Sashe 146
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka rayuwar London ta cigaba da tafiya cikin jin daɗi da farin ciki, sai dai wataran saɓani da ɓacin rai kanɗan gitta tamkar yanda akasan kowanne gidan ma'aurata. Amma lallai bazasu taɓa iya mantawa da rayuwar london ba dan rayuwace mai tsayawa azuciya garesu. Anci soyayya kamar babu gobe.
Sunada wata ɗaya a london matar dake ɗauke da cikin da aka dasa mata ta Morocco ta haihu, sai dai abin ƙaddara ta haifi yarinya mace babu rai, abinda yasa zancenta baiyi tsaho ba ta tabbatar ma su Baffah cewar da amincewarta su Zakiyya sukai komai, ko yanzu suka shirya kuma zata ƙara ɗauka musu wani cikin tunda wannan batazo da rai ba. Godiya kawai sukai mata da bata wasu kuɗaɗe suka barota.
Duk da kuwa AK yaji baƙin cikin ta yanda aka samar da ɗiyar itama sai da yay hawayen rasuwarta lokacin da aka turo masa hotonta a waya abin sha'awa. Ya sunbaci wayar da jerama UBANGIJI kirari da addu'a a gareta da sauran al'ummar musulmi baki ɗaya. Zinneerah kanta sai taji yarinyar ta shiga ranta. Hakama Hajiya iya dasu Mammah. To amma yaya za'ai da hukuncin ALLAH sai haƙuri.
Watansu biyu cif suka dawo gida Nigeria domin halartar bikin ƴaƴa bakwai daga zuri'ar Abdul-Mutallab Shira. A lokacin cikin Zinneerah nada watanni huɗu cif. Ya ɗan turo abinsa duk mai lura zai iya ganinsa.
Aiko sai ta dinga ƙunshe-ƙunshe musamman da taje gidan mmn Sadiq. aiko su Meenal suka dinga mata dariya. Taso zuwa duba Inna kafin a shiga hidimar bikin amma AK ya hana, acewarsa ta bari a gama biki sai suje dan akwai maganar Dr Mahmud ma da Sa'a a ƙasa.
Kamar yanda ya umarceta da haƙurin haka ta haƙura aka shiga shagalin bikin su Abidah da aka shiryama bidi'oi kala-kala, danma AK ya zaftare wasu a ciki yanata faɗa.
Ranar ɗaurin aure a bazata sai ga sunan Khalipha a cikin anguna. An zarga masa igiya uku da ɗiyar Uncle Ahmad Raheenat (Noor). Kowa kam yayi farin ciki da wannan haɗi musamman ma Uncle Ahmad. Shima dai ango da gaske yanaso dan ƙiri-ƙiri ya nuna farin cikinsa. Abin sauƙin ma shima yanada gidansa dama da yake gini, ƴan abubuwane kawai suka rage a ƙarasa dan haka aka hau sauran aiki babuji babu gani. Matar Uncle Ahmad tayi baƙin cikin wannan haɗi itakam, sai dai babu yanda zatai dole ta haƙura. Dan dama taƙi sakin jiki da matan gidan sam. Suko da yake ba kanwar lasa bane duk sai suka watsar da ita suma suka cigaba da sabgogin gabansu.
A bikin nan dauriya kawai Zinneerah keyi dan batajin daɗin jikinta, hayaniyarma sam bataso, shiyyasa lokuta da dama zaka sameta can gefe a killace. Hakan sai yayma AK daɗi dan bata halarci bidi'a ko daya ba da akai garama kamu da akayi anan cikin gidan. Ana saka kiɗa kuwa sai da tabar gidan saboda ciwon kai mai tsanani. Can gidansu ta koma tai kwanciyarta ta hutama ranta.
Ansha shagalin biki harna kwanaki uku aka miƙa amare ɗakinsu. Adilah lagos, Safiyya Abuja. Sauran kuma Ni'ima da Abidah duk anan kano ne, sai Noor da aka bari sai nan da kwanaki uku an kammala aikin gidan Khalipha.
