Sashe 33
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
RM
26
***Matar sa na zaune a falon suka shigo, tun a hanya yayi mata text message saboda haka ta san da zuwan su, ta fara'ar ta, ta tari Asma'un, ta dan saki fuskarta kad'an, suka gaisa sannan tace ta taso , ba musu ta bi bayan ta suka shiga dakinta, ta kawo mata ruwan sha da lemo sai abinci, ruwan kawai tasha ta jingina kanta da drawer din da take zaune a kusa da ita. Sake shigowa matar tayi, tace mata zatayi alwala kasancewar wajen karfe daya lokacin na rana, toilet ta nuna mata sannan ta shinfida mata sallaya kafin ta fito, ta koma wajen su Adam din da suke falo tare da mijinta, ta kwashe kayan abincin da suka ci. Fitowa tayi daga toilet idon ta ya sauka akan karamar wayar dake saman mirror, dauka tayi da dan sauri ta saka number Abba tayi dialing. A dai-dai lokacin Abban tare da Abban su Abeed da Umar da wani abokin Abban suna kokarin tafiya police station sai ga kiran, kallon number da be sani ba Abba yayi, wani tunani ya kawo masa, ya daga da sauri yana kiran sunan ta
"Asma'u?"
"Abba nice."
"Kina ina Asma'u? Fad'a min inda kike yanzu gamu nan."
"Bansan ina ya kawo ni ba, gidan wani abokin sa ne dai, yanzu haka ina dakin matar zanyi sallah."
"Ina adamun?"
"Suna falo."
"Ki kwantar da hankalinki, ki zauna a gidan kinji? Tunda bashi da hankali nasan ta inda zan bullo masa."
"Yawwa, zan kiraki yanzu ki rike wayar."
Kallon su yayi da su ma shi suke kallo jin ya ambaci Asma'u
"Wai wani gidan abokin sa ya kai ta, da sauki ma tunda ba wani wajen daban bane."
"Toh Alhamdulillah, yanzu menene abun yi."
"Ba zamu kai maganar wajen yan sanda ba musamman tunda tana hannu na gari, idan mukayi haka kamar mun daba ma cikin mu wuka ne, bamu san yadda mutane zasu juya labarin ba, sai kaga an juya masa maana kuma dai kaga mace ce gidan wani zata nan gaba. "
" Gaskiya ne." Abokin Abban yace, sai duk suka yi shiru kowa yana saka yadda za'a bullowa al'amarin.
Ajiye wayar tayi ta tada sallah, lokacin matar ta sake shigowa taga tana sallah sai ta juya, ta same su a tsaye zasu fita, dama Adam din ne yace tayi mata magana,
" Sallah take." Tace masa, dan jim yayi kamar yana tunani sai kuma yace
"Dan Allah ki kula da ita, kar tace miki zata wani wajen babu in da ta sani."
" In sha Allah." Fita sukayi ta rufe kofar falon ta koma ciki, ta zauna tana jiran ta idar da sallar, su kuwa dama fitar da sukayi wajen wani malami zai raka shi, zaman da sukayi suka ci abinci ne ya bashi labarin dalilin zuwan su nan din, amma ya boye masa da ainihin abinda ya raba su din, kuma ya nuna masa suna matukar kaunar junan su dashi da ita, shiyasa ma ya yarda zai taimaka masa suje wajen malamin ko Allah zai sa a dace a maida auren nasu kawai, idan yaso sai su koma gidan da auren su.
Murmushi tayi mata ganin ta idar, ta maida mata itama,
"Mijinki ya aiko na kiraki, amma sun fita ba dadewa zasuyi ba."
"Ok." Tace a gajarce,
"Sunana Aisha, kefa."
"Asma'u."
"Lallai, kamar ma baku dade da auren ba ko? Dan kamar nasan lokacin da dear yaje bikin naku."
"Eh... Bamu dadi ba."
"Allah sarki, Allah ya sanya alkhair."
Maimakon ta amsa sai tace
"Garin ku me kyau, na dade ina jin labarin garin wajen wata kawata mijinta dan nan ne, sai yau Allah yayi zanzo."
