Sashe 16
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsaye tayi tana duban sa baki bud'e, ya ja tsaki ya kwanta yana rufe kansa har sama da abinda aka kawo wa Asma'un saboda rufa, kallon gadon da Asma'un take tayi, taji tausayin ta ya kamata, ta kuma dau alkawarin in dai ta gane iyayenta sai ta sanar musu da su zauna da yar su gaskiya, yanzu take da bukatar kulawa fiye da kowanne lokaci.
Ana idar da sallah Hajiya Mama ta taho asibitin, ta tarar duk suna bacci shi a kujera ita a gado, murnushin jin dadi tayi , ta saka sallaya a gefe itama ta dan kishingida a wajen.
Duk abin nan a tunanin Nadeeya a asibitin Maman ta kwana, shiyasa daga asibitin su tayo nan din wajen bakwai da rabi dan night duty tayi dama da tabbas ita zata zauna da Asma'un.
Zuwan ta ya tashi Adam din, sai a lokacin ya ga Hajiyar ma, ya mike suka gaisa, Nadeeya ta tambaye shi me jiki ya amsa da sauki tamkar wanda ya san halin da take ciki da gaske. Tare suka tafi gida suka bar Hajiyan yaje yayi wanka ya huta. Wajen tara Umma tazo tare da Abbati da breakfast, jiya bata iya bacci ba saboda tunanin halin da Asma'un ke ciki, ta kuma sake rokon Abban akan ya barta amma sai ya nuna fushin sa sosai, sai kawai ta kyale shi duk a tunanin umman ai Hajiya Maman anan ta kwana, a yadda ta sameta ma da yadda ta amsa dubiyar zaka rantse a wajen ta kwana. Babban likita ne yazo, suka shigo tare da nurses ya duba Asma'un da hannun nata, hakan ya farkar da ita, suka gama suka fita daga nan yace ayi masa hoton hannun sannan sai aga me yakamata ayi.
Matsawa Umma tayi gaban gadon tace
"Ya jikin naki?" Maimakon ta amsa sai kawai ta saka kuka.
"Kuka kuma? Menene kuma na kuka eh? Hakuri zakiyi kowanne bawa da kaddarar sa."
"Dan Allah karki tafi umma, ki zauna."
"Ai dama ba yanzu zan tafi ba, sai anjima."
" A'ah, karki tafi gaba daya, bana son ya Adam ya zauna mugu ne, bashi da kirki."
Da sauri umman ta kalli Hajiya Mama da itama umman take kallo a gigice, sam Asma'u bata san Maman na dakin ba tunda a k'asa take daga jikin bango baa gano ta.
"Karki sake cewa mijinki mugu, bana so kar na sake ji." Umma ta fad'a ranta na sosuwa sosai.
Cigaba Asma'un tayi
"Jiya ficewar sa fa yayi ya barni, drip din ya kare babu kowa, so yake na mutu wallahi." Ta karashe tana sake fashewa.
Shiru umman tayi bata ce komai ba, sai zuwa chan tace mata tayi shiru kar ta karawa kanta wani ciwon ko ta sakawa kanta hawan jini wanda bata ma san ko ta riga ta kamu dashi ba.
Kasa hada ido mama tayi da Umma, ita kuma umman tayi kamar bata san me Asma'un ke nufi ba, har zuwa sanda Abba yazo duba Asma'un, tana ganin shi ta sake fashewa da kuka, sosai yaji tausayin yar tasa, ya kuma san tabbas baa kyauta mata ba. Hakuri ya dinga bata da zai tafi Hajiya Mama ta tashi ta bishi waje, umma ta tabe baki tana ayyana yau ko da auren ta zai mutu ba zata bar asibitin nan ba, kawaici da kara daidai gwargado tayi, kuma babu wanda baya son dansa bare ace ta nuna son yaya, ta shiryawa Abba bore duk abinda zai ce ba zai hanata zama ta kula da Asma'un ba.
Dawowa ciki Mama tayi, suka cigaba da zaman kurame har zuwa sanda yan gidan su Asma'un su Rauda suka zo, da kuma kannen Adam din, hakan ya saka wajen sakewa ba kamar dazu da ko uffan babu me cewa wani a cikin su ba, ita Hajiya Mama nauyi da kunya ta hanata katabus, ita kuwa Umma tana sane ta mata banza dan ta lura bata san kawaici ba, shiyasa zata nuna mata ita ma tana da iko akan yayanta da kuma mijinta, ba dole sai abinda taga dama take so shi za'a yi ba, ko da hakan na nufin cutar da yayan ne.
