Sashe 19
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsaki taja ta shige tana ganin kamar Adam din ma tsoron Asma'un yake ji, duk tsaurin sa da zafin sa akanta baya iya komai.
Sai da ya tabbatar Hajiyan ta shige ya kanne ma Asma'un ido daya ya sa dariya. Jiki a sanyaye ta koma wajen masu aikin ta cigaba da aikin amma rabin hankalin ta na ga abinda ya faru, tana jin ana cewa makircin mata bata san a mazan ma akwai makirai ba, marasa tsoron Allah masu dabi'ar da bata san me ma zata kira su ba.
Dare sosai ta kai a gidan sannan ta koma gida a gajiya tikis, kamar ta dora hannu aka tayi ta ihu haka take ji, zafi goma da ashirin, ta taba jin labarin makirin namiji wanda zai nuna a gaban yan uwansa shi din na kirki ne, ya kuma musguna miki a gida daga ke sai shi, irin Adam kenan shi abin nasa ma har yayi yawa dan ko ita da take mace ma ba zata iya abinda yayi ba wallahi.
Duk da uwar gajiyar da ta sha haka ta dora abincin dare me sauki ta ajiye masa ranta duk babu dadi, tana ajiyewa yazo ya haye yaci yayi kyatsa ya bar mata komai a wajen tazo ta tattare ta kai kitchen dan ba zata iya kuma wanke su a daren ba, burin ta kawai ta ajiye hakarkarin ta a kasa ko zata ji dadi. Kwanciyar ta kenan bacci ma ya soma daukar ta, taji ana tabata, ta yinkurin tashi amma ya danne ta, sai da yayi abinda ya kawo shi sannan ya tsallake yayi ficewar sa, ya barta da kuka me cin rai, ta tsani Adam ta tsani ko da jin sunan sa ne, haka ta tashi ta tsaftace jikin ta, sannan ta dawo ta kwanta amma sai ta nemi baccin da take ji ta rasa, tayi tayi amma sam yaki zuwa, tunani ta hau yi, ta saka wannan ta kwance wannan, ganin kwanciyar haka babu amfani sai kawai ta tashi ta dauro alwala ta raya daren, tana idarwa nan da nan bacci ya kwashe ta.
Da asubah ta farka kasan mararta na dan mata ciwo kad'an kad'an, har ta idar da sallah be daina ba, komawa tayi ta kwanta dan bata jin zata iya yin wani abu, kasala take ji sosai shiyasa har gari yayi sosai bata mike ba. Fitowa yayi ya nufi dinning din kamar yadda ya saba sai yaga wayam, haushi ne ya turnike shi dan yana sane jiya ya shigo da doya dan ita yake sha'awar ci yasan kuma in dai ta gani zata soya musu ita, yana matukar jin dadin abincin ta sosai shiyasa duk abinda yake baya taba yarda ya wuce shi, ji yayi ransa na sake baci, ya koma saman ya tura dakin sai ya tarar da ita a kwance a gado ya lulluba har kanta, yaye abun da ta rufar yayi, suka kalli juna
"Ina breakfast?" Yace yana tsaye kanta
"Babu." Tace kanta tsaye ta juya dayan side din, bankaro ta yayi ya juyo da ita
"Ya ina miki magana zaki juya min baya, uban wa ya saka ki fara abinda ba zaki iya dorewa ba, ko kinyi tunanin zaki sace zuciya ta da girkin ki ne?"
"Dan Allah Ya Adam ka rabu dani, ni na saka kaina nayi girkin kuma yau ban ba, ka kyale ni naji da abinda yake damuna dan Allah."
Tace cike da kosawa da halin sa
"Tashi zakiyi ki soya min doya kiyi min sauce, ina jiranki fita zanyi."
Tana jin sa ya juya ya fice, ta cigaba da kwanciya a wajen ciwon marar na karuwa sosai. Chan wajen minti talatin ya dawo dakin, ya tarar da ita a yarda ya barta, ransa idan yayi dubu ya baci, ya fizgota da karfi ta fado daga gadon, ya shiga kokarin neman abun da zai saka ya daketa. Tunawa yayi da belt din dake jikin wandon sa, ya hau kokarin ballo ta, tayi saurin rik'e hannun shi tuni har ta soma kuka sosai
"Dan Allah kayi hakuri wallahi bani da lafiya ne."