" Kice baki taba zuwa zariya ba, ah lallai kinyi missing, ba laifi kam garin namu."
" Gaskiya, ita wannan unguwar taku fa, ya sunan ta."
" Anguwar zariya."
" Ok su kamar a limancin kona suke."
"Owk na san unguwar sosai, akwai wasu yan uwan mu a can ina zuwa."
" Lallai."
Tace tana jinjina kai, ta lura gwanar hira ce Ayshan, ta sake da ita sosai kamar sun saba, daurewa take tana tayata hirar tun da ta ji in da take, ganin lokaci na tafiya yace tace
" Kinga na bar wayata a mota, dan Allah bani aron taki."
"Owk ba damuwa, ina na ajiye wayar ne?"
" Itace wannan?" Ta dago mata wadda tayi kiran daxu
" Yawwa eh, yi amfani da wannan din, bari na dubo dayar ko a kitchen na barta."
" Owk."
Text message ta turawa Abba
" Muna zariya, cikin birnin zariyan."
Reply yayi mata da
" Gamu nan. "
Goge komai tayi ta ajiye wayar tana sauke ajiyar zuciya, rashin wankan da batayi ba yafi komai damun ta, gashi bata da kayan da zata chanja da har wanka sai tayi, hijab din dake jikin ta ne kawai ya rufa mata asiri dan dogo ne har ya kusan rufe mata kafarta. Tana zaune suna hira sama-sama har su Adam din suka dawo, basu samu malamin ba sai anjima zasu koma, dan haka sai suka zauna a falo suka cigaba da hirar su, bata fito ba tun da suka zo, gashi yana son ganin ta, ji yake kamar ya shiga dakin yaga halin da take ciki amma dole yayi taka tsantsan dan ba zai yi wasa da wannan damar ba. Be kawo zata karbi waya ta kira ba, dan shi a tunanin sa itama tana son shi kamar yadda yake son ta, shiyasa ma yaga batayi wani abu da zai nuna damuwar ta ba, tun wanda tayi bayan sun dauko hanya, hakan ya kara bashi tabbacin komai zai zo musu da sauki. La'asar sukayi suka sake fita dan shi a son samun sa ma ace yau komai ya tabbata, daga nan ya koma gida su tattara kayan su, su bar garin gaba daya tunda be san da maganar Fido ba. A daidai lokacin su Abba sun riga sun kamo hanya har sun yi nisa ma, dan ba zasu bari sai gobe ba. Umar ya taba rashin mutuncin da zai wa Adam din idan suka isa, dan ya gama gane mahaukaci ne na gaske tunda har zai iya take abinda yazo a addinance saboda shegen son kansa.
***Kasa zama mama tayi a gidan ta tafi gidan Abban, ta tarar da Umman da yaranta, kadaran kadahan kowa yayi mata har Umman da take bata girma sosai amma sai taga akasin haka, zuwan nata ya taimaka mata wajen samun saukin tashin hankalin da take ciki tunda ta samu labarin an san in da Adam din yake, ta dauka da gaske Abban zai kai karar Adam din, bayan tahowar ta Faiza ta rako masu motar kayan furnitures da kayan kitchen, sun samu labarin an daura auren bayan Fido din ta koma, aikuwa suka hau shiri gadan gadam sauran kawayen Fido din da ta yarda dasu suka bi Faizan su zasuyi jere, ita kuma ta nufi salon daga nan zata wuce kunshi, ita a dole amarya, fadar irin farin cikin da take ciki ma bata baki ne, shi gogan bata san ko labarin auren be sani ba, kamar ma ya manta da maganar wata Fido kwata kwata. Babu izinin kowa suka shiga gidan maigadi ya bud'e musu cike da mamakin yanayin su, kasancewar gidan yana nan a sabon shi babu abinda yayi, sukayi jeren su da uban kaya, har yamma suka yi ganin ba zai gamu a ranar ba yasa suka bari su dawo gobe su karasa, Fido bata so ma, dan ma tayi kiran Hajiya da shi kansa Adam din duk bata shiga, hakura tayi goben amma idan har be kira ko yazo ba zata kai kanta ne, su Faiza sun rakata idan yaso ya dawo ya sameta a chan tunda dai aure ya riga ya dauro hatta sadakin ta yana cikin acc din ta.