(To amare da angwaye ALLAH ya sanya albarka ya kawo ƴan dugwi-dugwi iyalan baba).
Washe garin da aka shashshare daga bikin nan kuma aka kai kuɗin auren Sa'a danya. Inda baƙi suka sami tarba ta mutunci da girmamawa. Inna ga dama ta samu amma babu halin damawa, sai hawayen zuci takeyi.
Dan tuni aka maidota gida. Sai dai a duk sanda ta kalli Tinene da tsohon ciki ranar sai ciwonta ya rikice. Hakan yasa suka yanke shawarar maida Tinene gidan Gwaggo laritu harta haihu, dan an ajiye magana randa ta haihu za'a ɗaura mata aure damai cikin tunda ya amsa nasane.
Daga kai kuɗi baba yace shikam dai baimaga wani abun jeka ka dawo ba a ɗaura aure kawai a huta. Zuwa wani satin ta tare ɗakinta taje tai haƙuri tamkar kowa. Hakan yama Dr Mahmud daɗi, hakama su Baffah da suka kai kuɗin. Nanko take aka zarge igiya uku tsakanin Sa'adatu Sulaiman Danya da Dr Mahmud Dawood. Zokaga baki wajen ango. Aiko AK ya dinga masa sherin kurame yana ramawa shima kamar yanda yay masa. Dan bazai fito kai tsaye yay maganaba sai dai yayi a fisge ya tsuke baki cikin basarwa tamkar bashine yayi ba.
Cike da farin ciki suka dawo kano da wannan labari, Zinneerah kam tafi kowa murnar wannan al'amari dan har kukan daɗi tayi.
Cikin amincin ALLAH sati na zagayowa akai tariyar Sa'a. sai dai Zinneerah bataje Danya ba dan batajin daɗin jikinta kam, Khalipha ma tasa amaryar ta tare a nasa gida da aka kammala. Yanzu kam sai dai mu cigaba dabin kowa da fatan alkairi.
Tun bayan tariyar Sa'a komai ya sake lafawa, Khalipha ya koma London shi kaɗai domin karasa karatunsa. Zinneerah ma cikin ƙarfin hali AK ya sata zana exam na November/December. Tasha wahala saboda laulayin dake damunta, amma babu laifi tayi ƙoƙari Alhmdllh, sai fata da addu'ar fitowar ƙyaƙyƙyawan result.
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Zinneerah na rainon cikinta dake ƙara fitowa yana wahal da ita, duk ta rame sai haske data ƙara kam masha ALLAH. Yanda wahalar tai mata yawa ne ga aikin gida ga little ya fara makaranta, dan yanzu yafi zama anan fiye da ko ina, yawonsa sai weekend, ga gida shiru ita kaɗai yasa Hajiya iya cemasa ya maidota nan gidan sai ta haihu.
Babu wani ɓoye-ɓoye ya ɓata ransa. Dan shi dai yafison su cigaba da lallaɓawa a hakan har ALLAH ya sauketa lafiya. Tunda dai bawai kwance take rijif ba. Aikin gida da lalurarsa girki da sauransu duk tanayi. Fitace kawai bata cika sonyi ba dan wahala take sha sosai koda kuwa zuwa gidan su Granny ne kawai tayi ko gidan mmn sadiq. Shiyyasama ta tattara kowanne yawo ta ajiye.
“Ikon ALLAH, wai ka cika baki da iska! Bazaka maidotan bane komi kake nufi moddibo?”.
Shiru yay mata kamar bazai tanka ba, sai da yaja wasu sakanni ya dubeta yana ajiye wayar hannunsa. “Granny ki fahimta mana dan ALLAH, taya yarinya na gidan mijinta ace ta taso ta baro. Wazai kula damu ni da Abdul-Mutallab to?”.
