Sashe 59
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327
.
Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd
07069711327
__________________________
*page 26*
...........Baki ya buɗe zai bama wanda suke maganar amsa dai-dai da isowarsa gab dasu hakan ya gagara. Dan a take harshensa ya sarƙe saboda sauka da idanunsa sukai akan fuskar Little dake ɗauke a kafaɗar Zinneerah ya wani lafe jikinta hannunsa na wasa da jelar kitsonta ta bayanta. Ita kanta sake shiga ruɗani zuciyarta tayi kasancewar kusancinsu sosai yau da little ɗin ya ƙara fiddo mata da kamanninsu ainun.
Sannan ganin yanda yake kallon little ɗin shima sai da hanjin cikinta suka motsa. Ba ita da shi bane kawai a ruɗanin hatta da mmn sadiq sai da tayi kamar zata kifa daga bayansu. Ƙirjinta kuwa yay wani mummunar bugawa tanabin AK ɗin da kallo. Duk da ƙarancin shekarun Sadiq da Abdull suma dai su kalli little su kalli AK ɗin da ayanzu yay ƙarfin halin ɗauke idanunsa yana maida hankalinsa ga wanda suke wayar duk da a baɗini sam hankalin nasa baya tare da shi.
A haka suka wuce juna su Sadiq na waiwayensa, hakama mmn sadiq sau kusan uku tana waiwayowa ta kallesa, kamar yanda shima ɗin ya kasa daina binsu da kallo. Zinneerah kam da ƙar ta cigaba dajan ƙafafunta ta ƙarasa dasu sashen hajiya iya. Inda acanma kallo ya koma sama. Dan tun sallamar da sukayi kowa ya amsa su Meenal suka taso da gudu suka rungume Mmn sadiq suna mata sannu. Sun juyo da nufin ma su Sadiq sannu da zuwa idanunsu ya sauka akan little.
“What!”.
Jamal ya faɗa a hankali yana tsare little ɗin dake lafe a kafaɗar Zinneerah har yanzu da ido. Sam hankalin Zinneerah baya tare dasu a yanzu, dan yau tafi kowacce irin rana shiga ruɗani akan kamannin little da Yah Adnan. Shiyyasa harta sauke little ɗin ƙasa bama tasan tayi ba. Hakan kuma dataine ya bama duk sauran yaran gidan ganinsa sosai. A take sannu da zuwan da suke Mmn sadiq ya shiga maƙalewa a maƙosansu. Dan yau harsu Momie suna a sashen suma.
Cikin ƙarfin hali Khalipha da yay mutuwar tsaye shima ya nuna musu hanyar ɗakin hajiya iya yana faɗin, “Mama ku shiga tana ciki”.
Kai Mmn sadiq ta ɗaga masa tana murmushin yaƙe dabin Khalipha ɗin da idanu itama dan ta ganesa duk da ya ƙara buɗewa fiye da wancan sanin datai masa.
Duk wannan al'amari dake faruwa Farah na ɗaki kwance dan taƙi sakewa a cikinsu kamar yanda takeyi dama idan tazo gidan. Saboda karma Adnan ɗin ya zargeta catai masa bata da lafiya. Yarda yay tunda yasan tana laulayin ƙaramin ciki kamar yanda Mammah ta sanar masa.
Hajiya iya na kwance suka shigo. amma tunda idonta ya sauka akan little itama babu shiri sai gata zaune. Ta haɗiye yawu da ƙyar tana miƙa masa hannu shi dasu Aliyun. Babu musu duk suka nufeta. Sai da suka gaisheta da jiki sannan suka zazzauna inda ta nuna musu a kusa da ita kan gadon. Little kuwa matsawa yay jikinta ya kwanta dan shi dama akwai son jiki. Su Sadiq sun shagwaɓa shi, harma dasu Mmn Sadiq ɗin.
Hajiya iya takai hannu kan little ta shafa zuciyarta na wani irin harbawa. A ranta ko rayawa take tamkar Moddibo na ƙarami. A fili kuma saita maida hankalinta ga Mmn sadiq dake gaisheta cike da kulawa.
Tunda suka shige aka shiga ƴar kallon kallo a falon, dan bakin kowa ya kasa furta komai. Sai can kamar a fisge Saffiya tace, “Wannan ai yaron dana ɗakko muku hotonsa ne. Amma kuma ba maman bace wannan”.
Shigowar Baffah da AK ne ya hana kowa amsa zancen Safiyya ɗin. Sai ma zubama Yayan nasu ido sukai zukatansu fal ruɗani. Shima kansa a ruɗanin yake. Amma kasancewarsa gwanin kamewa yasa babu mai iya fahimtar halin da yake a ciki akan fuskarsa. Sannu da zuwa duk suka shiga yima Baffah. Ya amsa musu sama-sama yana nufar ɗakin mahaifiyarsa dan ba'a cikin hayyacinsa ya dawo ba.