La'asar likis Hajiya Maman tayi musu sallama ta tafi a zuwan sai gobe da safe, umma bata yi mamakin tafiyar ta ba dan kunya take ji sosai musamman da Umman ta gano ba ita ta zauna da Asma'un ba, kuma taga duk take taken Umman na son nuna ikon ta a wannan karon shiyasa ma ta ce Abban ya bar umman ta zauna ta kula da Asma'un ita sai ta dinga zuwa da safe, be yi musu ba tunda dama ita yake karawa amma dama har ga Allah yafi son umman ta zauna sai dai ba zai iya ce mata ta zauna din ba kar Hajiya Maman taga rashin kyautawar sa. Hakan kuwa da akayi sai yaji dadi, ya tafi kasuwa da yakinin daga umman har Asma'un zasu fi jin dadin hakan. Da yamma sai gashi ya sake dawowa ya sake duba jikin nata yaje ya samu likitan yaji duk bayanan da ya kamata ya sani akan hannun nata.
Adam be dawo asibitin ba sai dare, gida yayi tafiyar sa ya kwanta ya huta ya fito da yamma ya je chan majalisar su sannan ya wuce ya siyo nama da lemuna ya wuto asibitin. Babu wanda ya kulashi a cikin su Rauda shima be kula su ba, umma kawai ya gaida sai Ya Hadiza da ta fito daga toilet bayan ya zubar da ruwan da ta goge wa Asma'un jiki dashi. Kadaran kadahan ta amsa ya dan yi tsaye jim sai kuma ya ajiye ledar hannun sa ya fice.
"Adam baya kyautawa sam, na rasa dalilin da yasa ya amince da auren nan idan har baya son Asma'u."
Umma tace cike da takaici
"Hmm, duk wanda yayi na gari ai kansa ko? Ni dai fatana Allah yasa ba shine dalilin karayar nan tata ba, dan idan har aka tabbatar toh babu amfanin zaman su fa."
"Ni kaina abinda nake zargi kenan, dan dai kinga ba zaka fara tambayar yaro yana cikin wannan halin ba, jira nake ya sake samun karfin jikinta sai mu bi baasi, idan har akwai cutar wa babu amfanin auren."
"Gaskiya dai, ya kamata a bincike ta aji."
" Allah ya kyauta. " Umma tace tana mikewa ta fita wajen Abba suyi magana, ta tarar da Abba ya dawo zai shigo dakin, ta hade rai a tunanin ta zai mata maganar tafiya amma sai taji yace
" Yaran nan ya kamata su tafi haka saboda dare, idan kuma mazajen nasu ne zasu zo daukar su toh."
" Eh sune zasu zo. "
" Toh Madallah, ya jikin nata? "
" Da sauki. "
" Allah ya kara sauki, bari na wuce ni, zan shigo da safe saboda ance babban likitan da safe yake zuwa sai kuma yamma wajen biyar. "
" Ok, Allah ya kaimu. Allah ya bamu alkhairi. "
" Amin summa Amin, sai da safe. "
Ya juya ita kuma ta koma ciki, anan take fad'a ma su ya Hadiza yadda sukayi da Abban. Sukayi dariya Rauda har da kwaikwayon yadda Umman ta fita da nufin ita da Abban ko shi ko ita idan yayi mata maganar tafiya. Dariya suka saka gaba daya har Asma'u da take kwance sai data murmusa. Daya bayan daya suka yaye ya zama daga ita sai Umman, ta sake sosai tana jin kamar bata da saurin ciwo, hira umman ta dinga janta tana son gano irin zaman da take a gidan Adam din duk da dama duk sun yi hasashen irin rayuwar da zata tarar din. Kasa fadawa Umman dalilin da ya sakata faduwa tayi, dan da nauyi sosai, tace mata me? sai kawai tace mata zamewa tayi a wajen sauka daga benen bata fadi ainihin abinda ya faru ba, kamar dai Umman bata yarda ba, amma kuma sai ta kyale ta kurum, ta bita da addu'ar samun lafiya.***
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
*RM*
13
***Washegari da wuri Hajiya ta aiko masu aikin ta da abinci, tace zata shigo anjima. Karba umma tayi ta zuba ma Asma'un da tace kadan da k'yar, itama da dan ci sannan ta taimaka mata ta gyara jikin ta kafin likitan yazo, tun bayan fitar Adam be sake dawowa ba, gida ma ya wuce daga nan yana kokarin shigar da motar sa ciki Hajiya Mama ta kirashi tana son ganin sa, fasa shiga yayi ya ajiye motar a waje ya shiga gidan nasu in da ya tarar da ita zaune ita kadai a falo tana sakawa da warwarewa, tana ganin shi ta mike daga kishingidar da tayi, ya zauna kusa da ita daf ya dan matsa mata kafar ta, janye kafar tayi alamun tayi fushi ta tsare shi da ido cikin bacin rai irin wanda be taba gani ba tace
Ana idar da sallah Hajiya Mama ta taho asibitin, ta tarar duk suna bacci shi a kujera ita a gado, murnushin jin dadi tayi , ta saka sallaya a gefe itama ta dan kishingida a wajen.