“Owoo, sai ta zauna zaman kula da ku ita kuma ta kashe kanta. Kana ganin yanda duk jikinta ya koma ko abincin kirki bataci sai yame-yame”.
“Granny duk nasan da waɗanan matsalolin kuma suna damuna wlhy nima, ina kuma yin iya bakin ƙoƙarina na ganin na bata kulawa nima, kuma Alhmdllh jikin natama ya fara sauƙi. Kawai dai idan kin yarda a samo wata ta zauna da ita ni ko nawane zan biya. Kokuma ke ki koma can dan ALLAH ”.
“Wa? Kama kanka. Kawai sai naje ƙososo na zauna muku a gida raba kanka malam”.
Murmushi yayi a ransa yana faɗin, ‘Ai wlhy ke zan lallaɓa kije madam, nasan maganinki ai’. A fili kam sai yay mata shiru, daga ƙarshe ma ya miƙe yana faɗin, “Bara naje na ɗauka Abdul-Mutallab a makaranta”.
“ALLAH ya kiyaye ka gaishesu”.
Zinneerah na falon farko na sashenta a kwance cikin kujera barci ya ɗan fara figarta daga charting dasu Meenal suka shigo. Kamar yanda Little ya saba duk da kuwa yanzu ya ƙara girma da wayo ga shegen miskilanci kamar sunyi kaki sun ajiye ya nufeta da gudu. Yana ƙoƙarin faɗa mata a jiki AK ya ɗagashi sama dan yanayinta ya nuna masa batajin daɗin jikin. Kuma lafiya lau ya fita ya barta.
Itama ajiyar zuciya ta sauke ganin ya hana little ɗin faɗa mata a jiki. Ta yunƙura ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Amsawa yay idonsa a kanta yana kaiwa zaune kusa da ita little a jikinsa.
“Jikin ne kuma?”.
Fuska Zinneerah taɗan yamutse tana kamo hannun little ɗin. “Kawai dai banajin ƙarfi ne amma babu inda kemin ciwo, garama tashin zuciya daketa damuna tun cin kifin nan na jiya da naci”.
Tausayintane ya sake kamashi, musamman daya tuna yanda taita damunsa da maganar kifin. harma ya dawo gida jiya da nufin bazai sake fitaba ta takura sai da ya fita kusan goma na dare ya nemo mata kifin, gashi kuma taci ta kasa zaman lafiya.
“Sannu ALLAH yay miki albarka ya saukeki lafiya. Bara na taɓa Mahmud naji kozaki iya shan wani abu dazai baki nutsuwa”.
“Yayanmu kama barshi zai bari dan kansa. Dan nayi waya da Yaya gajeje tace na samu ɗan kanwa kaɗan nasa a ruwa na sha zai faɗa min”.
Kafin yace wani abu little da yay kamar ba saurarensu yakeba yace, “Aunty sorry, idan kika haifa mana babynmu zan kaiki makka”.
Dariya zancen nasa ya basu, dan haka suka murmusa AK na shafa kansa. “ALLAH ya tabbatar ɗan albarka. Yanzu ka muje na maka wanka kaga aunty yau babu kanta”.
Kansa ya ɗaga masa. Zinneerah tace, “Kama barshi zan iya masa. Bara kaima na haɗama ruwan wankan ga abinci nan na shirya”.
“Kina fama da kanki kika wani kama abinci? Nace miki duk randa baƙyajin daɗi basai kinyi ba tunda ga gidan Granny sai a kawo daga can”.
Murmushi ta ɗanyi da kama hannunsa dan ta tura little ɗaki ya kai kayan sa. Ta kwanto jikin hannunsa tana duban ƙyaƙyƙyawan fuskarsa. “Yayanmu nace makafa bawani ciwo nakejiba ALLAH. Kuma idan ban motsa jikin ai sai wani kuma ciwon ya taso”.
