Sashe 26
Rayuwar Mace Complete Hausa Novel · about 7 min read
***Dariya abun ya bawa umma, ita kadai ta dinga janjana maganar Asma'u na jinta taki fitowa, bata san Adam din ma bashi da kunya ba sai yau, ko kuma dai tsabar rainin wayo ne zai wanko kafafu yace wajen Asma'un yazo oho, aikuwa ta wanke shi tsaf dan dama ta jima tana jiran ranar duk da bata saka ran zuwan ta nan kusa ba. Wayar ta dake gefen ta, ta jawo ta kira Ya Hadiza ta bata labarin abinda ya faru, dan ta rasa wanda zasu zanta Asma'u tayi mata kirmisisi kamar bata ma san anayi ba, ita kanta Ya Hadizan sai da ta yaba kokarin Adam din ko tace tsantsar rashin ta ido da har zai iya zuwa kuma kai tsaye yace yana son magana da ita, duk da basu san maganar mece ba amma zuwan nasa kadai ya isa ka gane komai,sun jima suna magana kafin a kira sallar magriba sannan suka hakura.
Duk abinda ya faru Asma'un na ji amma bata da ta cewa, bata kawo zuwan nasa na da wani muhimmanci ba kamar yadda su umman suka zata dan ta riga ta san Adam baya da bukatar wani abu wajen ta dan bata cikin sahun mutanen da yake ganin su da kima da muhimmanci da har zai iya tako kafar sa yazo dan kawai yayi magana da ita, tafi tunanin dai ko yazo na ya kara jaddada mata tsanar da yayi mata ne, wanda idan ta samu damar haka tabbas sai ta sanar dashi yadda itama ta tsane shi, dan kaf duni babu mutumin da ta tsana kamar Adam din ba.
Suna cikin cin tuwon dare ne mijin Ya Hadiza yayi sallama, ita ta amsa masa ya shigo bayan umma ta yafa mayafin ta duk da babu wani haske sosai a tsakar gidan, gaisawa sukayi a mutunce dan shi mutum ne na gari ga kirki sosai sun saba da yan gidan kamar gidan su haka ya dauki su umma tamkar iyayen sa, su Abeed yazo dauka, umma tace ya tsaya a kawo masa tuwon, ba musu kuwa ya gyara zama Asma'u ta kawo masa, umma ta koma cikin falo ya kuwa ci tuwon sa sosai sannan ya kwashe su suka tafi. Suna tafiya Abba ya dawo tare da su Abbati da Umar da suka rakashi zariya daga nan suka tsaya kasuwa sukayi siyayyar kayan amfanin gidan. Dakin sa ya wuce kai tsaye Umar yaje ya kunna gen da Abba baya jure zafi ko kad'an. Bayan ya zauna ya nutsu ya huta sosai ne Asma'u ta shigo tambayar sa zuwa gidan Ya Hadizan da take son yi wanda Ya Hadizan ce da kanta ta roketa tazo ta kwana biyu dan idan ta itace tafi son zaman ta a gida akan ko ina, fuskar sa ce ta fad'ad'a da farin cikin ganin ta, ya amsa sallamar ta yana tsokanar ta
"Ma'u ce?"
"Nice Abba, sannu da hutawa."
"Yauwa sannu Asma'ul Husna."
"Yawwa."
"Akwai labari ne?" Yace yana matsar da plate din da yaci tuwo, tashi tayi da sauri ta kwashe ta matsar gefe ta saka tissue ta goge har miyar da ta zube sannan tace
"Abba dama so nake naje gidan su Abeed."
"Toh, wuni ko kwana?"
"Kwana Abba."
"Kin ganki ko? Har kwana nawa?"
Sai da ta boye fuskar ta a jikin kujerar da take kusa da ita sannan tace
"Sati daya."
"Umma kina jinta ko?"
