Sashe 45
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
***Siyayyar kayan ciye-ciye ya tsaya yayi, tare da fresh fruits masu yawan gaske sannan ya tura mata message din gashi nan, suna zaune suna maganar me gyaran jikin da Ya Hadiza zata kira wata neighbor dinta Amaryar Kb da tayi bala'in iya gyaran amarya har ma da uwargida, abubuwan da take siyarwa maganin mata na matsi dana ni'ima, turaren wuta, Khumra turaren wankan, vip humra, oils perfume sannan tana gyaran jiki na amare. Bangaren turaren wuta tana saida irinsu Sandal flakes , Kajiji ,Yellow sandal Mufaddal.Senegalese Kajiji Couscous.
Green sandal,Sudanese mix,Shek Bakhur, Sandal coconut.
Dorot , Hadut, Gabgab,Kajiji balls.
Aroosa da sauran su. Ga kuma maganin infection sadidan, su tsumi, zumar chad da sauran kayan gyara na kankaro mutunci, ga hadaddun khumra masu masifar kamshi da kama jiki, turaren wanka da na gashi, ga kuma na carpet da na curtains musamman a yanayin damunar nan. Amaryar kb Global Enterprise dai ta hada komai na gyara da kankaro mutunci 08067558902 shiyasa ma Ya Hadiza taga ya kamata ta kirata, suyi magana ta gyara Asma'un ciki da waje, ana cikin maganar ne sakon sa ya shigo, shine ta zame ta shige daki ta fad'a toilet tayi wanka a gurguje ta fito ta shafa daya daga cikin khumran da Ya Hadiza ta taho mata dashi na cikin kayan da Amaryar Kb take saidawa ta shafa ta dan shafa powder da wetlips, ta sake bin jikinta ta feshe shi da wasu kalolin turarurrukan masu sanyin kashi sannan ta zauna tana tunanin yadda zatayi ta fita idan yace mata yazo, Hidaya ce ta biyota ciki, ta ganta a shirye tsaf tana danna wayar ta, basarwa tayi kamar bata ga shigowar Hidayan ba, juyawa tayi ta tseguntawa su Yaya Hadiza, suka yi dariya har Umma da dadi ya lullube ta, fitar hidayan da kad'an zai ga kiran sa, ta daga gabanta na faduwa yace yana waje, a kasalance tace toh ta tashi ta shiga zagaye a dakin ta rasa ta ina zata fita, kunyar su take ji tana jiyo hirar su a tsakar gidan, kuru tayi ta daure ta fito rik'e da flat shoe dinta a hannu, taki yarda su hada ido da kowa tace
"Umma shine yazo."
"Allah ya kiyaye, ki gaishe shi."
Har tayi gaba Ya Hadiza tace bari ta tsokaneta
"Cewa zakiyi Umma angon yazo."
Dariya suka kwashe da, ta daga kafarta da sauri ta fice taji umma na cewa ya Hadiza ya kyale mata yarta.
Bayan sa ta hanga ya juya shi yana facing din kofar shigowa, dogo ne me cike da haiba, ba shi da rama sannan ba shi da kiba jikinsa dai-dai ya dace da yanayin sa, riga da wandon yadi ne a jikin sa ash colour dinkin rigar daga dan ya wuce guiwar sa, kansa babu hula sai takalmin kafarsa sau ciki, duk a dan dakikun da basu gaza goma ba ta gama tantance shi, takun ta yaji ya juyo da sauri yana rik'e da car key dinsa da babbar wayar sa a hannu, murmushi ya sakar mata ita ma ta maida masa tana russunar da kanta ganin ya kafe ta da kallon sa wanda yake kashe mata jiki, a gefen sa ta tsaya ta gaishe shi, maimakon ya amsa sai ya mika mata hannu alamun su gaisa, a kunyace ta mika masa ya kama hannun ya rik'e yana dan motsa shi acikin nasa hannu.
"Kinyi kyau sosai." Ya fad'a yana kallon lips dinta da suke shekin lips balms, kauda kai tayi cike da jin kunyar sa, har lokacin be saki hannun ta ba, kamar ma hakan na sashi nishadi, ciki tace ya shigo ya noke kafada
"Ban gama kallon ki ba, nan yafi haske na more kallon matata."
"Kai..."
"Emana."