Be ji ta ba, bakar zuciyar shi ta riga ta ingiza shi, ya daddage ya zabga mata da karfin gaske, ta gantsare tana kwala karar azaba, idon sa ya rufe ruf, burin sa kawai yayi mata lilis yadda gobe ba zata sake ja dashi ba, baya son raini da wulakanci ba kuma zai dauka a wajenta ba, ita din da bata da maraba da takalmin sawar sa, wanda yake takawa ya wuce. Sau uku yana zabga mata, ta rarrafa da k'yar ta shige bayan gadon, biyo ta yayi ya sake dagawa yaji an rik'e belt din, daga nan yaji saukar mahaukacin mari a kuncin sa, kafin ya dawo hayyacin shi aka sake sauke masa wani me zafin gaske. Umar ne a tsaye yana huci sosai, sai Umma dake gefe tana kuka sosai, sakin belt din yayi ya fadi kasa, umar din ya shaki wuyan sa ya gwara kansa da bangon dakin.
"Kasheta zakayi? Kasheta zakayi? Wallahi kafin ka kasheta ni zan fara kasheka, shege dan iska mara mutunci." Ya sake kaiwa bakin sa naushi
"Umar zo ka daga ta, mu kaita asibiti kamar tayi bari." Umma tace tana kuka ta tallafo Asma'un jikin ta, sakin sa umar din yayi, babban yayan su Asma'un kenan, yana da masifar zuciya shi yasa baya shiga sabgar kowa, yanzu ma umma ce tazo gidan Hajiyan bayan ta aika da cingam din gayyatar bikin yar kanwar Baban su Adam din wadda ta taba rik'e ta kafin ta koma hannun iyayenta saboda Adam din, duk da Hajiyar bata sani ba, bikin ake shine aikin da su Asma'un suka yi jiya, tayin aikin umman tazo shine tace bari ta fara shigowa gidan Asma'un, sai kuma suka ji ihunta a sama, shine suka hawo da sauri suka tarar da bakin azzalumin yana dukan ta tamkar ya samu jaka.
Bari tayi kamar yadda Umman tayi tunani ganin jini, a asibitin aka kara tabbatar musu sannan aka ce suje suyi scanning a tabbatar ko ya gama fita duka. Daga nan kuma aka bata maganunguna suka wuce gida, gefen idon ta shatin duka ne inda Allah ne ya kiyaye be same ta a ido ba, ajiyar zuciya kawai take babu wanda yayi magana a cikin su, ran umma yayi masifar baci suna isa gida ta kira Abba a waya tace yazo gida babu lafiya, sai gashi nan da nan kuwa, ya tarar da Asma'un a kwance, fuskar ta da ta dan daga ya kalla a tsorace sai kuma ya kalli Umman,
"Gata nan, zuwa mukayi muka tarar da ita yana jibga kamar ya samu jaka, kalli idon ta, bayan ta ma shatin dukan sa ne."
"Duka?"
"Gashi nan ka duba ka gani ai idan baka yarda ba, ko ka kira Baba ai a gabansa akayi."
"Asma'u?" Ya kira sunan ta, ficewa umma tayi daga dakin dan hatta Abban haushin sa take ji sosai.
" Dukan ki adamu yayi wai? "
" Eh. " Ta gida kanta tana goge kwallar takaici
Shiru Abban yayi tamkar ruwa ya cinye shi, jiri jiri yaji yana neman kayar dashi, ya zauna da sauri yana dafe jikin kujerar
" Innalillah wa inna ilaihi rajiun. "
Yayi ta maimaitawa, har ya samu nutsuwa, ya dinga kallon ta tausayin ta na shigar sa sosai. Idan har namiji zai daga hannu ya daki mace, toh lallai ya kai makura a jahilci, be san abun na Adam din ya kai haka ba, be san mahaukaci bane na ajin karshe, waya ya dauka ya kira Ya Asabe, lokacin tana gidan Adam din an kira likita yana goge masa wajen da Umar ya fasa masa, tana ganin kiran Abban ta daga a zafafe
" Yanzu Karami har Umar yayi girman da zai shigo har gidan Adam ya dake shi haka, wacce irin tarbiyya ka bawa yaran nan ne,? Har cikin gidan kazo ka daki mutum saboda kana tunanin wani abu daban? "
" Adamu ya aiko wa Asma'u da takardar sakin ta, yau ba sai gobe ba, idan kuma yaki sai hukuma ta raba mu dashi!"