Kanta ya shafa yana rungumota da ƙyau jikinsa. Ya sumbaci laɓɓanta da goshinta yana jera mata addu'a. Itama hannunsa ta sumbata ranta fes ƙaunarsa na ƙara shigarta jini da ɓargo.
Sunada wata ɗaya a london matar dake ɗauke da cikin da aka dasa mata ta Morocco ta haihu, sai dai abin ƙaddara ta haifi yarinya mace babu rai, abinda yasa zancenta baiyi tsaho ba ta tabbatar ma su Baffah cewar da amincewarta su Zakiyya sukai komai, ko yanzu suka shirya kuma zata ƙara ɗauka musu wani cikin tunda wannan batazo da rai ba. Godiya kawai sukai mata da bata wasu kuɗaɗe suka barota.
Duk da kuwa AK yaji baƙin cikin ta yanda aka samar da ɗiyar itama sai da yay hawayen rasuwarta lokacin da aka turo masa hotonta a waya abin sha'awa. Ya sunbaci wayar da jerama UBANGIJI kirari da addu'a a gareta da sauran al'ummar musulmi baki ɗaya. Zinneerah kanta sai taji yarinyar ta shiga ranta. Hakama Hajiya iya dasu Mammah. To amma yaya za'ai da hukuncin ALLAH sai haƙuri.
Watansu biyu cif suka dawo gida Nigeria domin halartar bikin ƴaƴa bakwai daga zuri'ar Abdul-Mutallab Shira. A lokacin cikin Zinneerah nada watanni huɗu cif. Ya ɗan turo abinsa duk mai lura zai iya ganinsa.
Aiko sai ta dinga ƙunshe-ƙunshe musamman da taje gidan mmn Sadiq. aiko su Meenal suka dinga mata dariya. Taso zuwa duba Inna kafin a shiga hidimar bikin amma AK ya hana, acewarsa ta bari a gama biki sai suje dan akwai maganar Dr Mahmud ma da Sa'a a ƙasa.
Kamar yanda ya umarceta da haƙurin haka ta haƙura aka shiga shagalin bikin su Abidah da aka shiryama bidi'oi kala-kala, danma AK ya zaftare wasu a ciki yanata faɗa.
Ranar ɗaurin aure a bazata sai ga sunan Khalipha a cikin anguna. An zarga masa igiya uku da ɗiyar Uncle Ahmad Raheenat (Noor). Kowa kam yayi farin ciki da wannan haɗi musamman ma Uncle Ahmad. Shima dai ango da gaske yanaso dan ƙiri-ƙiri ya nuna farin cikinsa. Abin sauƙin ma shima yanada gidansa dama da yake gini, ƴan abubuwane kawai suka rage a ƙarasa dan haka aka hau sauran aiki babuji babu gani. Matar Uncle Ahmad tayi baƙin cikin wannan haɗi itakam, sai dai babu yanda zatai dole ta haƙura. Dan dama taƙi sakin jiki da matan gidan sam. Suko da yake ba kanwar lasa bane duk sai suka watsar da ita suma suka cigaba da sabgogin gabansu.
A bikin nan dauriya kawai Zinneerah keyi dan batajin daɗin jikinta, hayaniyarma sam bataso, shiyyasa lokuta da dama zaka sameta can gefe a killace. Hakan sai yayma AK daɗi dan bata halarci bidi'a ko daya ba da akai garama kamu da akayi anan cikin gidan. Ana saka kiɗa kuwa sai da tabar gidan saboda ciwon kai mai tsanani. Can gidansu ta koma tai kwanciyarta ta hutama ranta.
Ansha shagalin biki harna kwanaki uku aka miƙa amare ɗakinsu. Adilah lagos, Safiyya Abuja. Sauran kuma Ni'ima da Abidah duk anan kano ne, sai Noor da aka bari sai nan da kwanaki uku an kammala aikin gidan Khalipha.
(To amare da angwaye ALLAH ya sanya albarka ya kawo ƴan dugwi-dugwi iyalan baba).
