Sashe 79
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daɗi sosai AK yaji akan hukuncin Mahma, danshi kanshi a yanzu filin yin nazari yake buƙatar samu akan wannan al'amarin, ALLAH shine shaidarsa bai taɓa aikata zina da ƴar kowa ba, shi baima taɓa ganin Zinneerah ba sai a gidansu wannan zuwan. Amma gashi Baffah kansa zargin yaron nasane yake. Kai shi kansa da kansa zargin kansa yake dan kamaninsa da yaron abun a dubane akumayi nazari. A yanzu kawai yana ganin shawarar da zuciyarsa ke bashi ya kamata yabi kozai fita daga ruɗanin da yake ciki daga shi har ƴan uwansa. Miƙewa yay batare da yacema kowa komaiba ya fice a ɗakin. Hakan yasa itama Farah dafa masa baya sai dai ɗakinta ta nufa tana kuka ba nashiba.
Hajiya iya da gaba ɗaya take jin komai yana mata nauyi a zuciya ta duba Khalipha a sanyaye tace, “Ka bisa Khalipha, kasan Moddibo bai iya ɗaukar damuwa da sauƙi ba”..
A raunane Khalipha ya jinjina mata kansa, dan shima a ruɗan yake da komai, saboda Hajiya Iya ta bashi takardar wajen mmn sadiq ya karanta ɗazun saboda fitowar sunansa a ciki. Ya kuma sanar mata gaskiyar abinda ya sani game da haɗuwarsa da Zinneerah.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_________________________
*Page 38*
............Sai da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin aka bashi izinin shiga sanna ya shigo, zaune ya sameshi cikin kujerar dake a ɗakin kansa jingine ya lumshe ido da makarinta. Bai motsaba daga yanda yake har Khalipha ya zauna a ɗayar kujerar dake kallonsa cike da tausayin ɗan uwan nasa. ɗan jimm yayi na wasu sakanni kafin yay ƙasa da kansa cikin lallashi yace, “Yayanmu dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, insha ALLAH bin komai a sannu zai warware dukan aninda zuciya ke hasashe duk rintsi”.
Wani ɗan murmushi AK ya saki yana buɗe idanunsa da gaba ɗaya launinsu ya canja, sai da ya yima Khalipha kallon wasu sakanni kafin ya tashi zaune sosai yana furzar da abinda ya tokare maƙoshinsa mai ɗaci. Cikin son danne duk damuwarsa yace, “Bestie dama kasanta?”.
Ɗan kallonsa Khalipha yay alamar wa?.
Idanunsa ya lumhe ya buɗe akansa, kamar bazai sake tankawaba sai kuma ya furta, “Zinneerah!”. A saman laɓɓansa.
A bazata Khalipha ya saki murmushi, a ransa ko gulma yake (kai yayanmu kako iya faɗar sunan). A fili kam sai ya gyaɗa masa kai tare da ƙara nutsuwa sosai. “Nasanta Yayanmu, amma sanin na kwanaki goma zuwa sha ɗaya ne kacal idan ban mantaba. (A take ya fara bashi labarin haɗuwarsu a randa aka bigeta, wanda a dalilin aiken da yay masanema yaje jigawan, suna hanyar dawowa motar ta samu matsala. ya baro wanda sukaje taren da motar shiko yabi ta haya dan zuwa ya isar da saƙon karsu makara tunda yasan jira yakeyi).
“Wannan shine dalilin dayasa na santa Yayanmu, ni duk zatona ma tanada aure wlhy, shiyyasa ban wani taɓa maida hankali akanta ba, inma baka mantaba na baka labarin accident ɗin ai a wancan lokacin. kuma ni a zuwan nan da mukaima sai ban ganetaba saboda duk ta canja, sai randa naga Gwaggo (Mmn sadiq) sannan na ƙara tabbatar da itace, inataso muyi maganama hakan bai faruba saboda ciwon Granny”.
Ɗari bisa ɗari AK ya yarda da Khalipha, dan yason bai iya ƙaryaba, tunda suke dashi bai taɓa kamashi da wani abu na rashin gaskiya ba, zamansa ya gyara da ƙyau yana furzar da numfashi, cikin tsatstsare Khalipha da idanu yace, “Miye amsata ta ɗazun game da kamannina da yaro?”.
