← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 123 OF 155

Sashe 123

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

         Duk da ya haɗa bayanai masu yawa akanta lokacin da yazo babbar gaɓar mallakarta da iyakar jarumtarsa yaje, sai dai samun hanyarsa ɓam ta sakashi jin wani irin zazzafan tausayinta da ƙaunarta mai tarin yawa da tsanani na shigar gaɓɓansa. Ba tare da tuna son binta a matakin tausayawaba ya ji saukar ƙarar kukanta cikin kunnensa, dan a gigice ta ƙwala kiran hajiya iya da Maman Sadiq tana ƙanƙamesa jikinta na wani irin mahaukacin rawa data sakashi ƙanƙameta shima ya manne bakinsa da nata...........

         Da ƙyar take fitar da numfashi hawaye masu matuƙar zafi da tausayin kanta na sakko mata. Bata taɓa sanin Yayansu mugu bane sai yau, ita kanta batasan adadin kuka da roƙon datai masaba, zata iya rantsewa har suma tayi na wucin gadi ta farfaɗo amma bai shirya barintaba sai da yakai inda yake buƙatar zuwa. Hannunsa dake damƙe da nata ya ɗan matsa da mirginowa ya rungumeta gaba ɗayanta a cikin jikinsa yana bata wasu irin hort kissis da ita kanta tasan na tsantsar ƙauna ne a gareta.
      “Thanks you, thanks you, thanks you” kawai yake jera mata hawayen tausayinta na taruwar masa a idanunsa. Dan duk da kasancewarsa mutum mai tsananin jarumta da kakan daɗe bakaga kuka daga idaniyarsaba yau yaji tausayi mai tsanani akan Zinneerah, saboda abubuwa masu yawan gaske dake zuwa masa arai game da haihuwa da rainon cikin Little da tayi. Sunanta ya ɓaci ta yanda ba lallai kowa ya yarda da ita ɗari bisa ɗariba koda yayi ƙoƙarin fallasama duniya gaskiyarta. Tayi kuka, tayi wahala, tayi ciwo, ta rabu da garinta, ta rabu da mahaifinta, ta rabu da ƴan uwanta, ta rabu da farin cikinta duk a dalilin cikin ɗansa da batasan mafarinsaba. Dolene ya godema ALLAH daya ƙaddara yarinyarnan kasancewa matarsa ba wani daban can ta auraba. Yayi alƙawarin zai jiyar da ita daɗin duniya gwargwadon ƙwazonsa har sai ta san itaɗin ta musamman ce a garesa kuma mutum mai daraja. Dolene ya sanarma duniya wacece ita? Dolene ya wanketa ga mutane koda bazasu yardaba ya tabbatar musu da *_MAKAUNIYAR ƘADDARAR_* data jefa rayuwarta cikin hajijiyar rayuwa badan ta shiryama zuwanta ko karɓartaba itama. “I'm so sorry Neerat”.
     Ya sake faɗa a cikin kunnenta hawayenta na sauka har bisa fuskarsa suna gaurayuwa da nasa na tsananin tausayin da yake mata dajin zafin zalunci mafi muni da akaima rayuwarta.
        Cikin kuka tace, “Yayanmu ruwa. Ruwa zansha”.
     A hankali ya ɗago kansa yana kallon fuskarta data kacame da hawaye, idanun sunyi luhu-luhu yana kallonta. Goshinta ya sumbata a hankali yace, “Ruwa kike so?”.
     Kanta ta ɗan juya masa a hankali itama tana matso wasu sabbin hawayen. Hannu yasa ya share mata su. “Tom ya isa haka kinji, banason kukannan zai saki ciwon kai. ALLAH yay miki albarka uhmyim”.
        Kanta ta maida gefe tana ƙoƙarin haɗiye kukan amma ta kasa. Raba jikinsa yay da nata da ƙyar ya jawo rigarsa ya saka, sakkowa yay daga gadon ya fita ɗakko mata ruwa dan yau ko shigowa dashi baiyiba ya manta.
      A yanda ya barta haka ya sameta. Zama yay ya jingina da gadon sannan ya ɗagota jikinsa, ta saki karamar ƙarar azabar da wajen ke mata. Ruwan ya saka mata a baki yana ambaton, “Sorry sha ruwan muje ki shiga ruwan zafi”.
      Sosai tasha ruwan wata sabuwar zufa na keto mata. Ta lafe a jikinsa tana lumshe idanu da sauke numfarfashin wahala. Idan zata iya tunawa bayan rainon cikin little da naƙudarsa data sha kafin ai mata cs bata taɓa jin abu mai azaba makamancin wanda taji yau a hannun Yah Abdul-Mutallab ba. Ta jigatu matuƙa irin jigatuwar da mantata gareta abune mai wahalar gaske. Tana tausayin mace a rayuwarta, da ace mata zasu nutsu su ajiye duk wani shirme da ruɗanin huɗubar sheɗan da tabbas wasu abubuwa ƙalilian dake zama wajib a rayuwarsu kawai sun isa zama sanadin kaisu aljannah. Yanzu da irin wannan daren kawai aka barka ai ba ƙaramin abin tashin hankali bane, balle akwai rainon ciki, uwa uba naƙuda da babu abinda za'a iya misaltata da shi. Ga fitar rai, Raino, hidimar gidan aure da ƙalubalensa.
        (Kai jama'a mata masu duniya, mata sarakan duniya, mata na gaisheku, na gaisheku gaisuwa irin ta girma da mutuntawa dan kun cancanci a yaba muku, ku ƙara haƙuri jaruman duniya, ku cigaba da haƙuri taurarin duniya, kuzama masu haƙuri ALLAH zai sakanka muku da aljannarsa😍😘).
Chapter 123 · 0% Book details