Da sallama ya shigo, AK biye dashi a baya. Ganin Mmn sadiq ya saka Baffah nuna jin daɗinsa. Suka gaisa cikkn girmama juna. Suma su Sadiq suka gaishesu ya amsa musu da kulawa. Sai da ya maida hankalinsa ga Hajiya Iya data kafe AK da kallo sannan shima idanunsa suka sauka akan little da barci ya fara ɗauka a jikin hajiya iya.
Wani irin muƙut, Baffah ya haɗiye yawu da ƙyar yana kallon little da ƙyau. Kasa jurewa yay sai da ya juyo ya kalli AK da gaba ɗaya hankalinsa ke akan little shima. Ya sake maidawa ya kalli little again zuciyarsa na wani irin rawa. Dan ƙarara zakaga shi ruɗaninsama akan fuska. Kasa jurewa yay sai da yace, “Ikon ALLAH innata kunga wani kamanni yau dake neman hargitsa tunanina anan, ɗan wanene wannan?”.
“Bakai kaɗaiba Babangida. Ni kaina bakaga na kasa daina kallon yaron da Moddibo ba. Ai wani hikima sai UBANGIJI. Wlhy sai kace Moddibo na ƙarami. Hauwa'u wannan yaro nikam idan a wani guri na gansa ai sai nace namune ma. Ina kika samosa?”.
Duk da faɗuwa da gaban mmn Sadiq yayi cikin juriya tai murmushi zata bata amsa Aliyu yay saurin faɗin, “Mama ƙaninmu ne”.
Shiru ɗakin yayi, Mmn Sadiq ta sauke wani ɓoyayyar ajiyar zuciya. Dan a ganinta ba'a wannan halin da hajiya iya ke a ciki yakamata tasan matsayin little ba. Amma insha ALLAHU tayi alƙawarin tana samun lafiya zasuzo ita da Abba sumasu bayanin komai. Shiyyasa taso tunma kan Zinneerah ta taho su faɗa musu. Amma batasan dalilin Abban na hanawaba.
Baffah ne ya katse tunanin na maman sadiq da faɗin, “Kai masha ALLAH, ALLAH ya albarkaceku, hikimar UBANGIJI ai tafi ƙarfin mamaki. Hakan na ƙara nuna mana muhimmancin zuminci da ƙarfin jini dake tsakaninmu Hauwa'u. ALLAH ya sake ƙara mana ƙarfi da kusanci, ya kuma sa muci amfanin hakan duniya da lahira”.
Da amin duk suka amsa. Baffa ya shafa kan yaran duka har little daya ɗan buɗe ido ya dubesa na kusan sakan goma sannan ya maida ya rufe. Daga haka aka koma gaishe-gaishe duk da zuciyar kowa dai ba adaidai takeba.
.
Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd
07069711327
__________________________
*page 26*
...........Baki ya buɗe zai bama wanda suke maganar amsa dai-dai da isowarsa gab dasu hakan ya gagara. Dan a take harshensa ya sarƙe saboda sauka da idanunsa sukai akan fuskar Little dake ɗauke a kafaɗar Zinneerah ya wani lafe jikinta hannunsa na wasa da jelar kitsonta ta bayanta. Ita kanta sake shiga ruɗani zuciyarta tayi kasancewar kusancinsu sosai yau da little ɗin ya ƙara fiddo mata da kamanninsu ainun.
Sannan ganin yanda yake kallon little ɗin shima sai da hanjin cikinta suka motsa. Ba ita da shi bane kawai a ruɗanin hatta da mmn sadiq sai da tayi kamar zata kifa daga bayansu. Ƙirjinta kuwa yay wani mummunar bugawa tanabin AK ɗin da kallo. Duk da ƙarancin shekarun Sadiq da Abdull suma dai su kalli little su kalli AK ɗin da ayanzu yay ƙarfin halin ɗauke idanunsa yana maida hankalinsa ga wanda suke wayar duk da a baɗini sam hankalin nasa baya tare da shi.
A haka suka wuce juna su Sadiq na waiwayensa, hakama mmn sadiq sau kusan uku tana waiwayowa ta kallesa, kamar yanda shima ɗin ya kasa daina binsu da kallo. Zinneerah kam da ƙar ta cigaba dajan ƙafafunta ta ƙarasa dasu sashen hajiya iya. Inda acanma kallo ya koma sama. Dan tun sallamar da sukayi kowa ya amsa su Meenal suka taso da gudu suka rungume Mmn sadiq suna mata sannu. Sun juyo da nufin ma su Sadiq sannu da zuwa idanunsu ya sauka akan little.
“What!”.
Jamal ya faɗa a hankali yana tsare little ɗin dake lafe a kafaɗar Zinneerah har yanzu da ido. Sam hankalin Zinneerah baya tare dasu a yanzu, dan yau tafi kowacce irin rana shiga ruɗani akan kamannin little da Yah Adnan. Shiyyasa harta sauke little ɗin ƙasa bama tasan tayi ba. Hakan kuma dataine ya bama duk sauran yaran gidan ganinsa sosai. A take sannu da zuwan da suke Mmn sadiq ya shiga maƙalewa a maƙosansu. Dan yau harsu Momie suna a sashen suma.