Ƙasa Khalipha yay da kansa cike dajin nauyin gaskiyar abinda ke a ransa. Muryarsa a dakushe yace, “Yayanmu al'amarin akwai rikitarwa, harga ALLAH banida takamaimai amsa, dan bayan matarka nine mutum na biyu da zan iya bada shaida akanka, hakan yasa duk abinda zuciyata zata iya hasasomin ƙwaƙwalwata bazata iya ɗaukaba, shawara ɗayace shine ai gwaji kawai, maybe hakan ya kawo hasken da kowa zai iya fahimtar bakin zaren. Ka gafarceni idan nayi kuskure”.
Murmushi AK ya sake saki mai sanyi yana gyaɗa kansa. Cikin nuna gamsuwar zantukan Khalipha yace, “Shiyyasa nake kiranka Bestie, dan mafi yawan tunaninka irin nawane, inason mutum mai gaskiya da ƙyaƙyƙyawan nazari akan komai Khalipha. ALLAH yay maka albarka, nima a raina shawarar zuwa Nigeria nake domin gwada ƙwayoyin halitarmu ni da yaron, maybe hakan zaisa na iya tuna wani abu dana manta ko samun ƙwarin gwiwar bakin zaren”.
Khalipha dake murmushi yana jinjina masa kai yace, “Nagode Yayanmu”.
“Nizan gode maka ai, dan ka zama ɗan uwa ɗaya tamkar da dubu. Yanzu kaje ka huta kaima, sai dai banason ka sanarma Granny tafiyata, sai na gama shiri zan sanar mata, insha ALLAH nanda awanni biyar zan wuce”.
Cikin waro idanu Khalipha yace, “Yayanmu ince sai nan da kamar kwana biyu?”.
Kai kawai ya girgizama Khalipha yana miƙewa da murmushi akan fuskarsa. Ganin ya nufi toilet shima sai Khalipha ya miƙe ya fita cike da tausayin Yayan nasu, ya tabbatar jarumtarsa da ƙoƙarin iya shanye damuwane kawai ya danne dukkan halin da yake ciki, amma duk wanda ya sanshi ya kalli ƙwayar idonsa yasan baya cikin kwanciyar hankali. (Ya ALLAH ka kawo mana mafita, ka haska mana duhun da muke ciki domin rahamarka ya UBANGIJI). Khalipha ya faɗa yana nufar ɗakinsa zuciyarsa cike da rauni da ɗaci. Har ransa kuma yanajin zai iya auren Zinneerah koda ace ƴaƴa goma ta haifa, amma yanason jin ta bakinta itama harga ALLAH.
★★
Tun bayan fitar Khalipha a ɗakin babu wanda ya sake jin ɗuriyar AK a gidan sai bayan awannin daya ambata ma Khalipha na wucewa 9ja. Duk da halin da yake ciki na tsananin ciwon kai dana zuciya jarumtarsa ta shanye kaso mafi yawa. Sam bazaka iya hasaso damuwarsa a saman fuskaba, sai dai idan ka masa sanin ƙwarai a kallo ɗaya zaka gano damuwar cikin ƙwayoyin idanunsa da rauninsu ya bayyana ƙuru-ƙuru.
A falo ya samu su Jamal nacin abinci su uku. Yay musu kallon nazari ganin yanda suke kowa fuska da damuwa ya ɗauke kansa. Sai da yazo dab dasu suka farga da shi saboda motsin takunsa da yawaitar ƙamshin turarensa. Gaishesa sukayi, ya amsa musu yana wucewa ɗakin hajiya iya.
Koda ya shigo bayan sallamar da yayi baiji an amsaba bai samu kowa a ɗakinba sai Zinneerah dake kwance tana barci har yanzun. Hanyar toilet ya ɗan duba saboda jin motsin ruwa, da alama Granny ce a ciki. Ya ɗauke kansa yana maidawa ga Zinneerah. Bayanta kawai yake iya gani, dan haka ya taka a hankali zuwa inda ta juya fuskarta, kansa tsaye ya zuba mata fitinannun idanunsa dake cike da abubuwa masu yawa a wannan yinin, kallo yake mata irin na ƙurulla da bai taɓa matashiba, ya kai tsahon minti ɗaya da wasu sakanni a haka kafin ya matso dab da ita, ahankali yaɗan ranƙwafo kanta, tare da kai hannusa a fuskarta ya janye mata jelar gashinta daya zubo biyu da akai mata kalba da ɗan yatsansa manuniya.