"Wannan maganar ku ce, ba ruwana." Tace daga cikin daki, dariya kawai Abba yayi
"Shikenan, Allah ya bada sa'a, amma kar a wuce satin."
"In Sha Allah, nagode Abba."
"Allah yayi miki albarka."
" Amin ya Allah."
Tashi tayi ta fita, Abba ya bita da kallon tausayawa, shi dai kawai yana tausayin ta sosai, tayi masa biyayya hakan ya kara masa son ta sosai.
Sai a lokacin ya tuna ya ga missed call din Hajiya Mama, ya kirata a lokacin saboda suna hanya bata shiga ba, duba lokaci yayi yaga tara tayi har da yan mintuna, kiranta yayi bata dauka ba, sai ya ajiye wayar ya mike kafarsa ya chanja channel tv ya shiga kallon labarai.
Daki ta koma ta hada kayan da zata tafi dasu waje daya, ta gama ta kwanta ta dan danna wayarta kad'an zuwa goma ta kashe ta kwanta gaba daya. Da safe ta tashi da shirin tafiya, har umma na tsokanar ta akan ta matsu, dariya kawai tayi, ta gama duk ayyukan da take taya umman zuwa sha biyu bayan Abbati ya kai Abba kasuwa ya dawo ya dauke ta, Abba be yarda da fitar ta ita kadai ba shiyasa ma yasa Abbati din ya dawo ya kai ta, lokacin Ya Hadiza na kitchen suka zo, ta fito da sauri ta rungume Asma'un tana musu sannu da zuwa. Daki ta kai kayanta ta dawo suka baje a falon sai hira, tafi sakewa da ita akan kowa yanzu dan sosai take jan ta a jiki take kulawa da ita, shiyasa tasu tazo daya, tare suka gama abincin ranar Abbati yaci sannan ya koma kasuwa wajen Abba. Yaran basu dawo ba sai yamma likis tare suke hadawa harda islamiyya, da murna suka dane ta dan duk miskilancin ta, tana sakewa sosai da yara, ta iya tafi dasu shiyasa suke nanike mata.
***Tun da Oga Adam ya koma gida sai ya kasa aiwatar da komai, ya dinga jin kamar ana hadeshi waje daya ana daddaure shi, be san me yake ji ba kai tsaye, amma yasan ko menene yana da nasaba da Asma'u, dakin ta ya shiga, wanda yake kamar yadda ta barshi, kayan sawar ta da sauran tarkacen ta kawai suka dauka sauran kayan da Hajiya Maman ce ta zuba basu dau komai ba, gadon ya hau ya kwanta yana tuna wasu abubuwa dangane da ita, runtse idon sa yayi ya bud'e su, yana mikewa a kasalance ya sakko k'asa zuwa kitchen ya dauki ruwa ya sha har lokacin tana sake masa gizo a idon sa, wayarsa dake aljihun sa ce tayi kara, ya ciro ta yana kallon screen din
"Kana ina?"
"Ina gida."
"Ka shigo gidan ina son ganin ka."
" Owk. "
Yace ya kashe ya maida aljihun, maimakon ya je a lokcin sai ya sake komawa saman, ya watsa ruwa ya sauya kayan jikinsa sañnan ya shiga gidan nasu ya samu Maman tana waya, zama yayi ta gama sannan ta dube shi
"Za'a je garin su fiddausi neman aurenta."
Kirjinsa ne ya buga da karfi, sai a sannan ya tuna da wani maganar aure, ya rasa dalilin da ya saka Hajiyar damuwa da maganar, yadda tadage akan maganar auren ne zai baka mamaki, kamar bata san wace yarinya bace Fido din,yasan ba tuban gaskiya tayi ba, kawai dai akwai dalilin ta na kafewa sai ta aure shi, wanda shi akaran kansa be san dalilin menene ba.
"Nifa ba zan auri yarinyar nan ba."
"Aikuwa baka isa ba, aure kamar anyi an gama ne."
