Sashe 47
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maimakon ya amsa sai ya tsare ta da ido, tayi murmushi tana rufe masa kofar ta zagayo ta bangaren sa, balle kofar yayi ya fito, ya bud'e bayan ya ciro ledojin ya mika mata biyu ya rike sauran, suka shiga takawa zuwa cikin gidan nasu, a ciki suka hadu da Abbati, ya karbi kayan ya shiga dasu, ya dan yi jim kad'an sannan yayi mata sallama ya juya yana tafiya a hankali. Sai da taga ya tafi sannan ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, ta kutsa kanta cikin gidan nasu tana ayyana kalar kunyar da zata sha musamman idan ta tarar su Rauda basu tafi ba.
*RM*
35
***Da sand'a ta shiga gidan tana addu'ar Allah yasa har ta shige daki umma bata wajen, muryar Rauda ta soma ji tana tambayar Abbati abubuwan da suke cikin ledar, lebewa tayi sai taji Umma tana cewa su daina bud'e mata su bari tazo, kamar ta koma haka taji, ta daure dai ta shiga da sallama ciki ciki, bin ta duk sukayi da kallo, tayi saurin zama daga gefen Rauda ta gaida umman kamar wata bakuwa, dariya ce take cin Rauda amma ta kanne.
"Babu matsala ko!? Abin da Adam yayi masa Ina fatan hakan be zama matsala ba." Umma tace tana mikewa
"Babu komai, ya dai ji babu dadi amma kuma be wani nuna ba."
"Toh masha ALLAH, Adam be kyauta ba, amma dai Abban ku yayi ma tufkar hanci, yace kar ya sake ganin kafarsa har sai kin tafi, idan bakya nan kuwa babu me hanashi zuwa amma yanzu kam kar ya sake ganin sa, ya ma rage kwanakin tarewar yace sati daya sai kawai a siya kayan ko readymade ne, tunda wannan na Hajiya Maman sai da su za'a yi sai ayi miki wasu kawai. "
" Ok. " Kawai tace tana hango yadda Abdallah zai ji idan tace masa an rage kwanakin, tunanin shi ta tafi gaba daya har bata ji sanda Rauda take cewa ta matsu a bude kayan ba, sai data dan taba ta sannan ta wayance tana cewa
" Me kika ce? Bari na shiga ciki. "
" Wai kayan fa zaki bud'e duk na matsu wallahi. "
" Rauda kwadayi." Umma tace tana dariya
" Allah Umma na matsu, nasan kayan kwalam ne, Allah ya taimake ni da na tafi shikenan ba ni za'a kwashi gara. "
" Ki bud'e mana, sai ni dole? Kin jiki. Ni bari kiga ma. " Ta tashi ta shige ciki tana jiyo Rauda da Abbati suna bud'e ledojin suka saki ihun murna.
Jacket dinsa da har lokacin take rik'e da ita ta saki akan gadon ta cire kayan jikinta ta saka wasu riga armless da dogon skirt sai ta dora rigar tasa akai saboda garin da dan sanyi dan ma taga alamar ruwan da akayi a chan yafi yawa sosai.
Rik'e da ledojin Rauda ta biyota da Abbati, suka baje su a tsakiyar dakin, suka ci sukayi nak, Raudan take ce mata anan zata kwana yaje garin su shima achan zai kwana sai da safe zai biyo su wuce, umma ce ta leko tace Abba yana kiran Asma'un, ta tashi zata dauki hijab dinta sai a lokacin Rauda taga jacket din, ta bita da kallo har ta fice kafin ta tashi ta haye gadon.
Dawowar sa kenan Abban ta shiga da sallama, yana tsaye ko zama be ba a tsakiyar falon, zamewa tayi k'asa ta gajshe shi, ya amsa cike da kulawa irin ta da da mahaifi, sannan yace
"Adam bashi da hankali sam, bansan haukan nasa ya kai haka ba, nayi magana da Alhaji Ibrahim dan dama saboda a samu damar shirye-shirye nace musu sati biyu, yace in dai akan abinda za'a zuba ne na kayan daki su ba'a yi musu, miji shi yake zuba komai, dan haka ko yanzu muka ce Abdallah yazo zaizo ya dauki matar sa, toh amma na shawarci mahaifiyar ki gata nan, tace dai dan Allah a barki ko kwana uku ne ko sati, akwai abubuwan da zasu karasa naku na mata, dan haka ni yanzu magana bata hannu na, tana hannun mijinki idan har ya amince shikenan, idan be amince ba, gobe yazo ya dauki matar sa."
