyyar ka, na gamsu da kai dari bisa dari."
"In sha Allah Abba."
"Madallah ke kuma Asma'u, ABDULLAHI mijinki ne, wanda aljannar ki take karkashin kafafunsa, ki bishi kiyi mishi biyayya kamar yadda Allah ya hukunta a gareki, kar naji ko na gani, kiyi koyi da halin mata na gari ki zauna da mijn ki lafiya da yan uwansa, kiyi hakuri ki ji kiki ji, Allah yayi muku albarka, ya baku zaman lafiya ya kade fitina a zamantakewar ku. "
Abdallah kadai ya amsa da Amin a ciki, ita kuma kuka kawai take wanda yake jin kukan har cikin ransa, shi Abban ya fara sallama ya fita ya tsaya a wajen su umma ya gaishe su sannan ya fita waje yana jiran ta, MD na zaune a mota yana danna waya ya fito ya jingina da jikin motar maganganun Abban na dawo masa, lallai aure wani girma ne da Allah ya bawa namiji wanda idan be yi wasa ba tsaf zai iya kaishi wuta, dole ne ya jajirce wajen ganin ya sauke dukkan nauyin da ya rataya a wuyansa ko dan samun rabauta. Kamar me kirga taurarin dake sararin samaniya haka ya daga kansa yana kallon hasken farin watan da yafi kama da dan kwana goma sha biyar saboda hasken sa, iska ya shaka ya fesar dai-dai lokacin da suka fito da ita kanta a lullube da mayafi, da sauri MD ya bud'e musu kofar, ta saka kafarta bakin ta dauke da Bismillah ta shiga, Ya Hadiza ta rankwafo tana fad'a mata wata magana kafin su juya su koma ciki. Bayan ya bud'e ya shiga MD ya juyo bayan yana dariya
"Yanzu shikenan na zama driver ko?"
"Face your front."
" Ai shikenan, Amarya barka da dare, welcome to the family Anty Asmy! "
" Ina wuni? "
" Lafiya lou Anty. "
Murmushi tayi me sauti, ya matso kusa da ita yana leka fuskar ta, har yanzu kunyar nan ta jiya bata bar ta ba, hannu yasa ya janye mayafin da ta rufe fuskarta, tayi saurin sadda kan k'asa ya saka hannu ya dago fuskar tata yana kallon cikin idon ta
"Kunyar ce wai?"
Daga masa kai tayi
"Oh! Toh I'm sorry toh... Bansan me yasa ba, na kasa resisting."
Sai ya dan sosa kansa yayi murmushi, duk maganar da suke MD baya ji dan k'asa k'asa yake maganar sosai ga sautin dake tashi a motar. Shiru ne ya biyo baya sai hannun ta da ya rik'e yana motsa su a cikin nasa, ta lura yana son hakan dan duk sanda suka hadu sai yayi kokarin rik'e mata hannu. Waya taga ya dauka yayi kira, kalma biyu ya fad'a ya ajiye yace
"Mu wuce chan kawai, sun riga sun tafi."
"Ok!" Yace yana juya motar zuwa hanyar tribes din.
Parking yayi ya fita ya bar su a ciki, ya kalli mayafin jikinta ya saka hannu ya gyara mata shi yadda zai sauko sosai, sannan ya cire babbar rigar tasa ya ajiye yace mata
" Ba zamu dade ba, dan sun takura ne ma kawai. "
" Fita zamuyi? " Tace tana kallon sa ta hasken da ya shigo motar
" Eh, ciki zamu shiga, your new family suna ciki suna jiranki. "
Sai ya bud'e murfin motar ya fita ya zagayo wajenta, ya bud'e yana mika mata hannu
" Kunya nake ji. "
" I'm with you, ki saki jikinki kawai kinji?"
" Zasu karbe ni?"
Dan dam yayi yana kallon ta yana hada maganar ta da wani tunani na daban, itama kallon sa take ta kasa motsawa daga zaunen bare ta karbi hannun nasa ta fito,
" Um?" Tace ganin kamar he was lost in thought, murmushi ya sakar mata ya kamo hannun nata ya taimaka mata ta fito, sannan yace
"Duk wanda be karbi Husna tah ba nima ban karbe shi ba, ko waye. So just relax, you are safe! "
"Are you for real!?"
"What?"
"Kai kadai zaka je!? Ba zan raka ka ba?"
"Bana bukata, ni kadai na isa."