Washe garin da aka shashshare daga bikin nan kuma aka kai kuɗin auren Sa'a danya. Inda baƙi suka sami tarba ta mutunci da girmamawa. Inna ga dama ta samu amma babu halin damawa, sai hawayen zuci takeyi.
Dan tuni aka maidota gida. Sai dai a duk sanda ta kalli Tinene da tsohon ciki ranar sai ciwonta ya rikice. Hakan yasa suka yanke shawarar maida Tinene gidan Gwaggo laritu harta haihu, dan an ajiye magana randa ta haihu za'a ɗaura mata aure damai cikin tunda ya amsa nasane.
Daga kai kuɗi baba yace shikam dai baimaga wani abun jeka ka dawo ba a ɗaura aure kawai a huta. Zuwa wani satin ta tare ɗakinta taje tai haƙuri tamkar kowa. Hakan yama Dr Mahmud daɗi, hakama su Baffah da suka kai kuɗin. Nanko take aka zarge igiya uku tsakanin Sa'adatu Sulaiman Danya da Dr Mahmud Dawood. Zokaga baki wajen ango. Aiko AK ya dinga masa sherin kurame yana ramawa shima kamar yanda yay masa. Dan bazai fito kai tsaye yay maganaba sai dai yayi a fisge ya tsuke baki cikin basarwa tamkar bashine yayi ba.
Cike da farin ciki suka dawo kano da wannan labari, Zinneerah kam tafi kowa murnar wannan al'amari dan har kukan daɗi tayi.
Cikin amincin ALLAH sati na zagayowa akai tariyar Sa'a. sai dai Zinneerah bataje Danya ba dan batajin daɗin jikinta kam, Khalipha ma tasa amaryar ta tare a nasa gida da aka kammala. Yanzu kam sai dai mu cigaba dabin kowa da fatan alkairi.
Tun bayan tariyar Sa'a komai ya sake lafawa, Khalipha ya koma London shi kaɗai domin karasa karatunsa. Zinneerah ma cikin ƙarfin hali AK ya sata zana exam na November/December. Tasha wahala saboda laulayin dake damunta, amma babu laifi tayi ƙoƙari Alhmdllh, sai fata da addu'ar fitowar ƙyaƙyƙyawan result.
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Zinneerah na rainon cikinta dake ƙara fitowa yana wahal da ita, duk ta rame sai haske data ƙara kam masha ALLAH. Yanda wahalar tai mata yawa ne ga aikin gida ga little ya fara makaranta, dan yanzu yafi zama anan fiye da ko ina, yawonsa sai weekend, ga gida shiru ita kaɗai yasa Hajiya iya cemasa ya maidota nan gidan sai ta haihu.
Babu wani ɓoye-ɓoye ya ɓata ransa. Dan shi dai yafison su cigaba da lallaɓawa a hakan har ALLAH ya sauketa lafiya. Tunda dai bawai kwance take rijif ba. Aikin gida da lalurarsa girki da sauransu duk tanayi. Fitace kawai bata cika sonyi ba dan wahala take sha sosai koda kuwa zuwa gidan su Granny ne kawai tayi ko gidan mmn sadiq. Shiyyasama ta tattara kowanne yawo ta ajiye.
“Ikon ALLAH, wai ka cika baki da iska! Bazaka maidotan bane komi kake nufi moddibo?”.
Shiru yay mata kamar bazai tanka ba, sai da yaja wasu sakanni ya dubeta yana ajiye wayar hannunsa. “Granny ki fahimta mana dan ALLAH, taya yarinya na gidan mijinta ace ta taso ta baro. Wazai kula damu ni da Abdul-Mutallab to?”.
“Owoo, sai ta zauna zaman kula da ku ita kuma ta kashe kanta. Kana ganin yanda duk jikinta ya koma ko abincin kirki bataci sai yame-yame”.