Kamar an buge mata kafafu haka taji maganar ta Abba, ta zauna sosai a dakin ta gaza dago kanta, tana jin Abban ya cigaba da kokarin chanja channel din TV, umma kuma ta fita ta sake dawowa tana nan a zaune bata san me zata ce ba, sai da ya zauna sosai sannan yace
" Ki nemi izinin shi idan har ya amince bani da matsala, yadda kukayi dashi sai naji idan Allah ya kaimu, Allah yayi miki albarka ya baku zaman lafiya, ayi hakuri dole baa cin ribar rayuwa sai da hakuri, bani da haufi akanki amma dole sai kin kara hakuri akan wanda kike dashi a dah, Allah yayi miki albarka."
Wani kuka ne ya taso mata, a karo na biyu amma na sake bada ita ga wani tamkar yadda ya faru a farko, sai dai akwai banbancin na farkon da na biyu, kuka ta soma yi ba dan bata son auren ba, sai dan tana jin kamar Abban ya gama mata komai, kamar ita shikenan kuma, tasan zata shiga sabuwar rayuwa ne me banbanci da rayuwar gidan Adam, bata san da wani kalubale zata zo mata ba, amma koma wanne iri ne tana fatan ta samu sassauci a cikin sa.
Tashi tayi bayan tayi ma Abban godiya ta fito, ta samu umma a dakin ta, tana zaune tana jiran fitowar Asma'un, tana shigowa ta ce
" Ki lallabashi ya barki ko satin ne, kinga akwai gyaran da ya kamata ki samu ko? Ki lallabashi dan Allah dan har Yarku ta biya kudi gobe za'ta fara aikinta."
" Umma toh me zance masa?"
" Kice masa dai akwai shirin da baki gama ba."
" Shikenan, zan fada masa."
" Karki kauron baki Asma'u na san halin ki, taimakon ki ne."
" Ba zan ba Umma."
" Yawwa, Allah ya baku zaman lafiya, wai yanzu Abban ku da ya shigo yake cewa Adam na asibiti, kamar wai jininsa ma ya hau a yadda likitoci suka ce."
" Allah ya bashi lafiya."
" Toh Amin."
Tare suka fito da Umman ita tayi dakin Abba ita kuma ta wuce nasu dakin tana sak'a yadda zata tambaye shi dan ta lura zai iya ki musamman yaji cewa Abba ya barshi shi zai yanke hukunci, dakin ta shigo Rauda ta hau waka
"Soyayya dadi, tafi zuma dadi, kinga yadda rigar nan tayi miki kyau?"
Sai lokacin ta tuna da rigar jikinta, ta harari Raudan kunya na kamata
"Yar sa ido, wai me ma yasa ya barki ki kwana ne?"
"Ai dakin umma ma zanje na kwana kar na hanaku more daren."
"Kyaji dashi." Tace tana isa gaban mirror ta dauki wayarta da ke kai ta zauna ta rubuta masa text message ta tura bayan ta goge ta sake rubutawa wajen sau uku, da k'yar ta daure ta tura na karshen, yana shiga ko minti daya baa yi ba, yayi reply
"Ban amince ba, ki shirya gani na."
Saroro tayi rik'e da wayar, ta kalli Rauda ta fara fad'a mata yadda sukayi da Abba, dariya ta saka tace mata
" Ki kirashi Allah, ki marairace masa zai hakura. "
" Zan iya? "
" Sosai ma, kiyi sauri kar yace gashi a waje. "
Tashi tayi da sauri ta koma dakin umma da ba kowa, ta kirashi tana rik'e da kirjinta da yake faman dukan uku uku, sai da ta kusan katsewa sannan ya dauka yana kishingida bayan ya ajiye cup din da yake shan bakin shayi a cikin sa.