"Allah sai naje, bari kaga." Ya haura ta saman gadon ya isa gaban wardrobe dinsa ya ciro sabuwar shaddar sa shima ya hau sakawa, be kula shi ba ya cigaba da shiryawa bakin sa na bitar suratul bagra, agogo ya daura a tsintsiyar hannun sa ya kafa hular yana gyara mata kari, nan da nan MD din ya shirya ya zo ya tsaya kusa dashi yana budawa.
"I'm ready, muje ko?"
"Shuganan yan naci da sa ido." Ya wuurga masa car key din yana ficewa daga dakin, dariya ya saka ya bishi suka jera gwanin sha'awa.
Afwan pls, yau nayi baki ne.
RM
42-43
****Cikin gidan suka nufa kai tsaye maimakon su tafi, MD na gaba yana bin bayansa, babbar rigar ta zauna a jikinsa, yayi kyau ainun sai kamshin turare ke tashi daga jikinsa masu dadi kamshi. Gud'a su Anty Faty suka saki suna shigowa, yayi murmushi yana zama a daya daga cikin kujerun dake falon, su ya su ne yan gidan a falo ya kalli wajen da su Amira suke zaune, daya bayan daya suka zame daga falon sukayi daki cike da tsoron abinda zai biyo baya, tunanin su ko zai fadawa su Anty Faty abinda sukayi, duk sai suka tsure suka kasa zama a dakin da suka koma suna tsoron yadda zata kasance.
"Dauko amaryar tamu za'a tafi ne!? Wannan wanka haka."
"A'ah, zance zan rakashi kinsan ya kyello wata fa, biyu zai hada."
"Banda sharri Mudan, wai haka Abuya?"
"Indirectly yake fad'a muku aure yake so ba wani abu ba."
"Haka nace maka oga?"
" Action speaks louder than voice, action dinka ya nuna."
" Naji, is it a crime? After all ai na girma ko Anty Asy?"
" Ba ruwana a cikin wannan maganar, ni team Abuya ce."
" Duk bakwa sona kenan?"
" Gaskiya, ga latest ango wa zai bi bayan gauro."
"Ni kuma potential ango ba, ku jira IV."
" Kamar gaske, muje karka cinye time Malam."
Yace yana mikewa
" Ina munafukan yaran nan suka shiga?"
" Su Amira wai?"
" Su, ko kafar su na gani a part dina ku shaida sai na kakkarya su na zubar."
" Me sukayi maka?"
" Sunfi kowa sani, muje bari mu dawo Anty Faty."
" Ok Ango, muna nan muna jiranku."
" Wai moctail din ne? Ba za'a hakura ba?"
" Ai har na kira tribes din, sun gyara mana wajen ma, we just eat and snap, nothing more, tunda ka hana mu biki sosai."
" Shikenan, zan fada miki idan mun kusa isowa. "
" Owk sai kunzo, zamu shirya muma kafin nan. "
" Ki fad'a ma su Mom. "
" Owk. " Tace tana mikewa
***Wanka tayi da ruwan turare me kamshi cikin kayan da Amaryar Kb ta aiko mata dasu na tafiya gidan aure, ita kanta tasan ta sauya ta zama wata ta musamman, ga fatar ta da ta zama kamar ta jarirai dan taushi. Kayan da aka turara su da turaren kaya wani material ne me sulbi da akayi masa dinkin doguwar riga fitted, daga kasa ta dan bud'e, ta saka ya kamata sosai daga sama, wuyan sa me v shape hakan ya sake fiddo da kyawun dinkin da kuma zaman da yayi a jikinta das kamar ma material ba. Mayafi madaidaci ta yafa a saman kanta tare da taimakon ya Hadiza ta gama shiryawa, ta kama hannun ta, ta kaita dakin Abba, sannan ta fito ta barsu a ciki yana yi mata nasiha me ratsa jiki, kuka ta samu kanta da yi wiwi, sai ga Abbati ya shigo yace wa Abban Abdallan ya karaso, cewa yayi ya shigo dashi ciki, ya koma yayi masa iso suka shigo a tare, har zuwa dakin Abban wanda shine karon sa na farko na shigowa har ciki sosai haka, zama yayi ya tankwashe kafarsa cike da girmamawa ya gaida Abban kansa a k'asa, amsawa Abban yayi sannan ya cigaba daga in da ya tsaya
"ABDULLAHI kaine shugana, kai Allah ya dora ma nauyin kula da hakkin iyalinka, sannan dole ne sai kayi hakuri da sha'anin mata ka dauke kai a abubuwa masu yawa sannan zaman ku zai yi dadi, ga Asma'u na amana ce a gareka, dan Allah karka ci amanar ta, ka kula min da ita duk da bani da haufi akan tarbiyyar ka, na gamsu da kai dari bisa dari."