Motsawa tayi alamar zatai juyi. Kauda kansa yayi yanaja da baya kamar bashi ya aikataba. A dai-dai nan Granny ta fito.
“Lafiya kuwa na ganka da jikka moddibo?”.
Juyiwa yay ya dubeta, kansa tsaye yace, “Zanje Nigeria ne Granny”.
“Nigeria kuma? Akanmi to?”.
“Akan abubuwa da yawa. Kimin addu'a ke dai”.
“To addu'a kam kullum cikin yimuku ita muke Moddibo, amma daka sanar dani nikam da tare muka wuce, dan zaman garin nan fa ya isheni”.
Guntun murmushi yayi yana matsawa inda take. Ya kamo hannunta, cike da lallashi yace, “Kiyi haƙuri kinsan baki gama ganin likitaba, nima bawani jimawa zanyiba inagama 2days zanyi insha ALLAH”.
“To ALLAH yasa haka. Amma wannan birkitacciyar matar taka tare zaku tafi? Dan bazaka barmana ita nanba”.
Maganar tata ta bashi dariya. sai dai baiyiba. hannunta ya saki da faɗin, “Matar tawace birkitacciya Granny? To ai duk birkicewarta kin iya da ita na sani. Karki damu babu abinda zai faru insha ALLAH”. Ya ƙare maganar yana ɗan duban inda Zinneerah take ya ɗauke kansa.
Duk da hajiya iya batasan manufar tafiyar tasaba bataso ya tafi ya barta ananba. Amma duk da haka sai tai masa fatan alkairi da gargaɗin karfa yaje yay zamansa.
Shidai fita yay kawai yana ɗan murmushi. Yasan ko mi zaiyi Farah bazata sauraresaba a yanzun, dan haka baibi takantaba dan ya bar mata saƙo a ɗakinsa. A falo ya tsaya ya aika Jamal kiran Khalipha. Babu jimawa kuwa sai gashi ya fito cikin shiri.
Tare suka fita shi da Jamal da Khalipha ɗin da zasu masa rakkiya airport.
_____________★
Zinneerah batasan da tafiyar AK ba, koda ta tashi kuma su Khalipha sun dawo gida. Kowa yaji daɗin yanda ta farka normal, sai dai jikinta duk a sanyaye, komai yinsa take kamar mara ƙashi a jiki, gashi sam bata da walwala. Abinci ma sai da Hajiya iya ta takura mata sannan tacisa tasha ruwan addu'oin da tai mata tun ɗazun kamar yanda Mahma ta faɗa.
Ta farka da abubuwa masu yawa a cikin rai. sai dai miskilancinta da rashin son nuna damuwa akan abu ya shanye kaso mafi yawa, dan haka yanayin ya rikiɗe mata kawai zuwa sanyin jiki da rashin son hayaniya.
Hajiya iya da gaba ɗaya take jin komai yana mata nauyi a zuciya ta duba Khalipha a sanyaye tace, “Ka bisa Khalipha, kasan Moddibo bai iya ɗaukar damuwa da sauƙi ba”..
A raunane Khalipha ya jinjina mata kansa, dan shima a ruɗan yake da komai, saboda Hajiya Iya ta bashi takardar wajen mmn sadiq ya karanta ɗazun saboda fitowar sunansa a ciki. Ya kuma sanar mata gaskiyar abinda ya sani game da haɗuwarsa da Zinneerah.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_________________________
*Page 38*
............Sai da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin aka bashi izinin shiga sanna ya shigo, zaune ya sameshi cikin kujerar dake a ɗakin kansa jingine ya lumshe ido da makarinta. Bai motsaba daga yanda yake har Khalipha ya zauna a ɗayar kujerar dake kallonsa cike da tausayin ɗan uwan nasa. ɗan jimm yayi na wasu sakanni kafin yay ƙasa da kansa cikin lallashi yace, “Yayanmu dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, insha ALLAH bin komai a sannu zai warware dukan aninda zuciya ke hasashe duk rintsi”.
