← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 98 OF 155

Sashe 98

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

    ★★

  Tarba suka samu maiban mamaki daga mmn sadiq da maman halima. ashe hajiya iya ta sanar musu da zuwan nasu, shiyyasa mmn sadiq datai niyyar zuwa dubata yau dole ta haƙura. Zinneerah kam ai tuni ta faɗa jikin mmn sadig tana murnar ganinta ita da mmn halima. hakan datai har sai da ya bama AK mamaki dan baiyi zatonta hakaba. Kasancewar Abba na gida yana jiransu a falonsa aka sauke AK, su Hajiya iya kuwa da mmn sadiq keji kamar ta goya suna a sashenta.
        Duk yanda mmn sakina taso nuna halin nata garesu saita kasa. Dan wani cika mata ido sukai dole ta kama kanta harda zuwa ɗakin mmn sadiq gaishesu. Ai kam sun amsa mata da fara'a da mutuntawa, hakan da sukai kuma sai ya ƙara musu kima a idonta da shakka. Mmn halima ma cike da girmamawa tazo ta gaidasu, Hajiya iya nata sanya mata albarka dan bata manta da fuskartaba taje mata gaiauwar Inno.
        Saboda zuwa nan hajiya iya dama taƙi cin abinci, dan ta taho da shirin cin abincin gidan ɗiyar tata. Aiko taji daɗin samun masa da mmn sadiq tai musu, sai gashi daga ita har Mommy sunci sosai suna godiya. hakan yasa Mmn sadiq ƙara jin daɗi da nutsuwa. Dan koba komai ai sun bata kimarta. Zinneerah kam tuni tana sashen mmn halima ta barsu dan su sake da kuma kasancewarsu manya a gareta.
    Da wannan damar mmn sadiq da baƙinta sukai hirar zuminci da tattaunawa game da labarin da Zinneerah ta bama hajiya iya da kuma abinda ya faru akan zancen little da maganar ɗaurin aurenta. Harma da shirye-shiryen tariya da a take mommy ta tabatar musu ita ta gama shirya komai rana kawai suke jira insha ALLAHU.
    Hawaye sosai mmn sadiq keyi har sai da hajiya iya ta shiga lallashinta.
     Sai da akai sallar la'asar Abba ya shigo gaida su hajiya iya tare da AK da shima yaci masa sosai dan yana sonta, ya kuma sha zoɓo shima. Sun gaisa cikin mutunta juna, suka ɗan ƙara tattaunawa har zuwa kusan biyar da rabi sannan sukai haramar tafiya.
    Sai kuma ga Zinneerah tai ƙwalkwal da idanu na kewar hajiya iya da zatayi duk da dai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zata koma. Sau biyu suna haɗa ido da AK da tuni ya shige mota ta mirror ɗin waje, daga ƙarshe dai ta matsa daga saitinsa tana ɗaga musu hannu.

    Tafiyarsu da mintuna basufi talatinba su Sadiq suka dawo gida. Ganin Zinneerah suka haukace da murna suna tambayarya ina little ɗinsu?, su dai sunyi kewarsa dan ALLAH a dawo musu da abinsu. Dariya kawai take musu dan ita dai wannan ba huruminta baneba ai. Tunda batasan yaje canba itama ganinsa tayi.
     Bata samu zama da mahaifiyartaba sai dare bayan yaran sunyi barci, kasancewar ɗakin mmn sadiq ɗin zata kwana suka sami damar yin hira, yayinda mmn sadiq ketama ƴar tata nasiha a kaikaice akan aure da muhimmancinsa da darajojinsa. Ita dai Zinneerah saurarenta kawai takeyi bawai fahimtar dalilin yinsuba. Sai dai suna shiga kwakwalwarta tana kuma ƙoƙarin adanawa da fatan yin aiki dasu a duk sanda ƙaddara ta tilasta mata yin aure dan bata kawosa a lissafinta sam. ita kullum lissafi da budget ɗinta akan karatune mai zurfi kawai.
     Washe gari ma bayan tafiyar su Abdul skull sake zaman hira tayi da mamanta. A yau ɗinma hirar ta kasance kusan duk nasiha da dabarun zaman gidan aure koda da kishiya. Harma dai takai abin ya fara bama Zinneerah mamaki amma saita danne a ranta kawai.

     Karfe huɗu dai-dai sai ga Ni'ima da driver sunzo ɗaukarta, jitai kamar ta fasa kuka. Amma jin mmn sadiq tace zasuje taron biki Danya kuma harda ita nanda kwanaki tara yasa taɗanji daɗi a ranta har fuskarta ta nuna. Bayan ta gama matse-matsen hawayenta ta shirya suka wuce ɗauke da madaidaicin botikin gullisuwa da mmn sadiq ɗin tai musu.
          Koda suka iso gidan cike da murna suka tari juna dasu Bahijja daketa mata ƙorafin basusan zataje wajen mama ba da sun bita. dan sai da su Mommy suka dawo suka sani. Haƙuri ta basu kawai, daga haka suka shiga hidimar cin gwullisuwa kuma.