"Dallah malam cika mata hannu! "
Ya buga tsawa idonsa na kankancewa cikin tsakanin tashin hankalin ganin hannun Asma'un cikin na Abdallah, tahowa yayi gadan gadan, wani banzan kallo Abdallan yayi masa ya saka hannu ya matso da Asma'un jikinsa sosai sannan yace
" Don't you dare, karka kuskura ka karaso kusa da matata."
" Matar ka? Yaushe ta zama matar ka?"
" Kaje ka tambaya kaji, kuma wallahi ko kusa da ita na ganka wallahi sai na daure ka kaji na rantse, shashasha kawai. "
A karkace Umar yayi parking suka fito shida Abbati a dari suka fado gidan ganin motar Abdallan data Adam a kofar gidan, suna zuwa suka damke Adam din daya fara hauka yana kokarin jan Asma'un, hannun ta cikin nasa ya shiga takawa da ita, ya nufi gate din gidan ya fita da ita, Adam ya birkice ya dinga kwala mata kira su Abbati suka rik'e shi gam, gaban motar ya bud'e mata ya sakata, sannan ya dawo ya shiga ya tada motar suka bar layin, ransa ya kai kololuwa a baci amma calmness dinsa na tare dashi, satar kallon sa take, driving kawai yake da hannu dayan dayan kuma yana rik'e da nata be ce uffan ba, be kuma sake kallon ta ba bare ta saka ran zai mata magana.
RM
34
***Driving kawai yake da hannu daya, dayan kuma yana rik'e da nata be ce uffan, be kuma sake kallon ta ba bare ta saka ran zai mata magana. Yayi kokari sosai wajen maintaining coolness dinsa dan yadda yake ji kamar ya koma ya saka a kama masa Adam a kulle masa shi har sai ya manta da Asma'un da duk abinda ya shafe shi, kishin sa yake ji sosai a yau fiye da kullum,
"Ka... Kayi hakuri.". Ta samu kanta da furtawa cikin rarrabewar kalmomi, kansa a gaba yana kallon titi ya dan matsa hannun ta kad'an amma bai ce komai,shiru ne ya sake biyo bayan motar, hanyar office ya dauka, akwai hadari sosai a area ba kamar baya da suka baro ba, har iska ta soma kadawa kad'an kad'an, rage tafiyar yayi ya shiga layin, har lokacin idanun sa na kan hanya hakan ya kara tabbatar mata ransa babu dadi. Kanta ta daga tana kallon building din dogon gaske, a chan sama ta hangi suna K'AREFA, bata gama karantawa ba aka wangale katoton gate din, harabar wajen cike take da motoci sababbi masu kyau, sai hadahadar mutane daga chan gefe, ciki sosai ya shiga da motar sannan yayi parking ya kashe ta, sai a lokacin ya juyo yana kallon ta, yana kallon mayafin da yake jikinta, babba ne amma kuma ba shi da kauri sosai, har yana iya hango rigar jikinta amma ba tar ba, sai ka saka ido sosai, kusa da ita ya matso sosai ya zura kansa bayan motar, ta sauke numfashi tana jin closeness din nasu na haifar mata da yanayi, rigar sa ya dauko jacket, ya kama mayafin nata yana kallonta cikin ido, dan motsawa tayi kadan ya karasa nannade mayafin ya dora mata jacket din akai, ya balle mata sannan ya maida mata mayafin ta, baya ya danyi yana so ya tabbatar da baa gani yanzu,sai ya fito yana zagayo side dinta ya bud'e mata. Fitowa tayi tana sadda kanta k'asa mamakin sa na cikata, tafiya ya soma yi bayan ya saka hannun sa a nata yabi hanyar baya mara cinkoso da hayaniya, ya shiga ta wata kofa inda suka tarar da mutane uku a zaune kowannen su na duba takardu a gaban su, daya mace ce sai sauran maza biyu, da sauri suka tashi tsaye suna masa sannu da zuwa dan rabon sa da bangaren kusan sati kenan MD ne yake kula da duk baangarorin, hannu ya daga musu kawai ya wuce da dan sassarfa ya danna bud'e kofar lift din ta bud'e ta shiga sannan ya mara mata baya, kus-kus suka hau yi bayan shigewar su, cikin yanayi na ban mamaki dan basu san komai game da maganar auren nasa ba, ba kuma su sanshi a mutumin banza ba. Duk iya hasashen su ba su iya hasaso komai ba, sai suka hakura duk suka koma bakin aikin su, suna masu kyautata masa zato.
