← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 155

Sashe 51

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

      koda taje sashensu Bahijja da suka tambayeta labarin yanda ta ƙare da kai shayi catai musu ai babu abinda ya faru, dama takai masa shayin yana wanka ajiyewa kawai tayi ta fito abinta. Mararta ke mata ciwo kaɗan-kaɗan shiyyasa taje ɗaki ta kwanta ganin sun fito.
       Meenal tace, “Yo tsoro mukaji kar wani abu ya faru yazo ya haɗa damu. dan laifinmu sai yafi naki. cazaiyi mune bamu nuna mikiba yasin”.
     Ƙaramar dariya kawai Zinneerah tai ta zame ta kwanta. Daga haka suka cigaba da hirarsu. Daga ƙarshe ranar anan ta kwana abinta.

_____________________★

    *DANYA*

     Ta daɗe kwance tana maida numfashin gajiya dana yunwa daya jigatata. Kafin ta miƙe dan ɗan kunun da tasha ya taimaketa. Ledar data shigo da ita ta jawo, ta buɗe tana fiddo kayan da malam ya haɗa mata da ƙara bitarsu yanda bazata mantaba. Baki ta washe na farin ciki tunawa da baba ya kusa dawowa gareta. Ta ɗaga wata ƴar kwalbar turare tana jujjuyawa.
        “Yanda ka bani wahala akan ƴarka Sule, sai na sakaka mantawa da ita na har abada acikin jerin ƴaƴanka. Duk dukiyata data salwanta dan ganin ka dawo saina fansheta a jikinka ko sisi bazanyi asaraba. Ƴan uwanka kuwa dake aibantani a gari cewar ta sanadina kabar Danya zan koyar dasu hankali a sannu, duk sai kunsan kunyi da Asabe wlhy”. Ta ajiye kwalbar tana cigana da dariyarta. Maida komai tai a ledar bayan ta ɗauka wasu layu guda biyu ta fice a ɗakin.
        Inda murhun girkinsu yake ta nufo. kasancewar jiyama ba girki sukai a gidanba yasa ta turbuɗa hannunta tsakkiyar tokar hankali kwance ta fara tonawa. Sai da ta ƙwakule tokar duka tasa icce ta fara tona ƙasar sannan ta saka layun nan guda biyu ta maida ƙasar da tokar ta rufesu ruf tamkar komai bai faruba. Duk da basu da isashen hatsin yin tuwon dare a gidan haka ta tattare ɗan wanda Yaya gajeje ta kawo musu daya rage ta wanke ta fita kai niƙa da kanta. Tasan ko jiran Tinene tace zatayi tayi a banza, baizama lallaima ta sake ganinta gidan a yanzuba kuma.

       Da ƙyar ta samu Malam Mati yay mata niƙan akan bashi zata kawo masa kuɗin. Rai ɓace ta baro injin saboda yarfin da malam mati ɗin yay mata a gaban yara. Tai ƙwafa kawai da ayyana rashin mutuncin da zatai masa shima.
         Sa'a ta iske a gidan tana shara, da alama ganin gidan datai kaca-kaca yasata takaici tana shigowa tahau aikinsa. “Sannu innarmu. Tun ɗazu nazo ai gida babu kowa ga ko ina kaca-kaca kamar ba mutane ke rayuwaba. Shiyyasa na hau aikin nan”.
        Baki innar ta taɓe tana ajiye ƙwaryar da tayo niƙan dawa a ciki. “Kin san dai Tinene ba moriya takesoba, ke kuma tunda kin zaɓi dangin ubanki sama dani wazai gyara mani”.
        “Kiyi haƙuri dan ALLAH Innarmu”.
     Banza tai mata. saima ƙoƙarin fara haɗa wuta a murhun data saka layun nan ta farayi, itama Sa'a sai ta cigaba da sharar tsakar gidan ranta duk babu daɗin. Bayan ta gama sharar ta tattara duka kwanika ta hau wanke-wanke da ruwan data fita ta roƙo a maƙwaftansu dan gidan ko ruwa babu. Itama Inna shita samu ta ɗiba tasa ruwan tuwo. Tsaf ta gama wanke-wanken shima ta ɗauki botiki ta fita dan dama ta gyaro ɗakunan.
       Sa'a na fita Inna ta miƙe ta ɗakko sauran kayan da malam ya bata ta ƙarasa yin yadda yace, sannan ta cigaba da hidimar girka tuwonta.
       Haka Sa'a taita kai kawon ɗibar ruwa har sai da ta cika ko ina na gidan sannan tai zaman hutawa. Sai a lokacin Tinene ta dawo gidan niƙi-niƙi da ledar kayan ƙwalam da maƙulashe. Yanda tayi tamkar bataga Sa'a bane ya bata haushi tahau zaginta, a take suka harƙume faɗa. Inna najinsu da kallonsu taƙi ta tanka sai da ta gaji da hayaniyarsu ta kora Sa'a wai ta tashi ta koma inda ta fito ita batason fitina.
       Da haushi Sa'a taja hijjabinta ta fice a gidan tana sharar hawaye......

