Sashe 29
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin seat room din ya kai shi,ya taimaka masa ya zauna ya zuba masa ruwa ya mika masa, karba yayi ya kafa kai, be ajiye ba sai da ya shanye tas, ya mika masa cup din ya mike, yana kiran sa be amsa ba, ya fice da sauri ya fad'a motar sa, ya tada ita a guje ya bar layin!
Unguwar ya nufa yana jin duk abinda za'a yi sai dai ayi, amma sai ya je, yana isa ya tarar da gate din a rufe yan sandan suna zaune daga gefe, horn ya danne yana daga cikin motar suka kallo shi, tasawo sukayi, ya sauke glass din yana zura kansa
"Wajen wa kazo?"
Kafin ya amsa dayan yace
"Baka gane shi bane? Gayen nan ne da yayi mana rashin kunya ranar har Oga Abdallah yace a kaishi gida."
"Oh na tuna, kai me ya kawo ka nan?"
" Wajen uban gidan naku nazo,idan har ya cika shi din jarumi ne, ya fito ya fuskance ni, ni kadai ba tare da ku ba."
" Gayen nan fa kamar yana da matsalar brain, ku wuce muga iya kar haukan sa."
Barin wajen sukayi suka koma suka zauna, ya dinga horn yana kumfan baki, sukayi masa banza hakan ya sake kona masa rai, ya juya ya bar layin. Allah ne kawai ya kaishi gida lafiya dan mahaukacin gudu ya dinga yi, ko parking din be daidaita ba, ya shiga gidan su, Mama na zaune taga ya fado
"Lafiya Adam? Na shiga uku."
Zube mata yayi cikin wani irin yanayi yace
"Mah Asma'u."
"Me ya same ta?"
"Wani, tare da wani na ganta, Mah zan mutu, wallahi zuciya ta ba zata iya dauka ba."
"Me zan gani? Macen kake wa wannan abun, macen ma Asma'u da kace baka son ta?"
"Karya nake wallahi, I'm a very big liar, ban san me nake aikatawa ba a lokacin. "
" Ka manta babu aure a tsakanin ku toh? "
" Nayi laifi dan Allah mAh karki bari a hukuntani da shirmen da na aikata, a nemi wasu malaman ai ance saki uku a kalma daya, daya ne."
" Saboda irin ku ai masu yin saki ukun na ganganci daga baya ku dawo kuce ba haka ba, aka hana, ka riga ka saki Asma'u saki uku cif ko a kalma daya ko a kalma daban daban ta saku."
Da sauri ya hau rarrafawa zuwa wajen Nadeeya da ta fito daga daki ta bashi amsar nan, ya kama kafarta cikin tashin hankali yace
"Dan Allah sister karki ce haka, sabanin malamai, dan Allah karki haramta min Asma'u wallahi ba zan iya rayuwa babu ita ba."
"Tirkashi, wannan shine abun da na guje maka Adam." Hajiya Mama tace tausayin dan nata na kama ta, janye kafarta Nadeeya tayi tana zama a kujera tace
"Bama tare a wannan lokacin boy, the earlier you realize the better for you, kayi wasa da damar ka Asma'u tayi maka nisa."
"Na shiga uku!"
Yace yana dafe kansa, kallon sa mama take ganin kamar ba adam dinta ba, sai a yanzu taga muguwar ramar da yayi, yayi baki ya wani shiririce, babu tsaftar nan da gayun nan kwata-kwata, girgiza kai kawai ta dinga yi dan al'amarin ya sha kanta yafi karfin ta, bata san ta ina zata bullowa al'amarin ba, shi kadai ya dinga mirgina kansa yana rik'e shi kamar wanda ya samu matsala, suka taso kansa suna tambayar sa me yake ji amma ya kasa magana, wannan wacce iriyar soyayya ce haka ta kama Adam, lallai Allah na azzalumin Sarki bane, duk abinda kayi Yana kallon ka, dole akwai ranar sakayya ko a kusa ko a gaba. Da k'yar Maman ta samu ta lallaba shi ya kwanta a saman kujerar falon, Nadeeya ta samo allurar bacci tayi masa ganin yana ta surutai, kafin allurar ta dauke shi sai da yayi ta nanata sunan Asma'u, har idon sa ya rufe ruf. Tagumi Hajiya Mama ta zabga a gabansa tana kallon sa, ji tayi hawaye na sakkowa a saman fuskarta, ta saka hannu ta share tana komawa dayar kujerar ta zauna abun duniya ya taru yayi mata yawa.