Binsa kawai take kamar rakumi da akala, har suka dangana da babban office din nasa, ya bud'e suka shiga ciki sannan ya murza key din yana sakin hannun ta, ya wuce gaba da sauri ya shiga toilet din dake cikin office din, tsaye tayi a inda ya barta tana satar kallon office din da yayi masifar tsaruwa, ga wani sanyin dadi da kamshi irin wanda take ji a jikinsa a duk sanda yazo wajen ta, tana nan a tsayen tana more kallon komai a tsanake ya fito hannun rigar sa a nannade, ya kalle ta yana takowa zuwa wajen da take tsaye
"Zo ki zauna."
Ya nuna mata couch din dake gefe da hannun sa, wuce shi tayi ta zauna a dosane tana mamakin sauyawarsa kamar bashi ba, bata san wannan side din nasa ba, sai yau da ya nuna mata shi din miskili ne, na gaske. Iska ce ta taso da karfi, ya rufe dukka windows din, ya rage hasken office din ya zama dim, duk abinda yake tana ta satar kallon sa, aka soma ruwan da karfin gaske, kujerar sa ya hau, ya bud'e system dinsa yana so ya rage abinda yake ji a zuciyar sa, baya so tunanin da zuciyar sa take bashi yayi tasiri akan sa, duk in da ya shiga sai ya fita ba tare da ya iya aikata komai ba, haka ya dinga shiga nan ya fita nan har ya gaji ya ture system din yana jan dan siririn tsaki, baya jin zai iya jure tsawon kwanakin da Baban yace zata tare gaskiya, dan hankalin sa ba zai taba kwanciya ba in dai har Adam na kaiwawo a tsakanin gidan nasu. Wajen da take ya kalla sai yaji ta bashi tausayi musamman sharentan da yake, yasan ba ita tayi masa laifin ba amma ya rasa dalilin da ya saka shi jin zafin sosai, lura yayi da tana jin sanyi kamar, dan ta dage kafarta sama ta cure waje daya, remote din AC ya dauka ya kashe ta gaba daya, ya ajiye ya isa wajen da take, ya durkusa a gabanta yana kamo hannunta cikin nasa
"Kayi hakuri." Ta sake ce masa a karo na biyu, hakan ya kara masa tausayin ta sosai, ya daga mata kai kafin ya furta
"Baki min laifi ba ai."
"Naga kamar kana fushi dani."
Green sandal,Sudanese mix,Shek Bakhur, Sandal coconut.
Dorot , Hadut, Gabgab,Kajiji balls.
Aroosa da sauran su. Ga kuma maganin infection sadidan, su tsumi, zumar chad da sauran kayan gyara na kankaro mutunci, ga hadaddun khumra masu masifar kamshi da kama jiki, turaren wanka da na gashi, ga kuma na carpet da na curtains musamman a yanayin damunar nan. Amaryar kb Global Enterprise dai ta hada komai na gyara da kankaro mutunci 08067558902 shiyasa ma Ya Hadiza taga ya kamata ta kirata, suyi magana ta gyara Asma'un ciki da waje, ana cikin maganar ne sakon sa ya shigo, shine ta zame ta shige daki ta fad'a toilet tayi wanka a gurguje ta fito ta shafa daya daga cikin khumran da Ya Hadiza ta taho mata dashi na cikin kayan da Amaryar Kb take saidawa ta shafa ta dan shafa powder da wetlips, ta sake bin jikinta ta feshe shi da wasu kalolin turarurrukan masu sanyin kashi sannan ta zauna tana tunanin yadda zatayi ta fita idan yace mata yazo, Hidaya ce ta biyota ciki, ta ganta a shirye tsaf tana danna wayar ta, basarwa tayi kamar bata ga shigowar Hidayan ba, juyawa tayi ta tseguntawa su Yaya Hadiza, suka yi dariya har Umma da dadi ya lullube ta, fitar hidayan da kad'an zai ga kiran sa, ta daga gabanta na faduwa yace yana waje, a kasalance tace toh ta tashi ta shiga zagaye a dakin ta rasa ta ina zata fita, kunyar su take ji tana jiyo hirar su a tsakar gidan, kuru tayi ta daure ta fito rik'e da flat shoe dinta a hannu, taki yarda su hada ido da kowa tace
"Umma shine yazo."