"Wai Mah kin fi son ta ne akaina? Ko ni yanzu bani da wani amfani."
"Oho, ban sani ba nima, aure ne dai babu fashi, ba zaka sake sani a wata masifar ba, karfin hali kawai nake ba wai Ina jin dadi bane, dan haka kar ma ka fara wata magana wallahi sai ka aureta sai dai idan mutuwa nayi."
Mikewa tayi ta bar shi a wajen a zaune tamkar wanda aka dasa, be san yaushe Hajiyan ta chanja masa haka ba, wanda a baya ita da kanta take bashi zabin duk abinda yake so, ta kuma mara masa baya dari bisa dari, amma be san dalilin da yasa yanzu ta kafe akan lallai sai ya auri Fido din ba, bayan ita da kanta ta san abinda ya hadu ba wai abu bane me kyau. Ita kanta Hajiyar sau tari tana mamakin yadda take jin sam ba zata taba iya nutsuwa ba har sai an daura auren, tamkar ana hura mata wuta haka take ji, shiyasa ta dage kai da fata ko da hakan na nufin shigar Adam din hali na daban ne.
*** Waya Faizan ta gama suka kwashe da dariya a tare suka tafa, Faiza tace
"Kin ga abinda nake fad'a miki ko!? Ai ba'a bori da sanyin jiki, maganin uwar kawai shine magana yanzu ba gashi nan ba komai na tafiya daidai, amma da ke kin dauki wata shawarar da ba zata bulle miki ba, hakan kuwa shine kawai maganin irin su, idan suka ki bi sai a biyad dasu, shima Adam din ki kyale shi zai gane bashi da wayo, sai ku zauna su gama daku sannan su ajiye ku su dauko masu kamun kai, ba zata sabu ba."
" Wallahi ni sam hankali na be dawo jiki na ba, sai da na samu labarin yarinyar da yaga min ihun baya so har da barin ciki tayi, ina rashin so anan?"
"Ke ya mayar gaula ai, ki zauna ki kare rayuwar ki a haka babu me kwasar ki, ko shi ba zai kwasa ba, bare wani."
"Haka ne wallahi, toh ba zata sabu ba wallahi."
" Ai da kin tsaya kallon ruwa."
" Ai na dawo hayyaci na wallahi, ko nawa zan kashe, akan na same shi, idan yaso duk abinda zai biyo baya wannan daga baya ne."
" Yawwa yar gari." Suka sake tafawa cike da jin dadin yadda abubuwan suke tafiya.
Duk abinda ya faru Asma'un na ji amma bata da ta cewa, bata kawo zuwan nasa na da wani muhimmanci ba kamar yadda su umman suka zata dan ta riga ta san Adam baya da bukatar wani abu wajen ta dan bata cikin sahun mutanen da yake ganin su da kima da muhimmanci da har zai iya tako kafar sa yazo dan kawai yayi magana da ita, tafi tunanin dai ko yazo na ya kara jaddada mata tsanar da yayi mata ne, wanda idan ta samu damar haka tabbas sai ta sanar dashi yadda itama ta tsane shi, dan kaf duni babu mutumin da ta tsana kamar Adam din ba.
Suna cikin cin tuwon dare ne mijin Ya Hadiza yayi sallama, ita ta amsa masa ya shigo bayan umma ta yafa mayafin ta duk da babu wani haske sosai a tsakar gidan, gaisawa sukayi a mutunce dan shi mutum ne na gari ga kirki sosai sun saba da yan gidan kamar gidan su haka ya dauki su umma tamkar iyayen sa, su Abeed yazo dauka, umma tace ya tsaya a kawo masa tuwon, ba musu kuwa ya gyara zama Asma'u ta kawo masa, umma ta koma cikin falo ya kuwa ci tuwon sa sosai sannan ya kwashe su suka tafi. Suna tafiya Abba ya dawo tare da su Abbati da Umar da suka rakashi zariya daga nan suka tsaya kasuwa sukayi siyayyar kayan amfanin gidan. Dakin sa ya wuce kai tsaye Umar yaje ya kunna gen da Abba baya jure zafi ko kad'an. Bayan ya zauna ya nutsu ya huta sosai ne Asma'u ta shigo tambayar sa zuwa gidan Ya Hadizan da take son yi wanda Ya Hadizan ce da kanta ta roketa tazo ta kwana biyu dan idan ta itace tafi son zaman ta a gida akan ko ina, fuskar sa ce ta fad'ad'a da farin cikin ganin ta, ya amsa sallamar ta yana tsokanar ta
"Ma'u ce?"