Shirye shiryen biki Fido take yi ita kadai bata damu da Adam din yana so ko baya so ba, ta riga tayi wa kanta alkawarin auren sa ko yana so ko baya so kuwa, duk abun da ya kamata tayi Faiza ce ke tsaya mata, ita ke sakata a hanyar komai, dama da kudin ta, kashe su kawai take tana shiryawa kanta da auren da zatayi, wanda da yawa kawayenta suke mata bakin ciki akai, ita dai ko a jikin ta, burin ta kawai ta shiga gidan Adam din, ta kuma juyashi a tafin hannun ta tamkar yadda ya dade yana gara rayuwar ta tamkar yar gare-gare. Dawowar su kenan daga kasuwa tare da Faiza aka kirata a waya, kafin ta ciro wayar ta katse, ta duba taga Hajiya Mama ce, tayi dariya tana nunawa Faiza
"Mutuniyar ki ce."
"Sirikarki wai?"
"Ita."
"Auw wai har kiranki take kenan."
"Wannan ne na biyu, ta matsu watan nan ya kare ayi bikin nan."
"Lallai Malam Ya'u yasan ta kan tsiya , ya bi da ita wallahi. "
" Bari na kira naji me ya faru kuma? "
" Owk kira muji."
Kira tayi Nadeeya ta daga, lokacin Maman ma kan Adam tana tofa masa addu'a, dan duk farkawa tun da allurar ta soma sakin sa yake surutai, da sumbatu, gashi da kunya ta kira Abban su Asma'u ta fad'a masa, bata san me kuma zatayi ba, gaba daya komai ya tsayaa mata chak,
" Bata kusa zata kira idan ta dawo. " Nadeeya tace ta katse kiran tana jan siririn tsaki,
" Kinga fa da gaske Adam yake fa, yanzu ya zamuyi? "
" Ya zamuyi Mama, ba zai yiwu ba wallahi. "
" Kunyar kiran karami nake, bansan me zan gaya masa ba. "
" Karma ki kirashi Allah, ai da kunya. "
" Shikenan sai na bar Adam a haka, tun yanzu ji yadda ya fara komawa inaga nan gaba. "
"Toh ai duk laifin sa ne ma, shi mutum daraja ce dashi, sanda yake wulakanta ta, be tuna irin wannan ranar ba. "
" Yanzu Nadeeya wannan maganganun naki me zasu sauya? " Bayan aikin gama ya gama ai sai ki goyi bayan shi ko sau daya ne, ba wai kiyi ta nuna kamar ma dadi kikeji da hakan ta faru ba, duk tsiya Adam jinin ki ne."
"Toh Mama na yi shiru."
"Yafi dai, bani wayar na kira Karami."
"Mama?"
"Bani nace, Kanina na ne ba naki ba."
Mika mata tayi
"Kira min shi ki bani, ai naka sai naka, ba zan iya jurar ganin Adam a wannan halin ba, hannun ka baya rubewa ka yanke ka yar, ballantana nasan karami yana kauna ta da duk abinda nake so."
"Gashi an daga." Ta mika mata tana matsawa gefe
"Lafiya lou, ya matar gidan?"
"Alhamdulillah, Adam ne bashi da lafiya wallahi." Sai ta fashe da kuka,
"Dan girman ALLAH ka taimake ni kar na rasa shi, kayi hakuri ka dawo masa da matar sa. "
" Yaya? " Ya katse ta da sauri cikin tsananin mamaki
" Dan Allah ka taimaka min, wallahi yayi nadama sosai ba zai sake ba. "
"Yaya kin manta babu aure tsakanin Adam da Asma'u ne? "
Cikin kuka tace
" Aje wajen malamai, akwai wadanda suke ganin tunda a kalma daya ne, za'a iya komawa. "
" Tirkashi! "
Ya ma rasa bakin magana, magiya ta cigaba da yi masa tana kuka wiwi
" Ka taimaka min dan Allah, ka dubi girman zumunci dan Allah. "
" Zanzo gidan Yaya, wannan maganar ba ta waya ba. " Be jira ta sake magana ba, ya kashe wayar yana murmushi
" Yaya Asabe ce. " Yace wa Umar da yake suna tare
" Wai so take Asma'u ta koma? "
"Eh wai. "
" Allah ya rufa asiri. "
" Toh Amin Babana. "
Har suka zo gida maganar na yawo akan Abba, ya bawa Umma labari tayi dariya kawai, dan bata so tace wani abu ne kawai saboda girman da Hajiya Maman take dashi a wajen Abba, amma da ba haka ba, da anji maganganu manya manya. Missed calls wajen biyar tayi masa, ya daga daga karshe ta cigaba da masa magiyar dan Allah ya daure yazo, yace zaizo zuwa da safe, ba dan taso ba tace toh, amma gani take safiyar tayi mata mugun nisa.