"Allah ya kiyaye, ki gaishe shi."
Har tayi gaba Ya Hadiza tace bari ta tsokaneta
"Cewa zakiyi Umma angon yazo."
Dariya suka kwashe da, ta daga kafarta da sauri ta fice taji umma na cewa ya Hadiza ya kyale mata yarta.
Bayan sa ta hanga ya juya shi yana facing din kofar shigowa, dogo ne me cike da haiba, ba shi da rama sannan ba shi da kiba jikinsa dai-dai ya dace da yanayin sa, riga da wandon yadi ne a jikin sa ash colour dinkin rigar daga dan ya wuce guiwar sa, kansa babu hula sai takalmin kafarsa sau ciki, duk a dan dakikun da basu gaza goma ba ta gama tantance shi, takun ta yaji ya juyo da sauri yana rik'e da car key dinsa da babbar wayar sa a hannu, murmushi ya sakar mata ita ma ta maida masa tana russunar da kanta ganin ya kafe ta da kallon sa wanda yake kashe mata jiki, a gefen sa ta tsaya ta gaishe shi, maimakon ya amsa sai ya mika mata hannu alamun su gaisa, a kunyace ta mika masa ya kama hannun ya rik'e yana dan motsa shi acikin nasa hannu.
"Kinyi kyau sosai." Ya fad'a yana kallon lips dinta da suke shekin lips balms, kauda kai tayi cike da jin kunyar sa, har lokacin be saki hannun ta ba, kamar ma hakan na sashi nishadi, ciki tace ya shigo ya noke kafada
"Ban gama kallon ki ba, nan yafi haske na more kallon matata."
"Kai..."
"Emana."
"Dallah malam cika mata hannu! "
Ya buga tsawa idonsa na kankancewa cikin tsakanin tashin hankalin ganin hannun Asma'un cikin na Abdallah, tahowa yayi gadan gadan, wani banzan kallo Abdallan yayi masa ya saka hannu ya matso da Asma'un jikinsa sosai sannan yace
" Don't you dare, karka kuskura ka karaso kusa da matata."
" Matar ka? Yaushe ta zama matar ka?"
" Kaje ka tambaya kaji, kuma wallahi ko kusa da ita na ganka wallahi sai na daure ka kaji na rantse, shashasha kawai. "
A karkace Umar yayi parking suka fito shida Abbati a dari suka fado gidan ganin motar Abdallan data Adam a kofar gidan, suna zuwa suka damke Adam din daya fara hauka yana kokarin jan Asma'un, hannun ta cikin nasa ya shiga takawa da ita, ya nufi gate din gidan ya fita da ita, Adam ya birkice ya dinga kwala mata kira su Abbati suka rik'e shi gam, gaban motar ya bud'e mata ya sakata, sannan ya dawo ya shiga ya tada motar suka bar layin, ransa ya kai kololuwa a baci amma calmness dinsa na tare dashi, satar kallon sa take, driving kawai yake da hannu dayan dayan kuma yana rik'e da nata be ce uffan ba, be kuma sake kallon ta ba bare ta saka ran zai mata magana.