Sai wajen magriba sannan su Abba suka isa zariyan, ya kira number da Asma'un ta kirashi, ta dan jima tana ringing kafin a daga, wayar na hannun matar abokin Adam din ita kauma Asma'u tana sallah, jin namiji ne ya kira wayar ya sakata katse kiran cike da mamakin waye, ajiye wayar tayi ta karasa abinda take ta fito, ta samu ta idar, wayar ta mika mata ganin kiran na sake shigowa
"Ko number da kika kira ce?"
Da sauri ta karba, ta daga tana mikewa tsaye
"Eh abba, bari na baka tayi maka kwatance."
Sai ta mika mata
"Dan Allah kwantancen gidan nan zaki ma abbanmu."
Karba tayi ta gajshe shi cikin girmamawa sannan tayi masa kwantancen, ta bawa Asma'un yace gasu nan, kasa zama tayi dan bata so Adam ya dawo, Aysha na lura da ita, ta kasa hakuri tace
"Zuwa zai yi?"
"Eh, zuwa zai mu tafi."
"Owk." Tace ba dan ta gamsu ba, ta shiga sake sake a ranta, ta tabbata akwai wani abu dan yanayin Asma'un ya sa ta gane labarin ba yadda Adam din ya fad'a bane, basu dade da wayar ba suka iso kuwa, Umar ne ya kira a wannan karon,yace mata sun karaso
Toh." Tace ta ajiye wayar, sannan tace wa Ayshan
" Suna waje, zasu jira Adam din su dawo, dama so nake su zo sai na fad'a miki gaskiya...Mun rabu da Adam bama tare a yanzu, karya yayi wa mijinki, ba da izini na ko na iyaye na ya taho dani nan ba, bayan kuma babu damar da auren mu zai koma saboda saki uku yayi min,. "
" Wayyo, amma be kyauta ba, wallahi ni Ina ganin ki naji kin kwanta min a rai na, dan Allah ki bani number ki ma dinga gaisawa. "
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
RM
26
***Matar sa na zaune a falon suka shigo, tun a hanya yayi mata text message saboda haka ta san da zuwan su, ta fara'ar ta, ta tari Asma'un, ta dan saki fuskarta kad'an, suka gaisa sannan tace ta taso , ba musu ta bi bayan ta suka shiga dakinta, ta kawo mata ruwan sha da lemo sai abinci, ruwan kawai tasha ta jingina kanta da drawer din da take zaune a kusa da ita. Sake shigowa matar tayi, tace mata zatayi alwala kasancewar wajen karfe daya lokacin na rana, toilet ta nuna mata sannan ta shinfida mata sallaya kafin ta fito, ta koma wajen su Adam din da suke falo tare da mijinta, ta kwashe kayan abincin da suka ci. Fitowa tayi daga toilet idon ta ya sauka akan karamar wayar dake saman mirror, dauka tayi da dan sauri ta saka number Abba tayi dialing. A dai-dai lokacin Abban tare da Abban su Abeed da Umar da wani abokin Abban suna kokarin tafiya police station sai ga kiran, kallon number da be sani ba Abba yayi, wani tunani ya kawo masa, ya daga da sauri yana kiran sunan ta
"Asma'u?"
"Abba nice."
"Kina ina Asma'u? Fad'a min inda kike yanzu gamu nan."
"Bansan ina ya kawo ni ba, gidan wani abokin sa ne dai, yanzu haka ina dakin matar zanyi sallah."
"Ina adamun?"
"Suna falo."
"Ki kwantar da hankalinki, ki zauna a gidan kinji? Tunda bashi da hankali nasan ta inda zan bullo masa."
"Yawwa, zan kiraki yanzu ki rike wayar."
Kallon su yayi da su ma shi suke kallo jin ya ambaci Asma'u
"Wai wani gidan abokin sa ya kai ta, da sauki ma tunda ba wani wajen daban bane."
"Toh Alhamdulillah, yanzu menene abun yi."