Duk abin nan a tunanin Nadeeya a asibitin Maman ta kwana, shiyasa daga asibitin su tayo nan din wajen bakwai da rabi dan night duty tayi dama da tabbas ita zata zauna da Asma'un.
Zuwan ta ya tashi Adam din, sai a lokacin ya ga Hajiyar ma, ya mike suka gaisa, Nadeeya ta tambaye shi me jiki ya amsa da sauki tamkar wanda ya san halin da take ciki da gaske. Tare suka tafi gida suka bar Hajiyan yaje yayi wanka ya huta. Wajen tara Umma tazo tare da Abbati da breakfast, jiya bata iya bacci ba saboda tunanin halin da Asma'un ke ciki, ta kuma sake rokon Abban akan ya barta amma sai ya nuna fushin sa sosai, sai kawai ta kyale shi duk a tunanin umman ai Hajiya Maman anan ta kwana, a yadda ta sameta ma da yadda ta amsa dubiyar zaka rantse a wajen ta kwana. Babban likita ne yazo, suka shigo tare da nurses ya duba Asma'un da hannun nata, hakan ya farkar da ita, suka gama suka fita daga nan yace ayi masa hoton hannun sannan sai aga me yakamata ayi.
Matsawa Umma tayi gaban gadon tace
"Ya jikin naki?" Maimakon ta amsa sai kawai ta saka kuka.
"Kuka kuma? Menene kuma na kuka eh? Hakuri zakiyi kowanne bawa da kaddarar sa."
"Dan Allah karki tafi umma, ki zauna."
"Ai dama ba yanzu zan tafi ba, sai anjima."
" A'ah, karki tafi gaba daya, bana son ya Adam ya zauna mugu ne, bashi da kirki."
Da sauri umman ta kalli Hajiya Mama da itama umman take kallo a gigice, sam Asma'u bata san Maman na dakin ba tunda a k'asa take daga jikin bango baa gano ta.
"Karki sake cewa mijinki mugu, bana so kar na sake ji." Umma ta fad'a ranta na sosuwa sosai.
Cigaba Asma'un tayi
"Jiya ficewar sa fa yayi ya barni, drip din ya kare babu kowa, so yake na mutu wallahi." Ta karashe tana sake fashewa.
Shiru umman tayi bata ce komai ba, sai zuwa chan tace mata tayi shiru kar ta karawa kanta wani ciwon ko ta sakawa kanta hawan jini wanda bata ma san ko ta riga ta kamu dashi ba.
Kasa hada ido mama tayi da Umma, ita kuma umman tayi kamar bata san me Asma'un ke nufi ba, har zuwa sanda Abba yazo duba Asma'un, tana ganin shi ta sake fashewa da kuka, sosai yaji tausayin yar tasa, ya kuma san tabbas baa kyauta mata ba. Hakuri ya dinga bata da zai tafi Hajiya Mama ta tashi ta bishi waje, umma ta tabe baki tana ayyana yau ko da auren ta zai mutu ba zata bar asibitin nan ba, kawaici da kara daidai gwargado tayi, kuma babu wanda baya son dansa bare ace ta nuna son yaya, ta shiryawa Abba bore duk abinda zai ce ba zai hanata zama ta kula da Asma'un ba.
Dawowa ciki Mama tayi, suka cigaba da zaman kurame har zuwa sanda yan gidan su Asma'un su Rauda suka zo, da kuma kannen Adam din, hakan ya saka wajen sakewa ba kamar dazu da ko uffan babu me cewa wani a cikin su ba, ita Hajiya Mama nauyi da kunya ta hanata katabus, ita kuwa Umma tana sane ta mata banza dan ta lura bata san kawaici ba, shiyasa zata nuna mata ita ma tana da iko akan yayanta da kuma mijinta, ba dole sai abinda taga dama take so shi za'a yi ba, ko da hakan na nufin cutar da yayan ne.