Cikin ƙarfin hali Khalipha da yay mutuwar tsaye shima ya nuna musu hanyar ɗakin hajiya iya yana faɗin, “Mama ku shiga tana ciki”.
Kai Mmn sadiq ta ɗaga masa tana murmushin yaƙe dabin Khalipha ɗin da idanu itama dan ta ganesa duk da ya ƙara buɗewa fiye da wancan sanin datai masa.
Duk wannan al'amari dake faruwa Farah na ɗaki kwance dan taƙi sakewa a cikinsu kamar yanda takeyi dama idan tazo gidan. Saboda karma Adnan ɗin ya zargeta catai masa bata da lafiya. Yarda yay tunda yasan tana laulayin ƙaramin ciki kamar yanda Mammah ta sanar masa.
Hajiya iya na kwance suka shigo. amma tunda idonta ya sauka akan little itama babu shiri sai gata zaune. Ta haɗiye yawu da ƙyar tana miƙa masa hannu shi dasu Aliyun. Babu musu duk suka nufeta. Sai da suka gaisheta da jiki sannan suka zazzauna inda ta nuna musu a kusa da ita kan gadon. Little kuwa matsawa yay jikinta ya kwanta dan shi dama akwai son jiki. Su Sadiq sun shagwaɓa shi, harma dasu Mmn Sadiq ɗin.
Hajiya iya takai hannu kan little ta shafa zuciyarta na wani irin harbawa. A ranta ko rayawa take tamkar Moddibo na ƙarami. A fili kuma saita maida hankalinta ga Mmn sadiq dake gaisheta cike da kulawa.
Tunda suka shige aka shiga ƴar kallon kallo a falon, dan bakin kowa ya kasa furta komai. Sai can kamar a fisge Saffiya tace, “Wannan ai yaron dana ɗakko muku hotonsa ne. Amma kuma ba maman bace wannan”.
Shigowar Baffah da AK ne ya hana kowa amsa zancen Safiyya ɗin. Sai ma zubama Yayan nasu ido sukai zukatansu fal ruɗani. Shima kansa a ruɗanin yake. Amma kasancewarsa gwanin kamewa yasa babu mai iya fahimtar halin da yake a ciki akan fuskarsa. Sannu da zuwa duk suka shiga yima Baffah. Ya amsa musu sama-sama yana nufar ɗakin mahaifiyarsa dan ba'a cikin hayyacinsa ya dawo ba.
Da sallama ya shigo, AK biye dashi a baya. Ganin Mmn sadiq ya saka Baffah nuna jin daɗinsa. Suka gaisa cikkn girmama juna. Suma su Sadiq suka gaishesu ya amsa musu da kulawa. Sai da ya maida hankalinsa ga Hajiya Iya data kafe AK da kallo sannan shima idanunsa suka sauka akan little da barci ya fara ɗauka a jikin hajiya iya.
Wani irin muƙut, Baffah ya haɗiye yawu da ƙyar yana kallon little da ƙyau. Kasa jurewa yay sai da ya juyo ya kalli AK da gaba ɗaya hankalinsa ke akan little shima. Ya sake maidawa ya kalli little again zuciyarsa na wani irin rawa. Dan ƙarara zakaga shi ruɗaninsama akan fuska. Kasa jurewa yay sai da yace, “Ikon ALLAH innata kunga wani kamanni yau dake neman hargitsa tunanina anan, ɗan wanene wannan?”.
“Bakai kaɗaiba Babangida. Ni kaina bakaga na kasa daina kallon yaron da Moddibo ba. Ai wani hikima sai UBANGIJI. Wlhy sai kace Moddibo na ƙarami. Hauwa'u wannan yaro nikam idan a wani guri na gansa ai sai nace namune ma. Ina kika samosa?”.
Duk da faɗuwa da gaban mmn Sadiq yayi cikin juriya tai murmushi zata bata amsa Aliyu yay saurin faɗin, “Mama ƙaninmu ne”.
Shiru ɗakin yayi, Mmn Sadiq ta sauke wani ɓoyayyar ajiyar zuciya. Dan a ganinta ba'a wannan halin da hajiya iya ke a ciki yakamata tasan matsayin little ba. Amma insha ALLAHU tayi alƙawarin tana samun lafiya zasuzo ita da Abba sumasu bayanin komai. Shiyyasa taso tunma kan Zinneerah ta taho su faɗa musu. Amma batasan dalilin Abban na hanawaba.
Baffah ne ya katse tunanin na maman sadiq da faɗin, “Kai masha ALLAH, ALLAH ya albarkaceku, hikimar UBANGIJI ai tafi ƙarfin mamaki. Hakan na ƙara nuna mana muhimmancin zuminci da ƙarfin jini dake tsakaninmu Hauwa'u. ALLAH ya sake ƙara mana ƙarfi da kusanci, ya kuma sa muci amfanin hakan duniya da lahira”.
Da amin duk suka amsa. Baffa ya shafa kan yaran duka har little daya ɗan buɗe ido ya dubesa na kusan sakan goma sannan ya maida ya rufe. Daga haka aka koma gaishe-gaishe duk da zuciyar kowa dai ba adaidai takeba.