__________________________★

*_SHIRA'S FAMILY_*

         Washe gari a bazata suka tashi da baƙuncin matar Yah Adnan. Lokacin duk suna dining suna karyawa saboda masu fita makaranta. Sai dai shi bandashi, amma yana zaune a falon shi da Khalipha suna magana akan wasu takardu dake baje a centre table ɗin falon, shi yanata danna lap-top Khalipha na gefensa yana masa magana da takarda ɗaya a hannunsa.
     Kasancewarsa a falon yasa babu yawan hayaniyarsu, dan Baffah ma bayanan yayi tafiya tun shekaran jiya. Iyakar sune kawai a falon suna taya Zinneerah murnar wayarta kowa na ƙoƙarin saka mata Number ɗinsa.
       Hajiya iya ce ta fito daga kitchen ɗin ita da baba Rahi tana faɗin, “Oh ALLAHU ni Amina. Yanzu dan ALLAH zaman latsa wayoyi zakuyi ko karin kuyi ku tafi makaranta. Sai kuma kun makara ku ishi mutane da mitar an saku makara”.
      Alamar roƙon tayi shiru suke mata wai dan kar Yayansu yaji. Basu sanma duk abinda suke tun ɗazun yana jiyosun ba. Ya sharesune kawai saboda aikin dake gabansa mai matuƙar muhimmanci ne. Suna fidda kuɗaɗen da zasuyi ginin company shinkafa ne da waken suya. Shiyyasa tun jiya yake busy. Da niyyar yin noman shinkafar kawai yazo Nigeria, sai dai Dr Mahmud da Khalipha sun canja masa tunani da shawarar mizai hana ya buɗe company kawai tunda dai yanzu Alhmdllh noma ya fara farfaɗowa a arewan. Ya yarda da Dr Mahmud sosai, dan ya jima yana bashi shawara tai masa amfani kuma, Shiyyasa ya amince babu wani ja'inja ya fara shirye-shiye. hakama Khalipha na hannun damarsane, akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu kasancewarsa mutum maison ƴan uwansa. Kosu sauran yaran gidan gama fahimtarsane kawai basu yiba, shiyyasa suke nuna tsoronsa da ganin tsaurinsa a garesu, dan da shima Khalipha hakanne a tsakaninsu, sai a ɗan zaman da yake tare da shi yanzu London ya fahimci yayansu mutumne mai sauƙin kai da haƙuri, sakewace dai kawai baida ita ga mutane sai wanda yaso. A yanzu haka suna kan yin cinikin wani fili ne da za'a fara ginin company ɗin.
       A fusace Hajiya Iya tace, “Anƙi ai shirun dan ubanku”.
     Bakuna suka shiga turawa gaba, dan duk ɗinsu sukanji haushi idan ta zagar musu iyaye. Yanda sukayinne ya sata hararsu ta koma kitchen.
      Baki Ni'ima ta buɗe baki zatai magana ƙarar takun takalma masu azabar tsini suka katseta. Su dukansu ƙofar suka zubama idanu banda shi da yayma wajen kallo guda ya maida kansa ga aikinsa duk da baisan wanene ba.
       “Hii Guys!!”. Ta faɗa dai-dai tana shigowa cikin falon.
      Duk idanu suka waro waje na mamakin ganinta matuƙa, dan badan ma akwai hotunan bikinta da Yayansu a gidanba, babu yanda za'ai su iya ganeta. Cikin ƙarfin hali Khalipha ya miƙe yana murmushi da faɗin, “Woow Aunty Farah Surprise Kece tafe haka?”.
         Ɗan yatsine fuska tai tana wani yarfar da hannu gefe da juya idanunta manya masha ALLAH, “Oh ko bakuyi murnar ganinaba na koma?”. Tai maganar tana kafe Khalipha daya nufeta da ido. Amsar handbag ɗinta yayi da cewa, “No. no auntynmu, taya zamu ƙiyin murnar ganinki bayan duk gidanan ƙishirwar ganinki sukeyi daman”.
      “Oh nice”.
  Ta faɗa cike da yanga tana sauke idanunta kan mai gayya mai aiki da yay mata kallo guda tun shigowarta ya maida kansa. Inda yake ta nufa cikin takunta na izza da tsantsar gayu da yanga mai gauraye da wayewa. “I miss you my hero”. Ta faɗa tana kaiwa duƙe ta sumbaci gefen fuskarsa na dama. Tare da nufar bakinsa da ware duka hannayenta zata rungumesa............✍

*_Wa yaga ƙawar su aunty Shahudah ƴar turawa😜😂😂_*

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘

*_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖

*_★ DALAAL_*💝

*_★ UBAYD MALEEK_*💓

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*     

*_TYPING📲_*

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 23*

______________________

_*YERWA INCENSE & MORE**_
_(The scents with diff essence for YOU& your HOME)_

_(MASARAUTAR KAMSHI)_

_Ina masu neman kayayyakin kamshi yan nahiyar ketaran chadi da Senegal? Kai harma da ingataccen had’i yan bornu? To ku matso domin nesa tazo kusa..._

_YERWA INCENSE & MORE: Sun zo muku da kayayyakin turaruka kamar haka:_

_Khumra kowacce Iri._
_Turarukan Wuta_
_Mopping khumrah_
_Washing khumrah_
_Bathing khumrah_
_body mist_
_kullaccam_
_scented hair cream/spray_
_wardrobe balls_

_carpet spray_
_air-fresheners_
_scented pebbles_
_body sprays_
_oil perfumes_
_Perfumes_

_kabbasa_
_burners_
_coal igniter_
_tong_
_kasko_
_kujerar tsugunno_
_english coal_
_dilke&halwa set_
_scented body mist_

_kai dama sauran kayayyakin da bamu ambata ba, YERWA INCENSE AND MORE, Na tura kayayyakin su ko’ina a fadin Nigeria da ketare. Domin tuntubar su. Suna instagram: _@yerwaincense_and_more. Ko _Facebook site:YERWA _COLLECTIONs. Ko a duba su ta number su: ___08095215215/09044191709! _

_suna bada kayan su kan sari ko sayi dai-‘dai_

_______________________

*Page 23*
Chapter 51 · 0% Book details