← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 143 OF 155

Sashe 143

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

       Wanka tayi masa itama tayi sannan, tura little tayi wajen AK ya amso kayansa, ita kuma tai ƙoƙarin shiryawa a gurguje ta fito. Sai da ta haɗa ma little tea ta fara nema musu abinda zasuci yanda bazata takura ba. Harta gama bataji ɗuriyar little mai kukan yunwaba, hakan bai dametaba dan tasan wani abun ya samu acan.
      Kamarko ta sani dan AK na gama saka masa kaya tea ɗin ya haɗa masa da ruwan dispencer, ya haɗa masa da biscuits. Shima wankan yayi dan yanason yaje asibiti kar abin yay masa nisa. Koda ya fito wankan rashin ƙarfin jikin ya sakashi sake komawa ya kwanta har takai barcin ya sake figarsa.
       Lokacin da Zinneerah ta shigo falon da kayan abincin little kawai ta samu a falon ya barbaza filos ɗin kujera yayma falon kaca-kaca. “ALLAH ya shiryeka” kawai ta iya cewa ta ajiye abincin a dining. Kayan shara ta ɗakko ta fara a tunaninta AK yana wani abunne a ciki. Waje ɗaya ta saka little zama harta kammala kimtsa falon tasa turare. Ganin har lokacin shiru babu motsin dadynsa ga goma harta gota ya sata nufar bedroom ɗin a ɗarare danta sanar masa ga abinci. Kusan sau uku tai sallama babu amsa. hakan ya sata tura ƙofar ta ɗan leƙa kanta a tunaninta koma dai baya gidan ne.
       Zaune ta hangosa a bakin gado dan dai-dai ya tashi kenan saboda sallamarta. Hannunsa dafe da kansa dake masa tsananin ciwo. Jitai tamkar ta juya da baya dan da ga shi sai boxer ne, amma ganin yanda ya dafe kansa yasata tunanin ba lafiya ba. tunda jiya dai ga a yanda suka dawo su duka, kuma tanaji sanda yake sanarma Khalipha kansa na masa ciwo a jiyan.
        Kanta a ƙasa ta ƙaraso cikin ɗakin, sai da tazo kusa da shi sannan ta rissina tana gaishesa batare data sake yarda ta kallesa ba. A yanda ya amsa ɗin kuma sai tsoro ya sake kamata, cikin damuwa tace, “Yayanmu baka da lafiya ne?”.
      Shiru kamar bazai amsaba har kusan mintuna biyu sannan ya ɗago idanunsa da sukai jajur yana dubanta. Kwalliyar tata tayi masa ƙyau, dan haka yaɗan lumshe ido ya sake buɗewa a kanta da cewa, “Kaina ke ciwo. Haɗamin ruwan wanka inason naje asibiti”.
           Sosai damuwa ta bayyana ƙarara a fuskarta. ta shiga jera masa sannu kamar zatai kuka. Shi dai kallonta kawai yake dan duk da yana cikin halin ciwo yanda takeyi ɗin tada masa tsigar jiki take. Ga mayatattun turarurrukan ta da ƙamshinsu ke ɗaga masa hankali zuwa ga buƙatarta.  Ya ɗan cije lips ɗinsa yana komawa da baya a saman gadon ya ɗan kwanta kafin ta kammala haɗa ruwan.
     Sai da ta tsaftace masa toilet ɗin duk da ba wani uban datti yay ba sannan ta haɗa ruwan, ta fito hanunta da tissue data warwaro daga can tana gogewa. Da ƙyar ya iya yunƙurawa ya tashi zuwa bayin.
       Ta ɗan sauke numfashi da fara ƙoƙarin gyara masa gadon, daga haka ta zarce da tsaftace ɗakin gaba ɗaya. Ɗan jimawa da yake a wanka yasa harta kammala kafin ya fito, tana fesa fresheners take jiyo little na ƙwala mata kira daga falo. “Aunty! Aunty!!”.
       “Oh ALLAH! Na'am”. Ta faɗa tana ajiye gwangwanin freshener ɗin. hakan kuma sai yay dai-dai da fitowar AK daga bayi. Bata yarda ta dubesaba, sai sake amsama little kiran da yake mata tayi. Ta ɗaga ƙafa zata nufi hanyar fita taji an ruƙo mata hannu. cak ta tsaya dan tasan dai shine.
        “Idan kin tafi wazai shiryani”. Ya faɗa a hankali yana jawota ta juyo tana fuskantarsa. Kasa kallonsa tai dan dagashi sai guntun towel. Ganin yanda taketa sinne kai ya ɗago fuskar tata da ƙoƙarin saka idanunsa cikin nata. “Nazama surukinki ne?”.
       “A'a” ta faɗa a hankali tana ɗan murmushi.
        “Hum” ya faɗa da kama hannunta yajata suka ƙarasa gaban mirror ɗin. Duk yanda taso zamewa dole tabi umarnin sa. dan dolenta ta shafa masa mai da kanta, ta kuma ɗakko masa kayan da zaisa wanda bazai takura ba. A gaɓar shiryawane dai kam ta kasa duk yanda yaso dole ya barta ya shirya da kansa.