“Granny duk nasan da waɗanan matsalolin kuma suna damuna wlhy nima, ina kuma yin iya bakin ƙoƙarina na ganin na bata kulawa nima, kuma Alhmdllh jikin natama ya fara sauƙi. Kawai dai idan kin yarda a samo wata ta zauna da ita ni ko nawane zan biya. Kokuma ke ki koma can dan ALLAH ”.
“Wa? Kama kanka. Kawai sai naje ƙososo na zauna muku a gida raba kanka malam”.
Murmushi yayi a ransa yana faɗin, ‘Ai wlhy ke zan lallaɓa kije madam, nasan maganinki ai’. A fili kam sai yay mata shiru, daga ƙarshe ma ya miƙe yana faɗin, “Bara naje na ɗauka Abdul-Mutallab a makaranta”.
“ALLAH ya kiyaye ka gaishesu”.
Zinneerah na falon farko na sashenta a kwance cikin kujera barci ya ɗan fara figarta daga charting dasu Meenal suka shigo. Kamar yanda Little ya saba duk da kuwa yanzu ya ƙara girma da wayo ga shegen miskilanci kamar sunyi kaki sun ajiye ya nufeta da gudu. Yana ƙoƙarin faɗa mata a jiki AK ya ɗagashi sama dan yanayinta ya nuna masa batajin daɗin jikin. Kuma lafiya lau ya fita ya barta.
Itama ajiyar zuciya ta sauke ganin ya hana little ɗin faɗa mata a jiki. Ta yunƙura ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Amsawa yay idonsa a kanta yana kaiwa zaune kusa da ita little a jikinsa.
“Jikin ne kuma?”.
Fuska Zinneerah taɗan yamutse tana kamo hannun little ɗin. “Kawai dai banajin ƙarfi ne amma babu inda kemin ciwo, garama tashin zuciya daketa damuna tun cin kifin nan na jiya da naci”.
Tausayintane ya sake kamashi, musamman daya tuna yanda taita damunsa da maganar kifin. harma ya dawo gida jiya da nufin bazai sake fitaba ta takura sai da ya fita kusan goma na dare ya nemo mata kifin, gashi kuma taci ta kasa zaman lafiya.
“Sannu ALLAH yay miki albarka ya saukeki lafiya. Bara na taɓa Mahmud naji kozaki iya shan wani abu dazai baki nutsuwa”.
“Yayanmu kama barshi zai bari dan kansa. Dan nayi waya da Yaya gajeje tace na samu ɗan kanwa kaɗan nasa a ruwa na sha zai faɗa min”.
Kafin yace wani abu little da yay kamar ba saurarensu yakeba yace, “Aunty sorry, idan kika haifa mana babynmu zan kaiki makka”.
Dariya zancen nasa ya basu, dan haka suka murmusa AK na shafa kansa. “ALLAH ya tabbatar ɗan albarka. Yanzu ka muje na maka wanka kaga aunty yau babu kanta”.
Kansa ya ɗaga masa. Zinneerah tace, “Kama barshi zan iya masa. Bara kaima na haɗama ruwan wankan ga abinci nan na shirya”.
“Kina fama da kanki kika wani kama abinci? Nace miki duk randa baƙyajin daɗi basai kinyi ba tunda ga gidan Granny sai a kawo daga can”.
Murmushi ta ɗanyi da kama hannunsa dan ta tura little ɗaki ya kai kayan sa. Ta kwanto jikin hannunsa tana duban ƙyaƙyƙyawan fuskarsa. “Yayanmu nace makafa bawani ciwo nakejiba ALLAH. Kuma idan ban motsa jikin ai sai wani kuma ciwon ya taso”.
Kanta ya shafa yana rungumota da ƙyau jikinsa. Ya sumbaci laɓɓanta da goshinta yana jera mata addu'a. Itama hannunsa ta sumbata ranta fes ƙaunarsa na ƙara shigarta jini da ɓargo.