Sashe 47
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
_KAMAR SU: Kitchen utensils_
_Fabrics_
_Shoes nd bag_
_Phones_
_Veils_
_Children's wears_
_Furnitures_
_Dubai, china, India, turkey, Malaysia_
_MUNA GARIN: Kano, Unguwar hotoro_
_Facebook handle d’inmu: Maryam muhd_
_Lambar tarhon mu: 07014488636_
_________________
*Page 21*
...........Khalipha kam da zuciyarsa tayi matuƙar nisa a cikin tunani sam baiji mi yayan nasuma ya faɗaba. Yaɗan ɗago ya dubi Moos'ab ɗin kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana binsu da kallon mamaki su duka ganin yanda duk suka sake nutsuwa. Sashen da yayansu yake ya maida kallonsa, sai yaga hankalinsama baya kan kowannensu.
Maida kansa kawai yayi ga abincinsa shima, sai dai gaba ɗaya hankalinsa ya tafine ga tunanin sake son ganin yarinyar ɗazu da sukace sunanta Zinneerah.
Har aka kammala breakfast ɗin babu wanda ya ƙara ƙwaƙwaran motsi. Shine ya fara tashi a dining ɗin, suka bishi da kallo harya shige ɗakinsa. Tamkar jira suke yabar wajen suka fara ƙus-ƙus na gulma.
“ALLAH ya baku sa'a ya fito ya jiku”. Khalipha ya faɗa yana miƙewa shima ɗauke da kofin shayi ya nufi ɗakin Hajiya Iya. Zaune take a gaban gadon saman carpet ɗin dake a malale, ta mimmiƙe ƙafafunta dake mata zugi, dan ciwon da suke matannema ya hanata zama cin abinci a dining ɗin yau.
Fuska ɗauke da murmushi take duban Khalipha. Ya zauna a kusa da ita yana ajiye kofin ya amshi man zafin ya fara shafa mata. “Moddibo fa?”. Hajiya iya ta tambaya tana kallon Khalipha.
Ya buɗe baki zai bata amsa sallamarsa ta katsesa. Duk suka kalli ƙofar dai-dai yana ziro ƙafarsa ciki. Kallonsu yay ya kauda kai, sai da ya shigo ciki sosai yakai zaune a bakin gadon dai-dai ƙafafun Zinneerah dake ƙudindine a bargo sannan yace, “Ciwo ƙafan yake ne?”.
“Ba wani da yawa bane ai. Yanzuma zakaga ta saki tunda Khalipha ya daddana min ita”.
Kansa ya maida ga wayarsa dake haske alamar kira ake batare da yace komaiba.
“Fita zakayine Yayanmu?”. Khalipha ya faɗa yana kallonsa.
Kansa ya girgiza masa da faɗin, “No, Phones ɗin yaran nan ne”.
“Woow, autoci an shigo gari kenan”. Khalipha yay maganar yana jawo ƙyaƙyƙyawar ledar gabansa. Kwalayen wayoyi masu ƙyau da tsada guda shidda ya fiddo a ciki. Ya miƙama Hajiya Iya. “Granny ga wayoyin jikokinki Yayanmu ya cika alƙawari”.
Murmushi tayi a karan farko da miƙa hannu ta amsa ɗaya tana kallo. “A to lallai munyi rabin shiri da ja'irin nan yau. ALLAH ya saka da alkairi ya bada ladan zuminci”.
Da amin suka amsa shi da Khalipha. Hajiya iya tace, “To ga kuma Zinneerah ta ƙaru, sai itama kasan yanda zakai da ita, dan ba'a basu wayoyiba ita batada ita”.
Kamar bazai tankaba sai kuma ya ɗan dubi Hajiya Iyan. “Tunda bansan tana a gidanba sai tai haƙuri sai wani karon”.
“A'a bazai yuwuba gaskiya Moddibo. A duba mata dai ko anan ita sai a saya mata”.
