Sashe 35
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yau dai naga wadda ta sace min zuciyar brother na, Masha Allah."
"Kaje mota gani nan"
"Ban gama ba, kina lafiya?"
"Lafiya lou."
"Toh Madallah, sunana Mudassir, amma an fi kirana da MD, kuma ni kanin sa ne, kuma best friend dinsa."
"Allah sarki."
" Kaje mota."
"Zan dawo ni kadai Aunty, tunda yanzu korata yake, bari na je motar bansan me yazo fad'a ba."
Ya juya yana dariyar mugunta, ya fice. Kallon cikin ido yayi mata bayan fitar MD, tayi saurin kauda idon ta tana sunne kanta k'asa,
" Ina office fa, naji kawai inason ganinki, dole na ajiye komai na taho shi kuma wannan uban surutun yazo zai cika miki kunne."
" Ba komai, ai yana da kirki."
" Ko?"
Kanta a kasa ta amsa, hakan ya bashi damar sake more kallon ta, yana admiring kyawunta, da cute innocent face dinta, calmness dinta yaana kara masa sonta
" Pleaseeee...Bari naga fuskarki sosai yadda ko na koma office ba zan kasa aiki ba, sai nayi ta tunawa."
Rufe fuskar tayi da tafin hannun ta, tayi dariya, ita da gaske kunya yake bata dan bata taba experiencing irin haka ba, da yaga da gaske dai kunyar sa take ji sai ya hakura, yace mata zai dawo, amma next zuwan da zai sai ya fara ganin Abba, daga nan sai yaga me ya kamata ayi, ita dai kawai jin sa take yi.
Komawa tayi ciki bayan yayi mata sallama ya tafi, yaje ya samu MD a mota yana waya, tada motar yayi suka bar unguwar har lokacin yana waya, sai da ya gama sannan yake fad'a masa jirgin su Baba Alhaji ya kusa sauka, dan haka yana sauke shi a office din ya wuce airport dauko shi, dan be yarda wani ya dauko shi ba idan ba MD din ko Abuyan ba.
Suna barin unguwar Adam na isowa, duk ya lalata motar sa dan tuki na hauka ya dinga yi baya kaucewa rami ko duk abinda yake hanyar, kafin yazo duk ta kakkarje ga dattin da tayi, Umar yaga sanda ya shigo layin a haukace, ya biyo bayan sa da sauri ya fasa siyan abinda zai siya, kafin ya karaso har ya shiga gidan kasancewar shi a mota yake shi kuma a kafa, a tsakar gidan ya same shi, umma tana tsaye daga kofar dakin ta, Asma'u kuma na cikin daki rufe har da key dan yanzu Adam ya wuce a sashi a layin masu hankali sai dai mahaukata. Sosai umma tayi mamakin yadda ya koma, kamar bashi ba ga uwar kasumba da ya tara na rashin gyara, Umar na shigowa be yi wata wata ba, ya zabga masa mari, ya rik'e shi yana kokarin dukan sa
"Menene haka Umar?" Umma ta daka masa tsawa
"Abinda ya dace dashi kenan umma, duk abinda yake wallahi iskanci ne, dan yaga ana kyale shi ne."
" Cika shi, babu ruwanka dashi duk wanda yayi nagari kansa, ai ko yanzu Adam ya gane cewa ba abu bane me kyau zalunci, idan Allah yaso kamaka sai ya kamaka ta in da baka yi zata ba."
" Toh ai Umma be ma kamata a bar shi ya shigo gidan nan ba, dan zai iya cutar da Asma'u."
" Babu abinda zai iya yi mata."
" Umma dan Girman Allah ayi hakuri, wallahi umma nayi nadama dan Allah Asma'u ta saurare ni, dan Allah magana kawai zan fada mata nasan zata amince."
"Wai Adam baka san babu aure tsakanin ka da Asma'u bane ko yaya?"
" Za'a iya gyarawa umma, dan Allah ki taimaka min."
" Tirkashi! Abun naka babba ne Adam."
Tace tana rik'e baki, jingina yayi da bangon tsakar gidan, Asma'u ta leko ta window ta hange shi a tsaye ya rataya hannun sa ta bayan sa, Umar na gefe yana hararar sa kamar ya kai masa bugu, umma kuma na kofar dakin ta, tana jiran Abba da ta kira yace gashi nan, komawa tayi ta haye gado tayi kwanciyar ta, dan bata da bukatar ji ko ganin duk wani abu da ya danganci Adam din.