" Wife? "
" Umm, dan Allah kayi hakuri kar kazo? "
"Kar nazo? Me yasa? Gani a hanya ma ki shirya kinji? "
" Dan Allah kayi hakuri, na shiga uku. "
" Baki shiga uku ba, kina tare dani wanne shiga uku zaki? "
" Ba zaka zo ba ko? "
" Yanzu kuwa, na ma fito ki shirya ina zuwa sai tafiya, wow I can't wait to have you in my arms, yadda gari yayi dadin nan.... "
Toshe bakin ta tayi da sauri tana ganin tsantsar rashin kunyar sa, magiya ta cigaba da yi masa yana sake biye mata, da gaske ta dauka zuwan zai sai da yace mata wasa yake amma kwana uku kawai, tace dan Allah sati, da k'yar da magiya kamar zata masa kuka ya hakura amma sati daya kawai, ajiyar zuciya ta sauke tayi masa godiya, yace baya son godiya sai dai ta bashi wani abun, shiru tayi tana tunanin me zata bashi, yayi breaking shirun nata ta hanyar cewa
" Sai kin ce I Love you Abdallah sau goma, shine na kara yarda da sati amma idan baki fad'a ba, kwana uku kawai na yarda. "
"Tirkashi. " Ta furta tana rik'e haba,
" Zan kashe, idan kin shirya zan kira dan dai Allah kawai dan an fi karfi na ne, da yanzu zan zo wallahi. "
" Zan fad'a toh."
" Oya, na bud'e zuciya ta, da kunnuwa na. "
" I lo... ve.. ueeew. "
" Ni a hade. "
" I love you." Ta fad'a kamar wdda aka hankada, ta kashe wayar da sauri tana kifa ta, sai kuma ta saki murmushi tana jin wani sabon so da kaunar sa na ratsa ta, so me zafin gaske.
Kyalkyalewa yayi da dariya cike da mamakin ta, kunyar ta tayi masifar yawa, dole sai ya koya mata yadda zata so shi, har ta iya kallon cikin idon sa ta fad'a masa irin son da take masa. Shafa kansa yayi yana bud'e gallery dinsa , ya shiga folder din hotunan da yayi mata dazu, ya dinga zooming dinsu yana karewa dan mitsitin bakin ta da yake tunanin yadda chokali yake shiga kallo. Tunanin moments din dazu ya shiga yi, softness din lips din su suka fi tafiya dashi fiye da komai, ga wani warmness da yake ji duk sanda ya samu close contact da ita.
RM*
36
*RM*
35
***Da sand'a ta shiga gidan tana addu'ar Allah yasa har ta shige daki umma bata wajen, muryar Rauda ta soma ji tana tambayar Abbati abubuwan da suke cikin ledar, lebewa tayi sai taji Umma tana cewa su daina bud'e mata su bari tazo, kamar ta koma haka taji, ta daure dai ta shiga da sallama ciki ciki, bin ta duk sukayi da kallo, tayi saurin zama daga gefen Rauda ta gaida umman kamar wata bakuwa, dariya ce take cin Rauda amma ta kanne.
"Babu matsala ko!? Abin da Adam yayi masa Ina fatan hakan be zama matsala ba." Umma tace tana mikewa
"Babu komai, ya dai ji babu dadi amma kuma be wani nuna ba."
"Toh masha ALLAH, Adam be kyauta ba, amma dai Abban ku yayi ma tufkar hanci, yace kar ya sake ganin kafarsa har sai kin tafi, idan bakya nan kuwa babu me hanashi zuwa amma yanzu kam kar ya sake ganin sa, ya ma rage kwanakin tarewar yace sati daya sai kawai a siya kayan ko readymade ne, tunda wannan na Hajiya Maman sai da su za'a yi sai ayi miki wasu kawai. "
" Ok. " Kawai tace tana hango yadda Abdallah zai ji idan tace masa an rage kwanakin, tunanin shi ta tafi gaba daya har bata ji sanda Rauda take cewa ta matsu a bude kayan ba, sai data dan taba ta sannan ta wayance tana cewa
" Me kika ce? Bari na shiga ciki. "
" Wai kayan fa zaki bud'e duk na matsu wallahi. "
" Rauda kwadayi." Umma tace tana dariya
" Allah Umma na matsu, nasan kayan kwalam ne, Allah ya taimake ni da na tafi shikenan ba ni za'a kwashi gara. "
" Ki bud'e mana, sai ni dole? Kin jiki. Ni bari kiga ma. " Ta tashi ta shige ciki tana jiyo Rauda da Abbati suna bud'e ledojin suka saki ihun murna.