"Ba zamu kai maganar wajen yan sanda ba musamman tunda tana hannu na gari, idan mukayi haka kamar mun daba ma cikin mu wuka ne, bamu san yadda mutane zasu juya labarin ba, sai kaga an juya masa maana kuma dai kaga mace ce gidan wani zata nan gaba. "
" Gaskiya ne." Abokin Abban yace, sai duk suka yi shiru kowa yana saka yadda za'a bullowa al'amarin.
Ajiye wayar tayi ta tada sallah, lokacin matar ta sake shigowa taga tana sallah sai ta juya, ta same su a tsaye zasu fita, dama Adam din ne yace tayi mata magana,
" Sallah take." Tace masa, dan jim yayi kamar yana tunani sai kuma yace
"Dan Allah ki kula da ita, kar tace miki zata wani wajen babu in da ta sani."
" In sha Allah." Fita sukayi ta rufe kofar falon ta koma ciki, ta zauna tana jiran ta idar da sallar, su kuwa dama fitar da sukayi wajen wani malami zai raka shi, zaman da sukayi suka ci abinci ne ya bashi labarin dalilin zuwan su nan din, amma ya boye masa da ainihin abinda ya raba su din, kuma ya nuna masa suna matukar kaunar junan su dashi da ita, shiyasa ma ya yarda zai taimaka masa suje wajen malamin ko Allah zai sa a dace a maida auren nasu kawai, idan yaso sai su koma gidan da auren su.
Murmushi tayi mata ganin ta idar, ta maida mata itama,
"Mijinki ya aiko na kiraki, amma sun fita ba dadewa zasuyi ba."
"Ok." Tace a gajarce,
"Sunana Aisha, kefa."
"Asma'u."
"Lallai, kamar ma baku dade da auren ba ko? Dan kamar nasan lokacin da dear yaje bikin naku."
"Eh... Bamu dadi ba."
"Allah sarki, Allah ya sanya alkhair."
Maimakon ta amsa sai tace
"Garin ku me kyau, na dade ina jin labarin garin wajen wata kawata mijinta dan nan ne, sai yau Allah yayi zanzo."
" Kice baki taba zuwa zariya ba, ah lallai kinyi missing, ba laifi kam garin namu."
" Gaskiya, ita wannan unguwar taku fa, ya sunan ta."
" Anguwar zariya."
" Ok su kamar a limancin kona suke."
"Owk na san unguwar sosai, akwai wasu yan uwan mu a can ina zuwa."
" Lallai."
Tace tana jinjina kai, ta lura gwanar hira ce Ayshan, ta sake da ita sosai kamar sun saba, daurewa take tana tayata hirar tun da ta ji in da take, ganin lokaci na tafiya yace tace
" Kinga na bar wayata a mota, dan Allah bani aron taki."
"Owk ba damuwa, ina na ajiye wayar ne?"
" Itace wannan?" Ta dago mata wadda tayi kiran daxu
" Yawwa eh, yi amfani da wannan din, bari na dubo dayar ko a kitchen na barta."
" Owk."
Text message ta turawa Abba
" Muna zariya, cikin birnin zariyan."
Reply yayi mata da
" Gamu nan. "
Goge komai tayi ta ajiye wayar tana sauke ajiyar zuciya, rashin wankan da batayi ba yafi komai damun ta, gashi bata da kayan da zata chanja da har wanka sai tayi, hijab din dake jikin ta ne kawai ya rufa mata asiri dan dogo ne har ya kusan rufe mata kafarta. Tana zaune suna hira sama-sama har su Adam din suka dawo, basu samu malamin ba sai anjima zasu koma, dan haka sai suka zauna a falo suka cigaba da hirar su, bata fito ba tun da suka zo, gashi yana son ganin ta, ji yake kamar ya shiga dakin yaga halin da take ciki amma dole yayi taka tsantsan dan ba zai yi wasa da wannan damar ba. Be kawo zata karbi waya ta kira ba, dan shi a tunanin sa itama tana son shi kamar yadda yake son ta, shiyasa ma yaga batayi wani abu da zai nuna damuwar ta ba, tun wanda tayi bayan sun dauko hanya, hakan ya kara bashi tabbacin komai zai zo musu da sauki. La'asar sukayi suka sake fita dan shi a son samun sa ma ace yau komai ya tabbata, daga nan ya koma gida su tattara kayan su, su bar garin gaba daya tunda be san da maganar Fido ba. A daidai lokacin su Abba sun riga sun kamo hanya har sun yi nisa ma, dan ba zasu bari sai gobe ba. Umar ya taba rashin mutuncin da zai wa Adam din idan suka isa, dan ya gama gane mahaukaci ne na gaske tunda har zai iya take abinda yazo a addinance saboda shegen son kansa.