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
*RM*
23
Unguwar ya nufa yana jin duk abinda za'a yi sai dai ayi, amma sai ya je, yana isa ya tarar da gate din a rufe yan sandan suna zaune daga gefe, horn ya danne yana daga cikin motar suka kallo shi, tasawo sukayi, ya sauke glass din yana zura kansa
"Wajen wa kazo?"
Kafin ya amsa dayan yace
"Baka gane shi bane? Gayen nan ne da yayi mana rashin kunya ranar har Oga Abdallah yace a kaishi gida."
"Oh na tuna, kai me ya kawo ka nan?"
" Wajen uban gidan naku nazo,idan har ya cika shi din jarumi ne, ya fito ya fuskance ni, ni kadai ba tare da ku ba."
" Gayen nan fa kamar yana da matsalar brain, ku wuce muga iya kar haukan sa."
Barin wajen sukayi suka koma suka zauna, ya dinga horn yana kumfan baki, sukayi masa banza hakan ya sake kona masa rai, ya juya ya bar layin. Allah ne kawai ya kaishi gida lafiya dan mahaukacin gudu ya dinga yi, ko parking din be daidaita ba, ya shiga gidan su, Mama na zaune taga ya fado
"Lafiya Adam? Na shiga uku."
Zube mata yayi cikin wani irin yanayi yace
"Mah Asma'u."
"Me ya same ta?"
"Wani, tare da wani na ganta, Mah zan mutu, wallahi zuciya ta ba zata iya dauka ba."
"Me zan gani? Macen kake wa wannan abun, macen ma Asma'u da kace baka son ta?"
"Karya nake wallahi, I'm a very big liar, ban san me nake aikatawa ba a lokacin. "
" Ka manta babu aure a tsakanin ku toh? "
" Nayi laifi dan Allah mAh karki bari a hukuntani da shirmen da na aikata, a nemi wasu malaman ai ance saki uku a kalma daya, daya ne."
" Saboda irin ku ai masu yin saki ukun na ganganci daga baya ku dawo kuce ba haka ba, aka hana, ka riga ka saki Asma'u saki uku cif ko a kalma daya ko a kalma daban daban ta saku."
Da sauri ya hau rarrafawa zuwa wajen Nadeeya da ta fito daga daki ta bashi amsar nan, ya kama kafarta cikin tashin hankali yace
"Dan Allah sister karki ce haka, sabanin malamai, dan Allah karki haramta min Asma'u wallahi ba zan iya rayuwa babu ita ba."
"Tirkashi, wannan shine abun da na guje maka Adam." Hajiya Mama tace tausayin dan nata na kama ta, janye kafarta Nadeeya tayi tana zama a kujera tace
"Bama tare a wannan lokacin boy, the earlier you realize the better for you, kayi wasa da damar ka Asma'u tayi maka nisa."
"Na shiga uku!"
Yace yana dafe kansa, kallon sa mama take ganin kamar ba adam dinta ba, sai a yanzu taga muguwar ramar da yayi, yayi baki ya wani shiririce, babu tsaftar nan da gayun nan kwata-kwata, girgiza kai kawai ta dinga yi dan al'amarin ya sha kanta yafi karfin ta, bata san ta ina zata bullowa al'amarin ba, shi kadai ya dinga mirgina kansa yana rik'e shi kamar wanda ya samu matsala, suka taso kansa suna tambayar sa me yake ji amma ya kasa magana, wannan wacce iriyar soyayya ce haka ta kama Adam, lallai Allah na azzalumin Sarki bane, duk abinda kayi Yana kallon ka, dole akwai ranar sakayya ko a kusa ko a gaba. Da k'yar Maman ta samu ta lallaba shi ya kwanta a saman kujerar falon, Nadeeya ta samo allurar bacci tayi masa ganin yana ta surutai, kafin allurar ta dauke shi sai da yayi ta nanata sunan Asma'u, har idon sa ya rufe ruf. Tagumi Hajiya Mama ta zabga a gabansa tana kallon sa, ji tayi hawaye na sakkowa a saman fuskarta, ta saka hannu ta share tana komawa dayar kujerar ta zauna abun duniya ya taru yayi mata yawa.