"Nice Abba, sannu da hutawa."
"Yauwa sannu Asma'ul Husna."
"Yawwa."
"Akwai labari ne?" Yace yana matsar da plate din da yaci tuwo, tashi tayi da sauri ta kwashe ta matsar gefe ta saka tissue ta goge har miyar da ta zube sannan tace
"Abba dama so nake naje gidan su Abeed."
"Toh, wuni ko kwana?"
"Kwana Abba."
"Kin ganki ko? Har kwana nawa?"
Sai da ta boye fuskar ta a jikin kujerar da take kusa da ita sannan tace
"Sati daya."
"Umma kina jinta ko?"
"Wannan maganar ku ce, ba ruwana." Tace daga cikin daki, dariya kawai Abba yayi
"Shikenan, Allah ya bada sa'a, amma kar a wuce satin."
"In Sha Allah, nagode Abba."
"Allah yayi miki albarka."
" Amin ya Allah."
Tashi tayi ta fita, Abba ya bita da kallon tausayawa, shi dai kawai yana tausayin ta sosai, tayi masa biyayya hakan ya kara masa son ta sosai.
Sai a lokacin ya tuna ya ga missed call din Hajiya Mama, ya kirata a lokacin saboda suna hanya bata shiga ba, duba lokaci yayi yaga tara tayi har da yan mintuna, kiranta yayi bata dauka ba, sai ya ajiye wayar ya mike kafarsa ya chanja channel tv ya shiga kallon labarai.
Daki ta koma ta hada kayan da zata tafi dasu waje daya, ta gama ta kwanta ta dan danna wayarta kad'an zuwa goma ta kashe ta kwanta gaba daya. Da safe ta tashi da shirin tafiya, har umma na tsokanar ta akan ta matsu, dariya kawai tayi, ta gama duk ayyukan da take taya umman zuwa sha biyu bayan Abbati ya kai Abba kasuwa ya dawo ya dauke ta, Abba be yarda da fitar ta ita kadai ba shiyasa ma yasa Abbati din ya dawo ya kai ta, lokacin Ya Hadiza na kitchen suka zo, ta fito da sauri ta rungume Asma'un tana musu sannu da zuwa. Daki ta kai kayanta ta dawo suka baje a falon sai hira, tafi sakewa da ita akan kowa yanzu dan sosai take jan ta a jiki take kulawa da ita, shiyasa tasu tazo daya, tare suka gama abincin ranar Abbati yaci sannan ya koma kasuwa wajen Abba. Yaran basu dawo ba sai yamma likis tare suke hadawa harda islamiyya, da murna suka dane ta dan duk miskilancin ta, tana sakewa sosai da yara, ta iya tafi dasu shiyasa suke nanike mata.
***Tun da Oga Adam ya koma gida sai ya kasa aiwatar da komai, ya dinga jin kamar ana hadeshi waje daya ana daddaure shi, be san me yake ji ba kai tsaye, amma yasan ko menene yana da nasaba da Asma'u, dakin ta ya shiga, wanda yake kamar yadda ta barshi, kayan sawar ta da sauran tarkacen ta kawai suka dauka sauran kayan da Hajiya Maman ce ta zuba basu dau komai ba, gadon ya hau ya kwanta yana tuna wasu abubuwa dangane da ita, runtse idon sa yayi ya bud'e su, yana mikewa a kasalance ya sakko k'asa zuwa kitchen ya dauki ruwa ya sha har lokacin tana sake masa gizo a idon sa, wayarsa dake aljihun sa ce tayi kara, ya ciro ta yana kallon screen din
"Kana ina?"