Wani ɗan murmushi AK ya saki yana buɗe idanunsa da gaba ɗaya launinsu ya canja, sai da ya yima Khalipha kallon wasu sakanni kafin ya tashi zaune sosai yana furzar da abinda ya tokare maƙoshinsa mai ɗaci. Cikin son danne duk damuwarsa yace, “Bestie dama kasanta?”.
Ɗan kallonsa Khalipha yay alamar wa?.
Idanunsa ya lumhe ya buɗe akansa, kamar bazai sake tankawaba sai kuma ya furta, “Zinneerah!”. A saman laɓɓansa.
A bazata Khalipha ya saki murmushi, a ransa ko gulma yake (kai yayanmu kako iya faɗar sunan). A fili kam sai ya gyaɗa masa kai tare da ƙara nutsuwa sosai. “Nasanta Yayanmu, amma sanin na kwanaki goma zuwa sha ɗaya ne kacal idan ban mantaba. (A take ya fara bashi labarin haɗuwarsu a randa aka bigeta, wanda a dalilin aiken da yay masanema yaje jigawan, suna hanyar dawowa motar ta samu matsala. ya baro wanda sukaje taren da motar shiko yabi ta haya dan zuwa ya isar da saƙon karsu makara tunda yasan jira yakeyi).
“Wannan shine dalilin dayasa na santa Yayanmu, ni duk zatona ma tanada aure wlhy, shiyyasa ban wani taɓa maida hankali akanta ba, inma baka mantaba na baka labarin accident ɗin ai a wancan lokacin. kuma ni a zuwan nan da mukaima sai ban ganetaba saboda duk ta canja, sai randa naga Gwaggo (Mmn sadiq) sannan na ƙara tabbatar da itace, inataso muyi maganama hakan bai faruba saboda ciwon Granny”.
Ɗari bisa ɗari AK ya yarda da Khalipha, dan yason bai iya ƙaryaba, tunda suke dashi bai taɓa kamashi da wani abu na rashin gaskiya ba, zamansa ya gyara da ƙyau yana furzar da numfashi, cikin tsatstsare Khalipha da idanu yace, “Miye amsata ta ɗazun game da kamannina da yaro?”.
Ƙasa Khalipha yay da kansa cike dajin nauyin gaskiyar abinda ke a ransa. Muryarsa a dakushe yace, “Yayanmu al'amarin akwai rikitarwa, harga ALLAH banida takamaimai amsa, dan bayan matarka nine mutum na biyu da zan iya bada shaida akanka, hakan yasa duk abinda zuciyata zata iya hasasomin ƙwaƙwalwata bazata iya ɗaukaba, shawara ɗayace shine ai gwaji kawai, maybe hakan ya kawo hasken da kowa zai iya fahimtar bakin zaren. Ka gafarceni idan nayi kuskure”.
Murmushi AK ya sake saki mai sanyi yana gyaɗa kansa. Cikin nuna gamsuwar zantukan Khalipha yace, “Shiyyasa nake kiranka Bestie, dan mafi yawan tunaninka irin nawane, inason mutum mai gaskiya da ƙyaƙyƙyawan nazari akan komai Khalipha. ALLAH yay maka albarka, nima a raina shawarar zuwa Nigeria nake domin gwada ƙwayoyin halitarmu ni da yaron, maybe hakan zaisa na iya tuna wani abu dana manta ko samun ƙwarin gwiwar bakin zaren”.
Khalipha dake murmushi yana jinjina masa kai yace, “Nagode Yayanmu”.
“Nizan gode maka ai, dan ka zama ɗan uwa ɗaya tamkar da dubu. Yanzu kaje ka huta kaima, sai dai banason ka sanarma Granny tafiyata, sai na gama shiri zan sanar mata, insha ALLAH nanda awanni biyar zan wuce”.
Cikin waro idanu Khalipha yace, “Yayanmu ince sai nan da kamar kwana biyu?”.