***Kasa zama mama tayi a gidan ta tafi gidan Abban, ta tarar da Umman da yaranta, kadaran kadahan kowa yayi mata har Umman da take bata girma sosai amma sai taga akasin haka, zuwan nata ya taimaka mata wajen samun saukin tashin hankalin da take ciki tunda ta samu labarin an san in da Adam din yake, ta dauka da gaske Abban zai kai karar Adam din, bayan tahowar ta Faiza ta rako masu motar kayan furnitures da kayan kitchen, sun samu labarin an daura auren bayan Fido din ta koma, aikuwa suka hau shiri gadan gadam sauran kawayen Fido din da ta yarda dasu suka bi Faizan su zasuyi jere, ita kuma ta nufi salon daga nan zata wuce kunshi, ita a dole amarya, fadar irin farin cikin da take ciki ma bata baki ne, shi gogan bata san ko labarin auren be sani ba, kamar ma ya manta da maganar wata Fido kwata kwata. Babu izinin kowa suka shiga gidan maigadi ya bud'e musu cike da mamakin yanayin su, kasancewar gidan yana nan a sabon shi babu abinda yayi, sukayi jeren su da uban kaya, har yamma suka yi ganin ba zai gamu a ranar ba yasa suka bari su dawo gobe su karasa, Fido bata so ma, dan ma tayi kiran Hajiya da shi kansa Adam din duk bata shiga, hakura tayi goben amma idan har be kira ko yazo ba zata kai kanta ne, su Faiza sun rakata idan yaso ya dawo ya sameta a chan tunda dai aure ya riga ya dauro hatta sadakin ta yana cikin acc din ta.
Sai wajen magriba sannan su Abba suka isa zariyan, ya kira number da Asma'un ta kirashi, ta dan jima tana ringing kafin a daga, wayar na hannun matar abokin Adam din ita kauma Asma'u tana sallah, jin namiji ne ya kira wayar ya sakata katse kiran cike da mamakin waye, ajiye wayar tayi ta karasa abinda take ta fito, ta samu ta idar, wayar ta mika mata ganin kiran na sake shigowa
"Ko number da kika kira ce?"
Da sauri ta karba, ta daga tana mikewa tsaye
"Eh abba, bari na baka tayi maka kwatance."
Sai ta mika mata
"Dan Allah kwantancen gidan nan zaki ma abbanmu."
Karba tayi ta gajshe shi cikin girmamawa sannan tayi masa kwantancen, ta bawa Asma'un yace gasu nan, kasa zama tayi dan bata so Adam ya dawo, Aysha na lura da ita, ta kasa hakuri tace
"Zuwa zai yi?"
"Eh, zuwa zai mu tafi."
"Owk." Tace ba dan ta gamsu ba, ta shiga sake sake a ranta, ta tabbata akwai wani abu dan yanayin Asma'un ya sa ta gane labarin ba yadda Adam din ya fad'a bane, basu dade da wayar ba suka iso kuwa, Umar ne ya kira a wannan karon,yace mata sun karaso
Toh." Tace ta ajiye wayar, sannan tace wa Ayshan
" Suna waje, zasu jira Adam din su dawo, dama so nake su zo sai na fad'a miki gaskiya...Mun rabu da Adam bama tare a yanzu, karya yayi wa mijinki, ba da izini na ko na iyaye na ya taho dani nan ba, bayan kuma babu damar da auren mu zai koma saboda saki uku yayi min,. "
" Wayyo, amma be kyauta ba, wallahi ni Ina ganin ki naji kin kwanta min a rai na, dan Allah ki bani number ki ma dinga gaisawa. "