Jacket dinsa da har lokacin take rik'e da ita ta saki akan gadon ta cire kayan jikinta ta saka wasu riga armless da dogon skirt sai ta dora rigar tasa akai saboda garin da dan sanyi dan ma taga alamar ruwan da akayi a chan yafi yawa sosai.
Rik'e da ledojin Rauda ta biyota da Abbati, suka baje su a tsakiyar dakin, suka ci sukayi nak, Raudan take ce mata anan zata kwana yaje garin su shima achan zai kwana sai da safe zai biyo su wuce, umma ce ta leko tace Abba yana kiran Asma'un, ta tashi zata dauki hijab dinta sai a lokacin Rauda taga jacket din, ta bita da kallo har ta fice kafin ta tashi ta haye gadon.
Dawowar sa kenan Abban ta shiga da sallama, yana tsaye ko zama be ba a tsakiyar falon, zamewa tayi k'asa ta gajshe shi, ya amsa cike da kulawa irin ta da da mahaifi, sannan yace
"Adam bashi da hankali sam, bansan haukan nasa ya kai haka ba, nayi magana da Alhaji Ibrahim dan dama saboda a samu damar shirye-shirye nace musu sati biyu, yace in dai akan abinda za'a zuba ne na kayan daki su ba'a yi musu, miji shi yake zuba komai, dan haka ko yanzu muka ce Abdallah yazo zaizo ya dauki matar sa, toh amma na shawarci mahaifiyar ki gata nan, tace dai dan Allah a barki ko kwana uku ne ko sati, akwai abubuwan da zasu karasa naku na mata, dan haka ni yanzu magana bata hannu na, tana hannun mijinki idan har ya amince shikenan, idan be amince ba, gobe yazo ya dauki matar sa."
Kamar an buge mata kafafu haka taji maganar ta Abba, ta zauna sosai a dakin ta gaza dago kanta, tana jin Abban ya cigaba da kokarin chanja channel din TV, umma kuma ta fita ta sake dawowa tana nan a zaune bata san me zata ce ba, sai da ya zauna sosai sannan yace
" Ki nemi izinin shi idan har ya amince bani da matsala, yadda kukayi dashi sai naji idan Allah ya kaimu, Allah yayi miki albarka ya baku zaman lafiya, ayi hakuri dole baa cin ribar rayuwa sai da hakuri, bani da haufi akanki amma dole sai kin kara hakuri akan wanda kike dashi a dah, Allah yayi miki albarka."
Wani kuka ne ya taso mata, a karo na biyu amma na sake bada ita ga wani tamkar yadda ya faru a farko, sai dai akwai banbancin na farkon da na biyu, kuka ta soma yi ba dan bata son auren ba, sai dan tana jin kamar Abban ya gama mata komai, kamar ita shikenan kuma, tasan zata shiga sabuwar rayuwa ne me banbanci da rayuwar gidan Adam, bata san da wani kalubale zata zo mata ba, amma koma wanne iri ne tana fatan ta samu sassauci a cikin sa.
Tashi tayi bayan tayi ma Abban godiya ta fito, ta samu umma a dakin ta, tana zaune tana jiran fitowar Asma'un, tana shigowa ta ce
" Ki lallabashi ya barki ko satin ne, kinga akwai gyaran da ya kamata ki samu ko? Ki lallabashi dan Allah dan har Yarku ta biya kudi gobe za'ta fara aikinta."
" Umma toh me zance masa?"
" Kice masa dai akwai shirin da baki gama ba."
" Shikenan, zan fada masa."
" Karki kauron baki Asma'u na san halin ki, taimakon ki ne."
" Ba zan ba Umma."
" Yawwa, Allah ya baku zaman lafiya, wai yanzu Abban ku da ya shigo yake cewa Adam na asibiti, kamar wai jininsa ma ya hau a yadda likitoci suka ce."