     Falo suka fito a tare suka sami little, baiyi tunanin ita tai girkinba, sai dai ya masa daɗi, kaɗan yaci yau kam dan da gaske bayajin daɗi, yana gamawa ya koma falo ya kwanta cikin kujera saboda jiri, wayarsa yace ta ɗakko tai kiran Doctor Mahmud yazo ya dubashi, dan bama zai iya driving ba. Cikin damuwa ta ɗakko ta lalubo masa no ɗin Dr Mahmud ɗin, yana ɗagawa ta miƙa masa wayar yay magana da shi.

       Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga Doctor Mahmud da Khalipha tare. Bayan ta gaisa dasu ta bar musu sashen saboda kallon da AK ke mata na gargaɗi dan ko mayafi babu a jikinta yau.
        Koda ta koma a can tai zaman karyawa itama. Bata sake leƙo sashenba sai da little yazo ya kirata. Hijjab ta zunbula dan hanyar lafiya a bita da shekara. Khalipha kawai ta samu tare da shi sai Huzaifa da batasan da zuwansaba. Ta gaisa da Huzaifa daketa tsokanarta da amarya amarya. Ita dai murmushi ne nata kawai babu bakin ramawa.
    Ta ɗan dubi AK da akema ƙarin ruwa idanunsa a lumshe. Sannu tai masa dan ta fahimci idonsa biyune, saboda riƙe yake da hannun little dake tsaye gaf da fuskarsa yana masa maganar da batasan kota micece ba. Khalipha ne ya sanar mata abinda zatayi, dan haka ta juya ta sake fita ta barsu.

           ★*********★

Abu kamar wasa sai ga AK yasha zazzaɓi kwana biyu, dan sai da takai har Baffah da Uncle Ahmad sai da sukazo dubashi, hakama su Mammah dake shirin komawa gobe idan ALLAH ya kaimu sunzo sun dubata da sake neman gafarar Zinneerah. Yanda Mammah taketa tattalin Little sai ta baka tausayi, gashi shi saima wani ƙiwan wulaƙanci yaketa faman mata.
     Shima AK ɗin sun ƙara masa nasiha da nuna masa muhimmancin yarda da ƙaddara. Mammah ta sake neman gafararsa duk da ta fahimci fushi yake da ita. Nuna mata yay shifa komai ya wuce, amma ita tasan bai wuce ba tunda ya kasa sakin jiki da kowa sai ɗansa da matarsa.