Shiru yay bai sake tankawaba duk da sarai yaji mi Hajiya iyan ta faɗa. Sanin halinsa yasa Khalipha saurin faɗin, “A'a Granny a bar Yayanmu ya huta. insha ALLAH ni saina saya mata kawai”.
Hajiya Iya tace, “To shikenan hakanma yayi ALLAH ya saka muku da alkairi. ya ƙara haɗemin kanku”.
Khalipha ne kawai ya amsa da amin. Shiko laɓɓansa kawai yaɗan motsa kaɗan alamar ya amsa ɗin.
Daga Haka Khalipha da Hajiya Iya suka cigaba da hira, shiko yana saurarensune kawai amma baya saka baki sai yaso, yama maida hankalinsa gaba ɗaya akan latsa waya.
Zinneerah da tun shigowar Khalipha ɗakin ta farka taɗan motsa kafarta, jin ta dunguri abu yasata saurin matsarwa baya tana rintse ido. Hakanne ya sakashi ɗan juyawa ya kalli abinda ke bayan nasa duk da tun shigowarsa yaga alamar mutumne kwance. Kamar zaiyi magana sai kuma ya miƙe yana tura wayarsa a aljihun wandon 3quarter ɗinsa. “Ni bara naje zanyi magana da Baffah, zuwa anjima inason zuwa Jigawa”.
“Jigawa kuma? Yin me?”.
Duban Hajiya iya mai maganar yayi, yaɗan kai yatsa gefen idonsa ya sosa kaɗan da cewar, “Akwai wani gona ne da nakeson yin noman shinkafa. So mun gama magana da Mahmud shine nakeson dubawa”.
“Tofa, bana kuma nan aka tsallaka kenan? Kai dai duk hanyar neman kuɗi kasanta Moddibo. Kana gudunmu kuma kana son zuwa kaci arziƙin ƙasarmu”.
“Tunda ni ba ƙasata baceba ko. Idan wannan mai barcin ta tashi taje ta gyaramin ɗaki”. Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin abinsa.
Harara Hajiya iya ta raka bayansa da shi tana yamutsa fuska. “Bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.
A yanda tai maganarne ya tilasta Khalipha ƙyalƙyalewa da dariya shima yana miƙewar. “Granny rigima. show ɗinki da Yayanmu nada matuƙar ƙayatarwa ga mai kallo. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani uwargida kuma amaryar Abdul-Mutallab Shira”.
“Oh to, ko kanamin baƙin cikine ba'a taɓamin kishiyaba?”.
“Wah? Ni? Rufamin asiri Granny karkisa Baffah yaji ya zagemin uwa. Kinga nayinan raba tsaraba na samo tukuyci. Itama ya kamata ta tashi ta karya”. Ya nuna Zinneerah da duk tana jinsu amma ta lafe.
“Eh nima yanzu nake tunanin nan a raina. Barama naji jikin nata kodai batajin daɗine, dan bata saba irin wannan barcinba sam”.
“Okay to bara naje na dawo sai naji wane hali take ciki”. Daga haka ya fice a ɗakin.
Ihun murnar waya da su Meenal suka shigo ɗakin sunayi ya tilasta Zinneerah tashi. A take suka kaure ɗakin da sabon ihu. Koda Hajiya iya data shiga bayi ta fito tana musu maganar su fice sun dameta a guje suka fita kuwa suna cigaba da ihunsu. Acan harabar gidan suka iske su Abidah suma suna nasu tsallen murnar dan da gaske yayan nasu ya shigo dasu gari da masu zafi kam.
Duk da babu Zinneerah a cikin masu wayar babu damuwa ko ɗigon sisi tattare da ita, hasalima itace mai farke wayoyin su Bahijja daga cikin kwalinsun. Da ƙyar hajiya iya ta tilastata zama cin abinci. tana gamawa kuma taje tai gyaran ɗakin nasa daya faɗa kamar yanda Hajiya iya ta sanar mata saƙon duk da itama taji da kunnenta.