" Allah ya bashi lafiya."
" Toh Amin."
Tare suka fito da Umman ita tayi dakin Abba ita kuma ta wuce nasu dakin tana sak'a yadda zata tambaye shi dan ta lura zai iya ki musamman yaji cewa Abba ya barshi shi zai yanke hukunci, dakin ta shigo Rauda ta hau waka
"Soyayya dadi, tafi zuma dadi, kinga yadda rigar nan tayi miki kyau?"
Sai lokacin ta tuna da rigar jikinta, ta harari Raudan kunya na kamata
"Yar sa ido, wai me ma yasa ya barki ki kwana ne?"
"Ai dakin umma ma zanje na kwana kar na hanaku more daren."
"Kyaji dashi." Tace tana isa gaban mirror ta dauki wayarta da ke kai ta zauna ta rubuta masa text message ta tura bayan ta goge ta sake rubutawa wajen sau uku, da k'yar ta daure ta tura na karshen, yana shiga ko minti daya baa yi ba, yayi reply
"Ban amince ba, ki shirya gani na."
Saroro tayi rik'e da wayar, ta kalli Rauda ta fara fad'a mata yadda sukayi da Abba, dariya ta saka tace mata
" Ki kirashi Allah, ki marairace masa zai hakura. "
" Zan iya? "
" Sosai ma, kiyi sauri kar yace gashi a waje. "
Tashi tayi da sauri ta koma dakin umma da ba kowa, ta kirashi tana rik'e da kirjinta da yake faman dukan uku uku, sai da ta kusan katsewa sannan ya dauka yana kishingida bayan ya ajiye cup din da yake shan bakin shayi a cikin sa.
" Wife? "
" Umm, dan Allah kayi hakuri kar kazo? "
"Kar nazo? Me yasa? Gani a hanya ma ki shirya kinji? "
" Dan Allah kayi hakuri, na shiga uku. "
" Baki shiga uku ba, kina tare dani wanne shiga uku zaki? "
" Ba zaka zo ba ko? "
" Yanzu kuwa, na ma fito ki shirya ina zuwa sai tafiya, wow I can't wait to have you in my arms, yadda gari yayi dadin nan.... "
Toshe bakin ta tayi da sauri tana ganin tsantsar rashin kunyar sa, magiya ta cigaba da yi masa yana sake biye mata, da gaske ta dauka zuwan zai sai da yace mata wasa yake amma kwana uku kawai, tace dan Allah sati, da k'yar da magiya kamar zata masa kuka ya hakura amma sati daya kawai, ajiyar zuciya ta sauke tayi masa godiya, yace baya son godiya sai dai ta bashi wani abun, shiru tayi tana tunanin me zata bashi, yayi breaking shirun nata ta hanyar cewa
" Sai kin ce I Love you Abdallah sau goma, shine na kara yarda da sati amma idan baki fad'a ba, kwana uku kawai na yarda. "
"Tirkashi. " Ta furta tana rik'e haba,
" Zan kashe, idan kin shirya zan kira dan dai Allah kawai dan an fi karfi na ne, da yanzu zan zo wallahi. "
" Zan fad'a toh."
" Oya, na bud'e zuciya ta, da kunnuwa na. "
" I lo... ve.. ueeew. "
" Ni a hade. "
" I love you." Ta fad'a kamar wdda aka hankada, ta kashe wayar da sauri tana kifa ta, sai kuma ta saki murmushi tana jin wani sabon so da kaunar sa na ratsa ta, so me zafin gaske.
Kyalkyalewa yayi da dariya cike da mamakin ta, kunyar ta tayi masifar yawa, dole sai ya koya mata yadda zata so shi, har ta iya kallon cikin idon sa ta fad'a masa irin son da take masa. Shafa kansa yayi yana bud'e gallery dinsa , ya shiga folder din hotunan da yayi mata dazu, ya dinga zooming dinsu yana karewa dan mitsitin bakin ta da yake tunanin yadda chokali yake shiga kallo. Tunanin moments din dazu ya shiga yi, softness din lips din su suka fi tafiya dashi fiye da komai, ga wani warmness da yake ji duk sanda ya samu close contact da ita.
RM*
36