Shiru Abban be karaso ba, umma ta shige ciki aka barshi a wajen, a rana amma kamar be damu ba, ya cigaaba da zaman jiran fitowar Asma'un, a daidai lokacin Fido da kawayenta suke isa gidan, Hajiya Mama na tsakar gida tana bawa masu aikinta sallahu dan Abba yace tazo gidan ayi magana, sai gasu sun shigo sun saka Fido a tsakiya ta sha lullubi a dole amarya, turus Hajiyan tayi, jiki a sanyaye ta jasu cikin falon, suka gaishe ta Faiza tace amarya suke kawo, da kanta ta tashi ta rakasu har gidan Adam din, sannan ta fito jikin ta na kara sanyaya, a halin da Adam din yake ciki yanzu bata san yadda zai karbi batun auren ba, wanda ita kanta bata san me ya sha kanta ta amince ba, dan sai yanzu take jin ta tafka babban kuskure wajen amincewa,amma kuma bata san ya zatayi ba, bata da zabi.
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ 2
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
RM
*28*
*****
Yana tsaye a tsakar gidan Hajiya ta shigo, ganin ta be saka shi tashi ba, sai ma sake gyara tsaiwar sa da yayi dan ko sama da k'asa zata hade yau sai yayi magana da Asma'u, yasan zata fahimce shi, yasan zata sake bashi dama,
"Adam!" Ta kira sunan sa tana rik'e bakin ta, sai kuma ta kada kanta zuwa ciki tana kwala sallama, jin sallamar ta ya saka Umma fitowa, tayi mata iso zuwa ciki, ta kasa zama ta tsaya daga tsaye jikin ta duk yayi sanyi
"Be karaso ba amma nasan daf yake da shigowa."
"Assalamu alaikum." Yayi sallama tana shigowa gidan
"Yauwa gashi nan ma."
Waje sukayo tare, suka tarar dashi a tsaye a gaban Adam din yana masa magana,
"Tsaiwar me kake anan Adam?"
Maimakon ya bashi amsa sai kawai gani sukayi ya zube guiwowin sa a k'asa
"Abba dan Allah kayi min rai."
"Tashi maza, tashi." Ya dago shi amma sai ya noke yana cigaba da magiya da hada Abban da Allah, jikin Mama ya kara sanyi sosai tana daga gefe bata ce komai ba, duk abinda yake faruwa bata tanka ba, fad'a Abban ya soma yiwa Adam din cikin sigar lallashi, amma sam ya kasa fahimta shi dai kawai ayi hakuri dan Allah, ganin da gaske ba zai gane ba, ya saka Abban yin gaba yana cewa
"Umar dauki waya ya kira min Ali."
Toh yace yana komawa daki ya dauko wayar sa, ya kira ya taho da wayar ya mikawa Abban, dagawa yayi da sallama ya gaida Abban,
"Kana jina Ali, yaron nan da yazo neman auren Asma'u nake so ka tura min shi, idan zai iya zuwa yanzu toh, idan sai yamma ma dai ina jiran sa."
"Yawwa." Ya katse kiran yana juyawa wajen Hajiya Mama
"Yaya nayi wa Asma'u miji in sha Allah, dalilin sanin cewa babu aure a tsakanin su da Adamu, dan haka nake so gani baki ga mahaifiyar Asma'u, ina so Adam ya kyale Asma'u ya barta tayi facing rayuwar ta, bana son wata matsala ta taso, alakar dake tsakanin mu tafi karfin abinda zai kai mu wajen hukuma, amma tabbas da ba Adam bane ya dauki Asma'u toh sai dai hukuma ta raba mu dashi."
"Na sani." Tace
" Amma kayi hakuri nasan ko ta ina ba'a kyauta maka ba, zan masa fad'a in sha Allah ba zai sake zamar wa Asma'u matsala ba."
"Kai kuma Wuce muje."
Kin tafiya yayi, ya cigaba da magiya, ciki Abba ya shige umma ma haka, ganin yaki tashi ya saka Hajiya Mama fita waje, ta kudura a ranta duk ma abinda zasu masa suyi masa kawai ita ta gaji, tana fita Umar ya fito, ganin babu kowa a wajen yazo da sauri yana kama kafadar Adam din
"Tashi ka fita, wallahi ko zaka mutu Asma'u ba zata ganka ba."
"Dan Allah minti biyu kawai ya isa, dan Allah."
"Ko minti rabi ne wallahi ba zaka ganta ba, kaje chan an kai maka mata, karka zo nan ka ishe mu."
"Mata?"
"Oho idan kaje ai zaka gani."
Cikin hanzari ya mike, yayi hanyar waje da mugun sauri, dariyar mugunta Umar ya fashe da, har da tafa hannu, yana cike da jin dadin yadda abubuwan suka sauya wa Adam din a dare daya, dama chan basa shiri haushin sa yake ji saboda shegen girman kansa. Asma'u na jin duk abinda akeyi, ta sake gyara kwanciyar ta kawai tana jin duk babu dadi.