Koda ta kammala taje tai wanka fitowa tai suka ɗora shirmensu daga inda suka tsaya ita da su Jamal. A haka Khalipha ya shigo ya samesu, daga asibiti yake yin bincike akan Zinneerah da suka haɗu wancan karon, dan gaba ɗaya zuciyarsa ta kasa yarda cewa wannan ɗin itace waccan Zinneerah ɗin. Gadai satar kammani sunayi da juna. Amma kuma wayewar kai da wasu abubuwa da yawa ya banbantasu. Babbar matsalar daya samu na rasa Number Naziru da yayi sakamakon wani tsautsayi daya samesa acan London. Yanzu kuma yaje asibitinma a iya binciken da yayi bai samu wani bakin zaren da zai iya nemansu ba. Amma an tabbatar masa ta haihu baby boy.
Gida ya dawo da sabon tunani akan tunkarar wannan Zinneerah ɗin yaji daga gareta ita kuma, dan a tunaninsa da ace waccan ɗince data ganesa. To waccanma ai matar aurece miyasa zaiyi tunanin itace anan?.
Ruwa Meenal ta kawo masa ya sha. Ya kumace ta haɗa masa abinci a dining zaije yay wanka ya dawo. Binsa Zinneerah tai da kallo a cikin wani irin bahagon yanayi. Cikin dabara takai hannu ta share ƙwallar da suka ciko mata idanu. A yanzu haka babu abinda kecin ranta da damuwarta sai yanda Khalipha ya nuna tamkar baima taɓa sanintaba. Bayan ita tunda ya barta bata taɓa hutawa da tunaninsaba a ranta. har mafarkinsa tasha yi ma. Amma insha ALLAH zata daure itama ta kama kanta gareshi, idan ya ganota fine. idan ya cigaba da pretending ɗin rashin sanin nata itama saita samawa kanta lafiya ai. Da wannan tunani ta cigaba da hidimarta har lokacin Islamiyya yayi suka fita.
*_DANYA_*
_Fabrics_
_Shoes nd bag_
_Phones_
_Veils_
_Children's wears_
_Furnitures_
_Dubai, china, India, turkey, Malaysia_
_MUNA GARIN: Kano, Unguwar hotoro_
_Facebook handle d’inmu: Maryam muhd_
_Lambar tarhon mu: 07014488636_
_________________
*Page 21*
...........Khalipha kam da zuciyarsa tayi matuƙar nisa a cikin tunani sam baiji mi yayan nasuma ya faɗaba. Yaɗan ɗago ya dubi Moos'ab ɗin kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana binsu da kallon mamaki su duka ganin yanda duk suka sake nutsuwa. Sashen da yayansu yake ya maida kallonsa, sai yaga hankalinsama baya kan kowannensu.
Maida kansa kawai yayi ga abincinsa shima, sai dai gaba ɗaya hankalinsa ya tafine ga tunanin sake son ganin yarinyar ɗazu da sukace sunanta Zinneerah.
Har aka kammala breakfast ɗin babu wanda ya ƙara ƙwaƙwaran motsi. Shine ya fara tashi a dining ɗin, suka bishi da kallo harya shige ɗakinsa. Tamkar jira suke yabar wajen suka fara ƙus-ƙus na gulma.
“ALLAH ya baku sa'a ya fito ya jiku”. Khalipha ya faɗa yana miƙewa shima ɗauke da kofin shayi ya nufi ɗakin Hajiya Iya. Zaune take a gaban gadon saman carpet ɗin dake a malale, ta mimmiƙe ƙafafunta dake mata zugi, dan ciwon da suke matannema ya hanata zama cin abinci a dining ɗin yau.
Fuska ɗauke da murmushi take duban Khalipha. Ya zauna a kusa da ita yana ajiye kofin ya amshi man zafin ya fara shafa mata. “Moddibo fa?”. Hajiya iya ta tambaya tana kallon Khalipha.