        Yau Alhmdllh ya tashi jikin nasa da sauƙi sosai, dan har fita yay zuwa gidansu shi da little. Bayan sallar la'asar Zinneerah na falonta na biyu zaune tana cire ƙumba ya shigo da sallama. Gaidashi tai da masa sannu da dawowa. Ya amsa mata yana kaiwa zaune. Ita kuma ta miƙe dan kawo masa ruwa. Amma sai jitai ya ruƙota. Duk yanda taso zamewa ya hanata damar hakan. Cikin wani irin kasalalliyar murya yake mata magana a kunne. “Wace irin amaryace wannan mai rowan tsiya nikam?”.
        Ɗan dubansa tai dan bata fahimci ina ya dosaba, ya ɗage giransa ɗaya yana kasheta da kallonsa mai sakata nutsuwa. Itama dai yau tayi dauriya da jarumtar kallon nasa cikin idon, da wannan damar yay amfani wajen ɗora lips ɗinsa kan tausasan nata. Sukaja numfashi a tare da lumshe idanunsu. Sai gata luff ta nutsu tana amsa saƙonsa. Sai da labarin ya fara canja salo kuma ta nema raina kanta. Ko saurarenta baiyiba ya ɗauketa cak yay cikin bedroom ɗinta da ita. Ganinfa irin na ranar yake son maimaitawa tuni ta fara tsuma da neman roƙomsa shikam baima jinta ya antaya duniyar kodumo.

      Duk yanda taso daurewa yau ma dai kasawa tai, sai da ta kaita da masa kuka, dan wannan yayan nasu bana wasan yara bane, baisan sauƙi ko sassauci ba har sai ya kai boader.
     Sai da ya ga ya samu kansa ya koma tsokanarta da suna ragguwa. Ita ko ta dinga tura baki har a wajen wanka da ya taimaka mata ta kuma gasa jikinta yanda zataji daɗi. Suna fitowa ya gudu sashensa dan kiran sallar magrib ake tayi.

      Bata sake ganin ƙeyarsa ba sai bayan sallar isha'i, ta fito domin nema musu abinci shi kuma ya shigo hannunsa ɗauke da leda alamar ya biya ta ɗakinsa kafin yazo nan. Zama yay da kiran sunanta, dan haka ta nufosa zata zauna ƙasa ya nuna mata gefensa. Sai da takai zaune sannan ya miƙa mata ledar. Amsa tai tai godiya duk da batasan minene a cikiba, tana buɗewa taci karo da waya mai ƙyau. Ai tuni jin daɗi yasa ta manta da Yayansu ne fa. Ta miƙe ta ɗane masa jiki tana murna.
           Murmushi yalwace da fuskarsa ya karɓe abinsa yana cusa kansa a wuyanta. “Yanzu kin ɗaneni, da an taɓaki kuma ki hau yima mutane raki”.
     Kanta ta cusa a ƙirjinsa tana dariya da faɗin “ALLAH akwai wuya Yayanmu, kai dan baka sani bane”.
     Dariya ta basa, amma sai baiyiba ya cigaba da murmushinsa yana cusa hannunsa cikin gashinta, “Ni kuma gashi ba wasa zan tsayaba ƙannen little nakeso da wuri, dan naga shikam ba barmana zasuyiba haka zai ringa yawo tsakanin danya, gidan Abba, gidan Baffah, london. Kinga saiki sama mana namu muma”.
      Ƙwaɓe fuska tai cikin marairaicewa. “Yayanmu ba yanzuba akwai wahala wlhy”.
     Kansa ya ɗan girgiza mata da sumbatar lips ɗinta. “Haba my Neerat ai ke jarumace tunda kika haifo Abdul-Mutallab tun kinada shekaru sha huɗu, yanzu kam ko ƴan huɗu ne zaki iya ai”.
       “Sai dai in zaka tayani”.
Ta faɗa tana ɓoye fuskarta a jikinsa. Sosai yanzu kam ya ƙyalƙyale da dariya. “Mizai hana na tayaki nikam Mrs Shira, ai tare zamuyi rainon cikin muyi naƙuda abunmu mukuma rainesa idan ya fito”.
    Dariya sosai Zinneerah keyi itama mamaki fal ranta na Yayansu. Ashe haka yake da sauƙin kai da sakin jiki, amma yayta musu mazurai a gida.
Chapter 143 · 0% Book details