"Ina gida."
"Ka shigo gidan ina son ganin ka."
" Owk. "
Yace ya kashe ya maida aljihun, maimakon ya je a lokcin sai ya sake komawa saman, ya watsa ruwa ya sauya kayan jikinsa sañnan ya shiga gidan nasu ya samu Maman tana waya, zama yayi ta gama sannan ta dube shi
"Za'a je garin su fiddausi neman aurenta."
Kirjinsa ne ya buga da karfi, sai a sannan ya tuna da wani maganar aure, ya rasa dalilin da ya saka Hajiyar damuwa da maganar, yadda tadage akan maganar auren ne zai baka mamaki, kamar bata san wace yarinya bace Fido din,yasan ba tuban gaskiya tayi ba, kawai dai akwai dalilin ta na kafewa sai ta aure shi, wanda shi akaran kansa be san dalilin menene ba.
"Nifa ba zan auri yarinyar nan ba."
"Aikuwa baka isa ba, aure kamar anyi an gama ne."
"Wai Mah kin fi son ta ne akaina? Ko ni yanzu bani da wani amfani."
"Oho, ban sani ba nima, aure ne dai babu fashi, ba zaka sake sani a wata masifar ba, karfin hali kawai nake ba wai Ina jin dadi bane, dan haka kar ma ka fara wata magana wallahi sai ka aureta sai dai idan mutuwa nayi."
Mikewa tayi ta bar shi a wajen a zaune tamkar wanda aka dasa, be san yaushe Hajiyan ta chanja masa haka ba, wanda a baya ita da kanta take bashi zabin duk abinda yake so, ta kuma mara masa baya dari bisa dari, amma be san dalilin da yasa yanzu ta kafe akan lallai sai ya auri Fido din ba, bayan ita da kanta ta san abinda ya hadu ba wai abu bane me kyau. Ita kanta Hajiyar sau tari tana mamakin yadda take jin sam ba zata taba iya nutsuwa ba har sai an daura auren, tamkar ana hura mata wuta haka take ji, shiyasa ta dage kai da fata ko da hakan na nufin shigar Adam din hali na daban ne.
*** Waya Faizan ta gama suka kwashe da dariya a tare suka tafa, Faiza tace
"Kin ga abinda nake fad'a miki ko!? Ai ba'a bori da sanyin jiki, maganin uwar kawai shine magana yanzu ba gashi nan ba komai na tafiya daidai, amma da ke kin dauki wata shawarar da ba zata bulle miki ba, hakan kuwa shine kawai maganin irin su, idan suka ki bi sai a biyad dasu, shima Adam din ki kyale shi zai gane bashi da wayo, sai ku zauna su gama daku sannan su ajiye ku su dauko masu kamun kai, ba zata sabu ba."
" Wallahi ni sam hankali na be dawo jiki na ba, sai da na samu labarin yarinyar da yaga min ihun baya so har da barin ciki tayi, ina rashin so anan?"
"Ke ya mayar gaula ai, ki zauna ki kare rayuwar ki a haka babu me kwasar ki, ko shi ba zai kwasa ba, bare wani."
"Haka ne wallahi, toh ba zata sabu ba wallahi."
" Ai da kin tsaya kallon ruwa."
" Ai na dawo hayyaci na wallahi, ko nawa zan kashe, akan na same shi, idan yaso duk abinda zai biyo baya wannan daga baya ne."
" Yawwa yar gari." Suka sake tafawa cike da jin dadin yadda abubuwan suke tafiya.