         Ana idar da sallar magrib hajiya iya tai baƙuwa. Bayan sun shiga ɗaki kusan awa ɗaya aka kira Zinneerah, kai tsaye hajiya iya tace mata ta shirya zasu tafi da baƙuwar gidanta. Mamaki ya kama Zinneerah, amma ganin yanda hajiya iya ta fiske dole itama ta shanye mamakin nata.
     Bayan ta shirya Hajiya iya ta jata gefe tai mata ƴar nasiha da gargaɗin duk abinda akai mata a inda zataje kartai jayayya, karkuma tai wasa wajen koyon komai ɗin. Ta amsama hajiya iya da girmamawa ita dai tana matsar ƙwalla, dan hankalinta ya tashi jin wai sati ɗaya zatai acan, a hakanma hajiya fadi take waje ya ƙure ba haka tasoba.

      Zinneerah naji na gani ta tafi tabar su Meenal tana hawaye suma sunayi tamkar masu rabuwa har abada. Hajiya iya kanta sai da taji kewarta, to amma wannan shine kawai gatan da zatai mata ta miƙata wajen kwararrun mata ta fannin sanin gyaran jiki da wasu sirrika irin su hajiya Falmata su gyara mata ƴar jikallen tata. Dan idan tai dubi da abinda ya faru da kuma kishiya irin Farah saita ƙara jin wannan shine gatan.

      Koda suka iso gidan hajiya falmata bata tsaya sanyaba saboda gargaɗi da sharuɗɗan hajiya iya akan irin salon gyaran da take buƙata aima Zinneerah ɗin, itako hajiya falmata dama aikinta kawai ta sani batasan wasaba. Musamman ma aiki irin wannan na manyan mutane kamar su hajiya iya da suke alaƙa tun zamanin ƙuruciya ba abinda zatai sanya bane. Dan haka tun a ranar ta fara gyara Zinneerah daga isowarsu gidan ko hutawa batama bari sunyi zaman yiba. Tun Zinneerah na kallon abin wani iri hardai ta fara jin yana shiga jikinta da sha'awarsa ganin yanda ta fara canjawa da ƙamshi mai kama jiki da gogewar fata a cikin kwana biyu.
       Babu abinda ke damunta sai kewarsu Jamal da hajiya iya dan ko abinci da ake bata na musamman ne. Hajiya Falmata kuwa nata aikinta da koya mata abubuwa kai tsaye har kunya na neman kashe Zinneerah da ganin hajiya falmata zata iskantar da ita shekarunta basu kai ba. A ranta kuma tana mamaki yanda ake mata magana mai kama da harshen damo akan aure da zamantakewarsa. Ta rasa wannan dalili itakam, takumayi alwashin bazata tambayaba zata cigaba dabi da ido da kuma saurare.

      A Ɓangaren su Hajiya iya kuwa Zinneerah na barin gidan aka ware fara tsare-tsaren biki da maganar invitations dan hajiya iya da Baffah fa shiri suke gagarumi kodan ƙular dasu Mammah dake can hotel suna jiran tsammani daga mai bincike, AK kuwa daketa ƙoƙari akan aikin shinkafarsa yana sane dasu, dan tuni yasa aka bincika masa inda suke, ya kuma shirya ɗaukar mataki akan Farah data bijirema maganarsa.
     Akan gyaran gidansa kuwa Dr Mahmud da Huzaifa ne tsaye akai duk da gidan bama taɓa zamansa Farah tayiba. Garamashi yankan zauna lokacin da yake shigowa ƙasar a munafunce.
     Ranar da Zinneerah ta cika kwanaki huɗu wajen Hajiya falmata lefen da Momie ta haɗa gudunmawarta ya iso, sai kuma ga Adilah da Mahma daga london suma sun iso da nasu kayan lefen, dan AK na sanar da ita komai bai ɓoyeba, takuma bashi goyon baya ɗari bisa ɗari.
     Zokaga yanda Adilah ke murna da farin cikin kasancewarta cikin ƴan uwa. mahma kuwa abinci kawai taci anan taɗan huta ta nema inda su Mammah suke, dan bata son ita kanta su san da maganar auren har sai ranar tariyar insha ALLAHU..............✍

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 48*

__________________________

Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu
Sannan munada beauty kit🤗duk me bukatan (flawless skin/perfect glow) toh yy kokari yamallaki set dinnan wn zncn baa mgn🧚🏻‍♀️cuz duk inda kayi se ankalleka😀
Buh gsky wnd besan yy haske karyayi using set din cuz gsky yn sa haske buh bn bleaching ne b zaidai murje fatane nd bring out that hidden beauty in you😍
Chapter 98 · 0% Book details