Shirye shiryen biki Fido take yi ita kadai bata damu da Adam din yana so ko baya so ba, ta riga tayi wa kanta alkawarin auren sa ko yana so ko baya so kuwa, duk abun da ya kamata tayi Faiza ce ke tsaya mata, ita ke sakata a hanyar komai, dama da kudin ta, kashe su kawai take tana shiryawa kanta da auren da zatayi, wanda da yawa kawayenta suke mata bakin ciki akai, ita dai ko a jikin ta, burin ta kawai ta shiga gidan Adam din, ta kuma juyashi a tafin hannun ta tamkar yadda ya dade yana gara rayuwar ta tamkar yar gare-gare. Dawowar su kenan daga kasuwa tare da Faiza aka kirata a waya, kafin ta ciro wayar ta katse, ta duba taga Hajiya Mama ce, tayi dariya tana nunawa Faiza
"Mutuniyar ki ce."
"Sirikarki wai?"
"Ita."
"Auw wai har kiranki take kenan."
"Wannan ne na biyu, ta matsu watan nan ya kare ayi bikin nan."
"Lallai Malam Ya'u yasan ta kan tsiya , ya bi da ita wallahi. "
" Bari na kira naji me ya faru kuma? "
" Owk kira muji."
Kira tayi Nadeeya ta daga, lokacin Maman ma kan Adam tana tofa masa addu'a, dan duk farkawa tun da allurar ta soma sakin sa yake surutai, da sumbatu, gashi da kunya ta kira Abban su Asma'u ta fad'a masa, bata san me kuma zatayi ba, gaba daya komai ya tsayaa mata chak,
" Bata kusa zata kira idan ta dawo. " Nadeeya tace ta katse kiran tana jan siririn tsaki,
" Kinga fa da gaske Adam yake fa, yanzu ya zamuyi? "
" Ya zamuyi Mama, ba zai yiwu ba wallahi. "
" Kunyar kiran karami nake, bansan me zan gaya masa ba. "
" Karma ki kirashi Allah, ai da kunya. "
" Shikenan sai na bar Adam a haka, tun yanzu ji yadda ya fara komawa inaga nan gaba. "
"Toh ai duk laifin sa ne ma, shi mutum daraja ce dashi, sanda yake wulakanta ta, be tuna irin wannan ranar ba. "
" Yanzu Nadeeya wannan maganganun naki me zasu sauya? " Bayan aikin gama ya gama ai sai ki goyi bayan shi ko sau daya ne, ba wai kiyi ta nuna kamar ma dadi kikeji da hakan ta faru ba, duk tsiya Adam jinin ki ne."
"Toh Mama na yi shiru."
"Yafi dai, bani wayar na kira Karami."
"Mama?"
"Bani nace, Kanina na ne ba naki ba."
Mika mata tayi
"Kira min shi ki bani, ai naka sai naka, ba zan iya jurar ganin Adam a wannan halin ba, hannun ka baya rubewa ka yanke ka yar, ballantana nasan karami yana kauna ta da duk abinda nake so."
"Gashi an daga." Ta mika mata tana matsawa gefe
"Lafiya lou, ya matar gidan?"
"Alhamdulillah, Adam ne bashi da lafiya wallahi." Sai ta fashe da kuka,
"Dan girman ALLAH ka taimake ni kar na rasa shi, kayi hakuri ka dawo masa da matar sa. "
" Yaya? " Ya katse ta da sauri cikin tsananin mamaki
" Dan Allah ka taimaka min, wallahi yayi nadama sosai ba zai sake ba. "
"Yaya kin manta babu aure tsakanin Adam da Asma'u ne? "
Cikin kuka tace
" Aje wajen malamai, akwai wadanda suke ganin tunda a kalma daya ne, za'a iya komawa. "
" Tirkashi! "
Ya ma rasa bakin magana, magiya ta cigaba da yi masa tana kuka wiwi
" Ka taimaka min dan Allah, ka dubi girman zumunci dan Allah. "
" Zanzo gidan Yaya, wannan maganar ba ta waya ba. " Be jira ta sake magana ba, ya kashe wayar yana murmushi
" Yaya Asabe ce. " Yace wa Umar da yake suna tare
" Wai so take Asma'u ta koma? "
"Eh wai. "
" Allah ya rufa asiri. "
" Toh Amin Babana. "
Har suka zo gida maganar na yawo akan Abba, ya bawa Umma labari tayi dariya kawai, dan bata so tace wani abu ne kawai saboda girman da Hajiya Maman take dashi a wajen Abba, amma da ba haka ba, da anji maganganu manya manya. Missed calls wajen biyar tayi masa, ya daga daga karshe ta cigaba da masa magiyar dan Allah ya daure yazo, yace zaizo zuwa da safe, ba dan taso ba tace toh, amma gani take safiyar tayi mata mugun nisa.
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
*RM*
23