"Kaje mota gani nan"
"Ban gama ba, kina lafiya?"
"Lafiya lou."
"Toh Madallah, sunana Mudassir, amma an fi kirana da MD, kuma ni kanin sa ne, kuma best friend dinsa."
"Allah sarki."
" Kaje mota."
"Zan dawo ni kadai Aunty, tunda yanzu korata yake, bari na je motar bansan me yazo fad'a ba."
Ya juya yana dariyar mugunta, ya fice. Kallon cikin ido yayi mata bayan fitar MD, tayi saurin kauda idon ta tana sunne kanta k'asa,
" Ina office fa, naji kawai inason ganinki, dole na ajiye komai na taho shi kuma wannan uban surutun yazo zai cika miki kunne."
" Ba komai, ai yana da kirki."
" Ko?"
Kanta a kasa ta amsa, hakan ya bashi damar sake more kallon ta, yana admiring kyawunta, da cute innocent face dinta, calmness dinta yaana kara masa sonta
" Pleaseeee...Bari naga fuskarki sosai yadda ko na koma office ba zan kasa aiki ba, sai nayi ta tunawa."
Rufe fuskar tayi da tafin hannun ta, tayi dariya, ita da gaske kunya yake bata dan bata taba experiencing irin haka ba, da yaga da gaske dai kunyar sa take ji sai ya hakura, yace mata zai dawo, amma next zuwan da zai sai ya fara ganin Abba, daga nan sai yaga me ya kamata ayi, ita dai kawai jin sa take yi.
Komawa tayi ciki bayan yayi mata sallama ya tafi, yaje ya samu MD a mota yana waya, tada motar yayi suka bar unguwar har lokacin yana waya, sai da ya gama sannan yake fad'a masa jirgin su Baba Alhaji ya kusa sauka, dan haka yana sauke shi a office din ya wuce airport dauko shi, dan be yarda wani ya dauko shi ba idan ba MD din ko Abuyan ba.
Suna barin unguwar Adam na isowa, duk ya lalata motar sa dan tuki na hauka ya dinga yi baya kaucewa rami ko duk abinda yake hanyar, kafin yazo duk ta kakkarje ga dattin da tayi, Umar yaga sanda ya shigo layin a haukace, ya biyo bayan sa da sauri ya fasa siyan abinda zai siya, kafin ya karaso har ya shiga gidan kasancewar shi a mota yake shi kuma a kafa, a tsakar gidan ya same shi, umma tana tsaye daga kofar dakin ta, Asma'u kuma na cikin daki rufe har da key dan yanzu Adam ya wuce a sashi a layin masu hankali sai dai mahaukata. Sosai umma tayi mamakin yadda ya koma, kamar bashi ba ga uwar kasumba da ya tara na rashin gyara, Umar na shigowa be yi wata wata ba, ya zabga masa mari, ya rik'e shi yana kokarin dukan sa
"Menene haka Umar?" Umma ta daka masa tsawa
"Abinda ya dace dashi kenan umma, duk abinda yake wallahi iskanci ne, dan yaga ana kyale shi ne."
" Cika shi, babu ruwanka dashi duk wanda yayi nagari kansa, ai ko yanzu Adam ya gane cewa ba abu bane me kyau zalunci, idan Allah yaso kamaka sai ya kamaka ta in da baka yi zata ba."
" Toh ai Umma be ma kamata a bar shi ya shigo gidan nan ba, dan zai iya cutar da Asma'u."
" Babu abinda zai iya yi mata."
" Umma dan Girman Allah ayi hakuri, wallahi umma nayi nadama dan Allah Asma'u ta saurare ni, dan Allah magana kawai zan fada mata nasan zata amince."
"Wai Adam baka san babu aure tsakanin ka da Asma'u bane ko yaya?"
" Za'a iya gyarawa umma, dan Allah ki taimaka min."
" Tirkashi! Abun naka babba ne Adam."
Tace tana rik'e baki, jingina yayi da bangon tsakar gidan, Asma'u ta leko ta window ta hange shi a tsaye ya rataya hannun sa ta bayan sa, Umar na gefe yana hararar sa kamar ya kai masa bugu, umma kuma na kofar dakin ta, tana jiran Abba da ta kira yace gashi nan, komawa tayi ta haye gado tayi kwanciyar ta, dan bata da bukatar ji ko ganin duk wani abu da ya danganci Adam din.