Yana kaiwa nan ya kashe wayar sa, saroro tayi da wayar a hannu, ta kalli Adam din ta kalli wayar, tana son sake tabbatar da Abban ne dai ya kirata ba wani ya bawa wayar ba, shi din ne dai yayi mata magana babu gaisuwa bare girmamawa!
RM
15
***Ajiye wayar yayi a kusa dashi ya karasa wajen Asma'un yana dubata,
"Tashi kinji."
Yace cikin tsananin tausayin ta, mikewa tayi zaune da k'yar har lokacin kanta na mata masifar ciwo, gefen idon ya dame ta sosai dan ya daga wajen.
"Ina hijab dinki? Zaki iya tafiya!?"
Girgiza wa Abban kai tayi saboda yadda take jin ta very weak, kamar zata fadi haka take ji.
"Ina zuwa." Ya fita yana kwala wa umma kira, ta taso tazo tana kin kallon sa
"Taimaka mata, ta saka Hijab dinta ku sameni a mota."
"Ba dai maida ita zakayi ya karasa kashe ta ba ko?"
Wani kallo yayi wa umman, yayi tsaki yace
"Kuyi sauri nace, ina jiranku."
Kada kai Umman tayi zuwa ciki shi kuma ya fita waje, taimaka mata tayi ta rik'e ta suka fito suka tarar dashi a mota Umar na zaune a mazaunin driver suna magana da Abban.
"Da ka sani ka karairaya shi ka zubar tunda be san mutunci ba."
Abban yace a maimakon tunanin da Umman tayi na zaiyi wa har Umar din fad'a, shiru umar din yayi bayan sun shigo, ya tada motar bayan ya kalli bayan cikin tausayin Asma'un.
"Asibiti zaka fara kaimu, kafin ka kaimu chan gidan tsoho."
Sai da ya tabbatar Hajiyan ta shige ya kanne ma Asma'un ido daya ya sa dariya. Jiki a sanyaye ta koma wajen masu aikin ta cigaba da aikin amma rabin hankalin ta na ga abinda ya faru, tana jin ana cewa makircin mata bata san a mazan ma akwai makirai ba, marasa tsoron Allah masu dabi'ar da bata san me ma zata kira su ba.
Dare sosai ta kai a gidan sannan ta koma gida a gajiya tikis, kamar ta dora hannu aka tayi ta ihu haka take ji, zafi goma da ashirin, ta taba jin labarin makirin namiji wanda zai nuna a gaban yan uwansa shi din na kirki ne, ya kuma musguna miki a gida daga ke sai shi, irin Adam kenan shi abin nasa ma har yayi yawa dan ko ita da take mace ma ba zata iya abinda yayi ba wallahi.
Duk da uwar gajiyar da ta sha haka ta dora abincin dare me sauki ta ajiye masa ranta duk babu dadi, tana ajiyewa yazo ya haye yaci yayi kyatsa ya bar mata komai a wajen tazo ta tattare ta kai kitchen dan ba zata iya kuma wanke su a daren ba, burin ta kawai ta ajiye hakarkarin ta a kasa ko zata ji dadi. Kwanciyar ta kenan bacci ma ya soma daukar ta, taji ana tabata, ta yinkurin tashi amma ya danne ta, sai da yayi abinda ya kawo shi sannan ya tsallake yayi ficewar sa, ya barta da kuka me cin rai, ta tsani Adam ta tsani ko da jin sunan sa ne, haka ta tashi ta tsaftace jikin ta, sannan ta dawo ta kwanta amma sai ta nemi baccin da take ji ta rasa, tayi tayi amma sam yaki zuwa, tunani ta hau yi, ta saka wannan ta kwance wannan, ganin kwanciyar haka babu amfani sai kawai ta tashi ta dauro alwala ta raya daren, tana idarwa nan da nan bacci ya kwashe ta.