Ya buɗe baki zai bata amsa sallamarsa ta katsesa. Duk suka kalli ƙofar dai-dai yana ziro ƙafarsa ciki. Kallonsu yay ya kauda kai, sai da ya shigo ciki sosai yakai zaune a bakin gadon dai-dai ƙafafun Zinneerah dake ƙudindine a bargo sannan yace, “Ciwo ƙafan yake ne?”.
“Ba wani da yawa bane ai. Yanzuma zakaga ta saki tunda Khalipha ya daddana min ita”.
Kansa ya maida ga wayarsa dake haske alamar kira ake batare da yace komaiba.
“Fita zakayine Yayanmu?”. Khalipha ya faɗa yana kallonsa.
Kansa ya girgiza masa da faɗin, “No, Phones ɗin yaran nan ne”.
“Woow, autoci an shigo gari kenan”. Khalipha yay maganar yana jawo ƙyaƙyƙyawar ledar gabansa. Kwalayen wayoyi masu ƙyau da tsada guda shidda ya fiddo a ciki. Ya miƙama Hajiya Iya. “Granny ga wayoyin jikokinki Yayanmu ya cika alƙawari”.
Murmushi tayi a karan farko da miƙa hannu ta amsa ɗaya tana kallo. “A to lallai munyi rabin shiri da ja'irin nan yau. ALLAH ya saka da alkairi ya bada ladan zuminci”.
Da amin suka amsa shi da Khalipha. Hajiya iya tace, “To ga kuma Zinneerah ta ƙaru, sai itama kasan yanda zakai da ita, dan ba'a basu wayoyiba ita batada ita”.
Kamar bazai tankaba sai kuma ya ɗan dubi Hajiya Iyan. “Tunda bansan tana a gidanba sai tai haƙuri sai wani karon”.
“A'a bazai yuwuba gaskiya Moddibo. A duba mata dai ko anan ita sai a saya mata”.
Shiru yay bai sake tankawaba duk da sarai yaji mi Hajiya iyan ta faɗa. Sanin halinsa yasa Khalipha saurin faɗin, “A'a Granny a bar Yayanmu ya huta. insha ALLAH ni saina saya mata kawai”.
Hajiya Iya tace, “To shikenan hakanma yayi ALLAH ya saka muku da alkairi. ya ƙara haɗemin kanku”.
Khalipha ne kawai ya amsa da amin. Shiko laɓɓansa kawai yaɗan motsa kaɗan alamar ya amsa ɗin.
Daga Haka Khalipha da Hajiya Iya suka cigaba da hira, shiko yana saurarensune kawai amma baya saka baki sai yaso, yama maida hankalinsa gaba ɗaya akan latsa waya.
Zinneerah da tun shigowar Khalipha ɗakin ta farka taɗan motsa kafarta, jin ta dunguri abu yasata saurin matsarwa baya tana rintse ido. Hakanne ya sakashi ɗan juyawa ya kalli abinda ke bayan nasa duk da tun shigowarsa yaga alamar mutumne kwance. Kamar zaiyi magana sai kuma ya miƙe yana tura wayarsa a aljihun wandon 3quarter ɗinsa. “Ni bara naje zanyi magana da Baffah, zuwa anjima inason zuwa Jigawa”.
“Jigawa kuma? Yin me?”.
Duban Hajiya iya mai maganar yayi, yaɗan kai yatsa gefen idonsa ya sosa kaɗan da cewar, “Akwai wani gona ne da nakeson yin noman shinkafa. So mun gama magana da Mahmud shine nakeson dubawa”.
“Tofa, bana kuma nan aka tsallaka kenan? Kai dai duk hanyar neman kuɗi kasanta Moddibo. Kana gudunmu kuma kana son zuwa kaci arziƙin ƙasarmu”.
“Tunda ni ba ƙasata baceba ko. Idan wannan mai barcin ta tashi taje ta gyaramin ɗaki”. Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin abinsa.