Shiru Abban be karaso ba, umma ta shige ciki aka barshi a wajen, a rana amma kamar be damu ba, ya cigaaba da zaman jiran fitowar Asma'un, a daidai lokacin Fido da kawayenta suke isa gidan, Hajiya Mama na tsakar gida tana bawa masu aikinta sallahu dan Abba yace tazo gidan ayi magana, sai gasu sun shigo sun saka Fido a tsakiya ta sha lullubi a dole amarya, turus Hajiyan tayi, jiki a sanyaye ta jasu cikin falon, suka gaishe ta Faiza tace amarya suke kawo, da kanta ta tashi ta rakasu har gidan Adam din, sannan ta fito jikin ta na kara sanyaya, a halin da Adam din yake ciki yanzu bata san yadda zai karbi batun auren ba, wanda ita kanta bata san me ya sha kanta ta amince ba, dan sai yanzu take jin ta tafka babban kuskure wajen amincewa,amma kuma bata san ya zatayi ba, bata da zabi.
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_
_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ 2
_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_
_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._
_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH
_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_
_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰
_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍
_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰
_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️
_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍
***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
RM
*28*
*****
Yana tsaye a tsakar gidan Hajiya ta shigo, ganin ta be saka shi tashi ba, sai ma sake gyara tsaiwar sa da yayi dan ko sama da k'asa zata hade yau sai yayi magana da Asma'u, yasan zata fahimce shi, yasan zata sake bashi dama,
"Adam!" Ta kira sunan sa tana rik'e bakin ta, sai kuma ta kada kanta zuwa ciki tana kwala sallama, jin sallamar ta ya saka Umma fitowa, tayi mata iso zuwa ciki, ta kasa zama ta tsaya daga tsaye jikin ta duk yayi sanyi
"Be karaso ba amma nasan daf yake da shigowa."
"Assalamu alaikum." Yayi sallama tana shigowa gidan
"Yauwa gashi nan ma."
Waje sukayo tare, suka tarar dashi a tsaye a gaban Adam din yana masa magana,
"Tsaiwar me kake anan Adam?"
Maimakon ya bashi amsa sai kawai gani sukayi ya zube guiwowin sa a k'asa
"Abba dan Allah kayi min rai."
"Tashi maza, tashi." Ya dago shi amma sai ya noke yana cigaba da magiya da hada Abban da Allah, jikin Mama ya kara sanyi sosai tana daga gefe bata ce komai ba, duk abinda yake faruwa bata tanka ba, fad'a Abban ya soma yiwa Adam din cikin sigar lallashi, amma sam ya kasa fahimta shi dai kawai ayi hakuri dan Allah, ganin da gaske ba zai gane ba, ya saka Abban yin gaba yana cewa
"Umar dauki waya ya kira min Ali."
Toh yace yana komawa daki ya dauko wayar sa, ya kira ya taho da wayar ya mikawa Abban, dagawa yayi da sallama ya gaida Abban,
"Kana jina Ali, yaron nan da yazo neman auren Asma'u nake so ka tura min shi, idan zai iya zuwa yanzu toh, idan sai yamma ma dai ina jiran sa."
"Yawwa." Ya katse kiran yana juyawa wajen Hajiya Mama
"Yaya nayi wa Asma'u miji in sha Allah, dalilin sanin cewa babu aure a tsakanin su da Adamu, dan haka nake so gani baki ga mahaifiyar Asma'u, ina so Adam ya kyale Asma'u ya barta tayi facing rayuwar ta, bana son wata matsala ta taso, alakar dake tsakanin mu tafi karfin abinda zai kai mu wajen hukuma, amma tabbas da ba Adam bane ya dauki Asma'u toh sai dai hukuma ta raba mu dashi."
"Na sani." Tace
" Amma kayi hakuri nasan ko ta ina ba'a kyauta maka ba, zan masa fad'a in sha Allah ba zai sake zamar wa Asma'u matsala ba."
"Kai kuma Wuce muje."
Kin tafiya yayi, ya cigaba da magiya, ciki Abba ya shige umma ma haka, ganin yaki tashi ya saka Hajiya Mama fita waje, ta kudura a ranta duk ma abinda zasu masa suyi masa kawai ita ta gaji, tana fita Umar ya fito, ganin babu kowa a wajen yazo da sauri yana kama kafadar Adam din
"Tashi ka fita, wallahi ko zaka mutu Asma'u ba zata ganka ba."
"Dan Allah minti biyu kawai ya isa, dan Allah."
"Ko minti rabi ne wallahi ba zaka ganta ba, kaje chan an kai maka mata, karka zo nan ka ishe mu."
"Mata?"
"Oho idan kaje ai zaka gani."
Cikin hanzari ya mike, yayi hanyar waje da mugun sauri, dariyar mugunta Umar ya fashe da, har da tafa hannu, yana cike da jin dadin yadda abubuwan suka sauya wa Adam din a dare daya, dama chan basa shiri haushin sa yake ji saboda shegen girman kansa. Asma'u na jin duk abinda akeyi, ta sake gyara kwanciyar ta kawai tana jin duk babu dadi.