Da asubah ta farka kasan mararta na dan mata ciwo kad'an kad'an, har ta idar da sallah be daina ba, komawa tayi ta kwanta dan bata jin zata iya yin wani abu, kasala take ji sosai shiyasa har gari yayi sosai bata mike ba. Fitowa yayi ya nufi dinning din kamar yadda ya saba sai yaga wayam, haushi ne ya turnike shi dan yana sane jiya ya shigo da doya dan ita yake sha'awar ci yasan kuma in dai ta gani zata soya musu ita, yana matukar jin dadin abincin ta sosai shiyasa duk abinda yake baya taba yarda ya wuce shi, ji yayi ransa na sake baci, ya koma saman ya tura dakin sai ya tarar da ita a kwance a gado ya lulluba har kanta, yaye abun da ta rufar yayi, suka kalli juna
"Ina breakfast?" Yace yana tsaye kanta
"Babu." Tace kanta tsaye ta juya dayan side din, bankaro ta yayi ya juyo da ita
"Ya ina miki magana zaki juya min baya, uban wa ya saka ki fara abinda ba zaki iya dorewa ba, ko kinyi tunanin zaki sace zuciya ta da girkin ki ne?"
"Dan Allah Ya Adam ka rabu dani, ni na saka kaina nayi girkin kuma yau ban ba, ka kyale ni naji da abinda yake damuna dan Allah."
Tace cike da kosawa da halin sa
"Tashi zakiyi ki soya min doya kiyi min sauce, ina jiranki fita zanyi."
Tana jin sa ya juya ya fice, ta cigaba da kwanciya a wajen ciwon marar na karuwa sosai. Chan wajen minti talatin ya dawo dakin, ya tarar da ita a yarda ya barta, ransa idan yayi dubu ya baci, ya fizgota da karfi ta fado daga gadon, ya shiga kokarin neman abun da zai saka ya daketa. Tunawa yayi da belt din dake jikin wandon sa, ya hau kokarin ballo ta, tayi saurin rik'e hannun shi tuni har ta soma kuka sosai
"Dan Allah kayi hakuri wallahi bani da lafiya ne."
Be ji ta ba, bakar zuciyar shi ta riga ta ingiza shi, ya daddage ya zabga mata da karfin gaske, ta gantsare tana kwala karar azaba, idon sa ya rufe ruf, burin sa kawai yayi mata lilis yadda gobe ba zata sake ja dashi ba, baya son raini da wulakanci ba kuma zai dauka a wajenta ba, ita din da bata da maraba da takalmin sawar sa, wanda yake takawa ya wuce. Sau uku yana zabga mata, ta rarrafa da k'yar ta shige bayan gadon, biyo ta yayi ya sake dagawa yaji an rik'e belt din, daga nan yaji saukar mahaukacin mari a kuncin sa, kafin ya dawo hayyacin shi aka sake sauke masa wani me zafin gaske. Umar ne a tsaye yana huci sosai, sai Umma dake gefe tana kuka sosai, sakin belt din yayi ya fadi kasa, umar din ya shaki wuyan sa ya gwara kansa da bangon dakin.
"Kasheta zakayi? Kasheta zakayi? Wallahi kafin ka kasheta ni zan fara kasheka, shege dan iska mara mutunci." Ya sake kaiwa bakin sa naushi
"Umar zo ka daga ta, mu kaita asibiti kamar tayi bari." Umma tace tana kuka ta tallafo Asma'un jikin ta, sakin sa umar din yayi, babban yayan su Asma'un kenan, yana da masifar zuciya shi yasa baya shiga sabgar kowa, yanzu ma umma ce tazo gidan Hajiyan bayan ta aika da cingam din gayyatar bikin yar kanwar Baban su Adam din wadda ta taba rik'e ta kafin ta koma hannun iyayenta saboda Adam din, duk da Hajiyar bata sani ba, bikin ake shine aikin da su Asma'un suka yi jiya, tayin aikin umman tazo shine tace bari ta fara shigowa gidan Asma'un, sai kuma suka ji ihunta a sama, shine suka hawo da sauri suka tarar da bakin azzalumin yana dukan ta tamkar ya samu jaka.