La'asar likis Hajiya Maman tayi musu sallama ta tafi a zuwan sai gobe da safe, umma bata yi mamakin tafiyar ta ba dan kunya take ji sosai musamman da Umman ta gano ba ita ta zauna da Asma'un ba, kuma taga duk take taken Umman na son nuna ikon ta a wannan karon shiyasa ma ta ce Abban ya bar umman ta zauna ta kula da Asma'un ita sai ta dinga zuwa da safe, be yi musu ba tunda dama ita yake karawa amma dama har ga Allah yafi son umman ta zauna sai dai ba zai iya ce mata ta zauna din ba kar Hajiya Maman taga rashin kyautawar sa. Hakan kuwa da akayi sai yaji dadi, ya tafi kasuwa da yakinin daga umman har Asma'un zasu fi jin dadin hakan. Da yamma sai gashi ya sake dawowa ya sake duba jikin nata yaje ya samu likitan yaji duk bayanan da ya kamata ya sani akan hannun nata.
Adam be dawo asibitin ba sai dare, gida yayi tafiyar sa ya kwanta ya huta ya fito da yamma ya je chan majalisar su sannan ya wuce ya siyo nama da lemuna ya wuto asibitin. Babu wanda ya kulashi a cikin su Rauda shima be kula su ba, umma kawai ya gaida sai Ya Hadiza da ta fito daga toilet bayan ya zubar da ruwan da ta goge wa Asma'un jiki dashi. Kadaran kadahan ta amsa ya dan yi tsaye jim sai kuma ya ajiye ledar hannun sa ya fice.
"Adam baya kyautawa sam, na rasa dalilin da yasa ya amince da auren nan idan har baya son Asma'u."
Umma tace cike da takaici
"Hmm, duk wanda yayi na gari ai kansa ko? Ni dai fatana Allah yasa ba shine dalilin karayar nan tata ba, dan idan har aka tabbatar toh babu amfanin zaman su fa."
"Ni kaina abinda nake zargi kenan, dan dai kinga ba zaka fara tambayar yaro yana cikin wannan halin ba, jira nake ya sake samun karfin jikinta sai mu bi baasi, idan har akwai cutar wa babu amfanin auren."
"Gaskiya dai, ya kamata a bincike ta aji."
" Allah ya kyauta. " Umma tace tana mikewa ta fita wajen Abba suyi magana, ta tarar da Abba ya dawo zai shigo dakin, ta hade rai a tunanin ta zai mata maganar tafiya amma sai taji yace
" Yaran nan ya kamata su tafi haka saboda dare, idan kuma mazajen nasu ne zasu zo daukar su toh."
" Eh sune zasu zo. "
" Toh Madallah, ya jikin nata? "
" Da sauki. "
" Allah ya kara sauki, bari na wuce ni, zan shigo da safe saboda ance babban likitan da safe yake zuwa sai kuma yamma wajen biyar. "
" Ok, Allah ya kaimu. Allah ya bamu alkhairi. "
" Amin summa Amin, sai da safe. "
Ya juya ita kuma ta koma ciki, anan take fad'a ma su ya Hadiza yadda sukayi da Abban. Sukayi dariya Rauda har da kwaikwayon yadda Umman ta fita da nufin ita da Abban ko shi ko ita idan yayi mata maganar tafiya. Dariya suka saka gaba daya har Asma'u da take kwance sai data murmusa. Daya bayan daya suka yaye ya zama daga ita sai Umman, ta sake sosai tana jin kamar bata da saurin ciwo, hira umman ta dinga janta tana son gano irin zaman da take a gidan Adam din duk da dama duk sun yi hasashen irin rayuwar da zata tarar din. Kasa fadawa Umman dalilin da ya sakata faduwa tayi, dan da nauyi sosai, tace mata me? sai kawai tace mata zamewa tayi a wajen sauka daga benen bata fadi ainihin abinda ya faru ba, kamar dai Umman bata yarda ba, amma kuma sai ta kyale ta kurum, ta bita da addu'ar samun lafiya.***
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
*RM*
13
***Washegari da wuri Hajiya ta aiko masu aikin ta da abinci, tace zata shigo anjima. Karba umma tayi ta zuba ma Asma'un da tace kadan da k'yar, itama da dan ci sannan ta taimaka mata ta gyara jikin ta kafin likitan yazo, tun bayan fitar Adam be sake dawowa ba, gida ma ya wuce daga nan yana kokarin shigar da motar sa ciki Hajiya Mama ta kirashi tana son ganin sa, fasa shiga yayi ya ajiye motar a waje ya shiga gidan nasu in da ya tarar da ita zaune ita kadai a falo tana sakawa da warwarewa, tana ganin shi ta mike daga kishingidar da tayi, ya zauna kusa da ita daf ya dan matsa mata kafar ta, janye kafar tayi alamun tayi fushi ta tsare shi da ido cikin bacin rai irin wanda be taba gani ba tace