Harara Hajiya iya ta raka bayansa da shi tana yamutsa fuska. “Bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.
A yanda tai maganarne ya tilasta Khalipha ƙyalƙyalewa da dariya shima yana miƙewar. “Granny rigima. show ɗinki da Yayanmu nada matuƙar ƙayatarwa ga mai kallo. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani uwargida kuma amaryar Abdul-Mutallab Shira”.
“Oh to, ko kanamin baƙin cikine ba'a taɓamin kishiyaba?”.
“Wah? Ni? Rufamin asiri Granny karkisa Baffah yaji ya zagemin uwa. Kinga nayinan raba tsaraba na samo tukuyci. Itama ya kamata ta tashi ta karya”. Ya nuna Zinneerah da duk tana jinsu amma ta lafe.
“Eh nima yanzu nake tunanin nan a raina. Barama naji jikin nata kodai batajin daɗine, dan bata saba irin wannan barcinba sam”.
“Okay to bara naje na dawo sai naji wane hali take ciki”. Daga haka ya fice a ɗakin.
Ihun murnar waya da su Meenal suka shigo ɗakin sunayi ya tilasta Zinneerah tashi. A take suka kaure ɗakin da sabon ihu. Koda Hajiya iya data shiga bayi ta fito tana musu maganar su fice sun dameta a guje suka fita kuwa suna cigaba da ihunsu. Acan harabar gidan suka iske su Abidah suma suna nasu tsallen murnar dan da gaske yayan nasu ya shigo dasu gari da masu zafi kam.
Duk da babu Zinneerah a cikin masu wayar babu damuwa ko ɗigon sisi tattare da ita, hasalima itace mai farke wayoyin su Bahijja daga cikin kwalinsun. Da ƙyar hajiya iya ta tilastata zama cin abinci. tana gamawa kuma taje tai gyaran ɗakin nasa daya faɗa kamar yanda Hajiya iya ta sanar mata saƙon duk da itama taji da kunnenta.
Koda ta kammala taje tai wanka fitowa tai suka ɗora shirmensu daga inda suka tsaya ita da su Jamal. A haka Khalipha ya shigo ya samesu, daga asibiti yake yin bincike akan Zinneerah da suka haɗu wancan karon, dan gaba ɗaya zuciyarsa ta kasa yarda cewa wannan ɗin itace waccan Zinneerah ɗin. Gadai satar kammani sunayi da juna. Amma kuma wayewar kai da wasu abubuwa da yawa ya banbantasu. Babbar matsalar daya samu na rasa Number Naziru da yayi sakamakon wani tsautsayi daya samesa acan London. Yanzu kuma yaje asibitinma a iya binciken da yayi bai samu wani bakin zaren da zai iya nemansu ba. Amma an tabbatar masa ta haihu baby boy.
Gida ya dawo da sabon tunani akan tunkarar wannan Zinneerah ɗin yaji daga gareta ita kuma, dan a tunaninsa da ace waccan ɗince data ganesa. To waccanma ai matar aurece miyasa zaiyi tunanin itace anan?.
Ruwa Meenal ta kawo masa ya sha. Ya kumace ta haɗa masa abinci a dining zaije yay wanka ya dawo. Binsa Zinneerah tai da kallo a cikin wani irin bahagon yanayi. Cikin dabara takai hannu ta share ƙwallar da suka ciko mata idanu. A yanzu haka babu abinda kecin ranta da damuwarta sai yanda Khalipha ya nuna tamkar baima taɓa sanintaba. Bayan ita tunda ya barta bata taɓa hutawa da tunaninsaba a ranta. har mafarkinsa tasha yi ma. Amma insha ALLAH zata daure itama ta kama kanta gareshi, idan ya ganota fine. idan ya cigaba da pretending ɗin rashin sanin nata itama saita samawa kanta lafiya ai. Da wannan tunani ta cigaba da hidimarta har lokacin Islamiyya yayi suka fita.
*_DANYA_*