"In sha Allah Abba."
"Madallah ke kuma Asma'u, ABDULLAHI mijinki ne, wanda aljannar ki take karkashin kafafunsa, ki bishi kiyi mishi biyayya kamar yadda Allah ya hukunta a gareki, kar naji ko na gani, kiyi koyi da halin mata na gari ki zauna da mijn ki lafiya da yan uwansa, kiyi hakuri ki ji kiki ji, Allah yayi muku albarka, ya baku zaman lafiya ya kade fitina a zamantakewar ku. "
Abdallah kadai ya amsa da Amin a ciki, ita kuma kuka kawai take wanda yake jin kukan har cikin ransa, shi Abban ya fara sallama ya fita ya tsaya a wajen su umma ya gaishe su sannan ya fita waje yana jiran ta, MD na zaune a mota yana danna waya ya fito ya jingina da jikin motar maganganun Abban na dawo masa, lallai aure wani girma ne da Allah ya bawa namiji wanda idan be yi wasa ba tsaf zai iya kaishi wuta, dole ne ya jajirce wajen ganin ya sauke dukkan nauyin da ya rataya a wuyansa ko dan samun rabauta. Kamar me kirga taurarin dake sararin samaniya haka ya daga kansa yana kallon hasken farin watan da yafi kama da dan kwana goma sha biyar saboda hasken sa, iska ya shaka ya fesar dai-dai lokacin da suka fito da ita kanta a lullube da mayafi, da sauri MD ya bud'e musu kofar, ta saka kafarta bakin ta dauke da Bismillah ta shiga, Ya Hadiza ta rankwafo tana fad'a mata wata magana kafin su juya su koma ciki. Bayan ya bud'e ya shiga MD ya juyo bayan yana dariya
"Yanzu shikenan na zama driver ko?"
"Face your front."
" Ai shikenan, Amarya barka da dare, welcome to the family Anty Asmy! "
" Ina wuni? "
" Lafiya lou Anty. "
Murmushi tayi me sauti, ya matso kusa da ita yana leka fuskar ta, har yanzu kunyar nan ta jiya bata bar ta ba, hannu yasa ya janye mayafin da ta rufe fuskarta, tayi saurin sadda kan k'asa ya saka hannu ya dago fuskar tata yana kallon cikin idon ta
"Kunyar ce wai?"
Daga masa kai tayi
"Oh! Toh I'm sorry toh... Bansan me yasa ba, na kasa resisting."
Sai ya dan sosa kansa yayi murmushi, duk maganar da suke MD baya ji dan k'asa k'asa yake maganar sosai ga sautin dake tashi a motar. Shiru ne ya biyo baya sai hannun ta da ya rik'e yana motsa su a cikin nasa, ta lura yana son hakan dan duk sanda suka hadu sai yayi kokarin rik'e mata hannu. Waya taga ya dauka yayi kira, kalma biyu ya fad'a ya ajiye yace
"Mu wuce chan kawai, sun riga sun tafi."
"Ok!" Yace yana juya motar zuwa hanyar tribes din.
Parking yayi ya fita ya bar su a ciki, ya kalli mayafin jikinta ya saka hannu ya gyara mata shi yadda zai sauko sosai, sannan ya cire babbar rigar tasa ya ajiye yace mata
" Ba zamu dade ba, dan sun takura ne ma kawai. "
" Fita zamuyi? " Tace tana kallon sa ta hasken da ya shigo motar
" Eh, ciki zamu shiga, your new family suna ciki suna jiranki. "
Sai ya bud'e murfin motar ya fita ya zagayo wajenta, ya bud'e yana mika mata hannu
" Kunya nake ji. "
" I'm with you, ki saki jikinki kawai kinji?"
" Zasu karbe ni?"
Dan dam yayi yana kallon ta yana hada maganar ta da wani tunani na daban, itama kallon sa take ta kasa motsawa daga zaunen bare ta karbi hannun nasa ta fito,
" Um?" Tace ganin kamar he was lost in thought, murmushi ya sakar mata ya kamo hannun nata ya taimaka mata ta fito, sannan yace
"Duk wanda be karbi Husna tah ba nima ban karbe shi ba, ko waye. So just relax, you are safe! "