Bari tayi kamar yadda Umman tayi tunani ganin jini, a asibitin aka kara tabbatar musu sannan aka ce suje suyi scanning a tabbatar ko ya gama fita duka. Daga nan kuma aka bata maganunguna suka wuce gida, gefen idon ta shatin duka ne inda Allah ne ya kiyaye be same ta a ido ba, ajiyar zuciya kawai take babu wanda yayi magana a cikin su, ran umma yayi masifar baci suna isa gida ta kira Abba a waya tace yazo gida babu lafiya, sai gashi nan da nan kuwa, ya tarar da Asma'un a kwance, fuskar ta da ta dan daga ya kalla a tsorace sai kuma ya kalli Umman,
"Gata nan, zuwa mukayi muka tarar da ita yana jibga kamar ya samu jaka, kalli idon ta, bayan ta ma shatin dukan sa ne."
"Duka?"
"Gashi nan ka duba ka gani ai idan baka yarda ba, ko ka kira Baba ai a gabansa akayi."
"Asma'u?" Ya kira sunan ta, ficewa umma tayi daga dakin dan hatta Abban haushin sa take ji sosai.
" Dukan ki adamu yayi wai? "
" Eh. " Ta gida kanta tana goge kwallar takaici
Shiru Abban yayi tamkar ruwa ya cinye shi, jiri jiri yaji yana neman kayar dashi, ya zauna da sauri yana dafe jikin kujerar
" Innalillah wa inna ilaihi rajiun. "
Yayi ta maimaitawa, har ya samu nutsuwa, ya dinga kallon ta tausayin ta na shigar sa sosai. Idan har namiji zai daga hannu ya daki mace, toh lallai ya kai makura a jahilci, be san abun na Adam din ya kai haka ba, be san mahaukaci bane na ajin karshe, waya ya dauka ya kira Ya Asabe, lokacin tana gidan Adam din an kira likita yana goge masa wajen da Umar ya fasa masa, tana ganin kiran Abban ta daga a zafafe
" Yanzu Karami har Umar yayi girman da zai shigo har gidan Adam ya dake shi haka, wacce irin tarbiyya ka bawa yaran nan ne,? Har cikin gidan kazo ka daki mutum saboda kana tunanin wani abu daban? "
" Adamu ya aiko wa Asma'u da takardar sakin ta, yau ba sai gobe ba, idan kuma yaki sai hukuma ta raba mu dashi!"
Yana kaiwa nan ya kashe wayar sa, saroro tayi da wayar a hannu, ta kalli Adam din ta kalli wayar, tana son sake tabbatar da Abban ne dai ya kirata ba wani ya bawa wayar ba, shi din ne dai yayi mata magana babu gaisuwa bare girmamawa!
RM
15
***Ajiye wayar yayi a kusa dashi ya karasa wajen Asma'un yana dubata,
"Tashi kinji."
Yace cikin tsananin tausayin ta, mikewa tayi zaune da k'yar har lokacin kanta na mata masifar ciwo, gefen idon ya dame ta sosai dan ya daga wajen.
"Ina hijab dinki? Zaki iya tafiya!?"
Girgiza wa Abban kai tayi saboda yadda take jin ta very weak, kamar zata fadi haka take ji.
"Ina zuwa." Ya fita yana kwala wa umma kira, ta taso tazo tana kin kallon sa
"Taimaka mata, ta saka Hijab dinta ku sameni a mota."
"Ba dai maida ita zakayi ya karasa kashe ta ba ko?"
Wani kallo yayi wa umman, yayi tsaki yace
"Kuyi sauri nace, ina jiranku."
Kada kai Umman tayi zuwa ciki shi kuma ya fita waje, taimaka mata tayi ta rik'e ta suka fito suka tarar dashi a mota Umar na zaune a mazaunin driver suna magana da Abban.
"Da ka sani ka karairaya shi ka zubar tunda be san mutunci ba."
Abban yace a maimakon tunanin da Umman tayi na zaiyi wa har Umar din fad'a, shiru umar din yayi bayan sun shigo, ya tada motar bayan ya kalli bayan cikin tausayin Asma'un.
"Asibiti zaka fara kaimu, kafin ka kaimu chan gidan tsoho."