RM
34
***Driving kawai yake da hannu daya, dayan kuma yana rik'e da nata be ce uffan, be kuma sake kallon ta ba bare ta saka ran zai mata magana. Yayi kokari sosai wajen maintaining coolness dinsa dan yadda yake ji kamar ya koma ya saka a kama masa Adam a kulle masa shi har sai ya manta da Asma'un da duk abinda ya shafe shi, kishin sa yake ji sosai a yau fiye da kullum,
"Ka... Kayi hakuri.". Ta samu kanta da furtawa cikin rarrabewar kalmomi, kansa a gaba yana kallon titi ya dan matsa hannun ta kad'an amma bai ce komai,shiru ne ya sake biyo bayan motar, hanyar office ya dauka, akwai hadari sosai a area ba kamar baya da suka baro ba, har iska ta soma kadawa kad'an kad'an, rage tafiyar yayi ya shiga layin, har lokacin idanun sa na kan hanya hakan ya kara tabbatar mata ransa babu dadi. Kanta ta daga tana kallon building din dogon gaske, a chan sama ta hangi suna K'AREFA, bata gama karantawa ba aka wangale katoton gate din, harabar wajen cike take da motoci sababbi masu kyau, sai hadahadar mutane daga chan gefe, ciki sosai ya shiga da motar sannan yayi parking ya kashe ta, sai a lokacin ya juyo yana kallon ta, yana kallon mayafin da yake jikinta, babba ne amma kuma ba shi da kauri sosai, har yana iya hango rigar jikinta amma ba tar ba, sai ka saka ido sosai, kusa da ita ya matso sosai ya zura kansa bayan motar, ta sauke numfashi tana jin closeness din nasu na haifar mata da yanayi, rigar sa ya dauko jacket, ya kama mayafin nata yana kallonta cikin ido, dan motsawa tayi kadan ya karasa nannade mayafin ya dora mata jacket din akai, ya balle mata sannan ya maida mata mayafin ta, baya ya danyi yana so ya tabbatar da baa gani yanzu,sai ya fito yana zagayo side dinta ya bud'e mata. Fitowa tayi tana sadda kanta k'asa mamakin sa na cikata, tafiya ya soma yi bayan ya saka hannun sa a nata yabi hanyar baya mara cinkoso da hayaniya, ya shiga ta wata kofa inda suka tarar da mutane uku a zaune kowannen su na duba takardu a gaban su, daya mace ce sai sauran maza biyu, da sauri suka tashi tsaye suna masa sannu da zuwa dan rabon sa da bangaren kusan sati kenan MD ne yake kula da duk baangarorin, hannu ya daga musu kawai ya wuce da dan sassarfa ya danna bud'e kofar lift din ta bud'e ta shiga sannan ya mara mata baya, kus-kus suka hau yi bayan shigewar su, cikin yanayi na ban mamaki dan basu san komai game da maganar auren nasa ba, ba kuma su sanshi a mutumin banza ba. Duk iya hasashen su ba su iya hasaso komai ba, sai suka hakura duk suka koma bakin aikin su, suna masu kyautata masa zato.
Binsa kawai take kamar rakumi da akala, har suka dangana da babban office din nasa, ya bud'e suka shiga ciki sannan ya murza key din yana sakin hannun ta, ya wuce gaba da sauri ya shiga toilet din dake cikin office din, tsaye tayi a inda ya barta tana satar kallon office din da yayi masifar tsaruwa, ga wani sanyin dadi da kamshi irin wanda take ji a jikinsa a duk sanda yazo wajen ta, tana nan a tsayen tana more kallon komai a tsanake ya fito hannun rigar sa a nannade, ya kalle ta yana takowa zuwa wajen da take tsaye
"Zo ki zauna."
Ya nuna mata couch din dake gefe da hannun sa, wuce shi tayi ta zauna a dosane tana mamakin sauyawarsa kamar bashi ba, bata san wannan side din nasa ba, sai yau da ya nuna mata shi din miskili ne, na gaske. Iska ce ta taso da karfi, ya rufe dukka windows din, ya rage hasken office din ya zama dim, duk abinda yake tana ta satar kallon sa, aka soma ruwan da karfin gaske, kujerar sa ya hau, ya bud'e system dinsa yana so ya rage abinda yake ji a zuciyar sa, baya so tunanin da zuciyar sa take bashi yayi tasiri akan sa, duk in da ya shiga sai ya fita ba tare da ya iya aikata komai ba, haka ya dinga shiga nan ya fita nan har ya gaji ya ture system din yana jan dan siririn tsaki, baya jin zai iya jure tsawon kwanakin da Baban yace zata tare gaskiya, dan hankalin sa ba zai taba kwanciya ba in dai har Adam na kaiwawo a tsakanin gidan nasu. Wajen da take ya kalla sai yaji ta bashi tausayi musamman sharentan da yake, yasan ba ita tayi masa laifin ba amma ya rasa dalilin da ya saka shi jin zafin sosai, lura yayi da tana jin sanyi kamar, dan ta dage kafarta sama ta cure waje daya, remote din AC ya dauka ya kashe ta gaba daya, ya ajiye ya isa wajen da take, ya durkusa a gabanta yana kamo hannunta cikin nasa
"Kayi hakuri." Ta sake ce masa a karo na biyu, hakan ya kara masa tausayin ta sosai, ya daga mata kai kafin ya furta
"Baki min laifi ba ai."
"Naga kamar kana fushi dani."