Kai kawai ya girgizama Khalipha yana miƙewa da murmushi akan fuskarsa. Ganin ya nufi toilet shima sai Khalipha ya miƙe ya fita cike da tausayin Yayan nasu, ya tabbatar jarumtarsa da ƙoƙarin iya shanye damuwane kawai ya danne dukkan halin da yake ciki, amma duk wanda ya sanshi ya kalli ƙwayar idonsa yasan baya cikin kwanciyar hankali. (Ya ALLAH ka kawo mana mafita, ka haska mana duhun da muke ciki domin rahamarka ya UBANGIJI). Khalipha ya faɗa yana nufar ɗakinsa zuciyarsa cike da rauni da ɗaci. Har ransa kuma yanajin zai iya auren Zinneerah koda ace ƴaƴa goma ta haifa, amma yanason jin ta bakinta itama harga ALLAH.
★★
Tun bayan fitar Khalipha a ɗakin babu wanda ya sake jin ɗuriyar AK a gidan sai bayan awannin daya ambata ma Khalipha na wucewa 9ja. Duk da halin da yake ciki na tsananin ciwon kai dana zuciya jarumtarsa ta shanye kaso mafi yawa. Sam bazaka iya hasaso damuwarsa a saman fuskaba, sai dai idan ka masa sanin ƙwarai a kallo ɗaya zaka gano damuwar cikin ƙwayoyin idanunsa da rauninsu ya bayyana ƙuru-ƙuru.
A falo ya samu su Jamal nacin abinci su uku. Yay musu kallon nazari ganin yanda suke kowa fuska da damuwa ya ɗauke kansa. Sai da yazo dab dasu suka farga da shi saboda motsin takunsa da yawaitar ƙamshin turarensa. Gaishesa sukayi, ya amsa musu yana wucewa ɗakin hajiya iya.
Koda ya shigo bayan sallamar da yayi baiji an amsaba bai samu kowa a ɗakinba sai Zinneerah dake kwance tana barci har yanzun. Hanyar toilet ya ɗan duba saboda jin motsin ruwa, da alama Granny ce a ciki. Ya ɗauke kansa yana maidawa ga Zinneerah. Bayanta kawai yake iya gani, dan haka ya taka a hankali zuwa inda ta juya fuskarta, kansa tsaye ya zuba mata fitinannun idanunsa dake cike da abubuwa masu yawa a wannan yinin, kallo yake mata irin na ƙurulla da bai taɓa matashiba, ya kai tsahon minti ɗaya da wasu sakanni a haka kafin ya matso dab da ita, ahankali yaɗan ranƙwafo kanta, tare da kai hannusa a fuskarta ya janye mata jelar gashinta daya zubo biyu da akai mata kalba da ɗan yatsansa manuniya.
Motsawa tayi alamar zatai juyi. Kauda kansa yayi yanaja da baya kamar bashi ya aikataba. A dai-dai nan Granny ta fito.
“Lafiya kuwa na ganka da jikka moddibo?”.
Juyiwa yay ya dubeta, kansa tsaye yace, “Zanje Nigeria ne Granny”.
“Nigeria kuma? Akanmi to?”.
“Akan abubuwa da yawa. Kimin addu'a ke dai”.
“To addu'a kam kullum cikin yimuku ita muke Moddibo, amma daka sanar dani nikam da tare muka wuce, dan zaman garin nan fa ya isheni”.
Guntun murmushi yayi yana matsawa inda take. Ya kamo hannunta, cike da lallashi yace, “Kiyi haƙuri kinsan baki gama ganin likitaba, nima bawani jimawa zanyiba inagama 2days zanyi insha ALLAH”.
“To ALLAH yasa haka. Amma wannan birkitacciyar matar taka tare zaku tafi? Dan bazaka barmana ita nanba”.
Maganar tata ta bashi dariya. sai dai baiyiba. hannunta ya saki da faɗin, “Matar tawace birkitacciya Granny? To ai duk birkicewarta kin iya da ita na sani. Karki damu babu abinda zai faru insha ALLAH”. Ya ƙare maganar yana ɗan duban inda Zinneerah take ya ɗauke kansa.
Duk da hajiya iya batasan manufar tafiyar tasaba bataso ya tafi ya barta ananba. Amma duk da haka sai tai masa fatan alkairi da gargaɗin karfa yaje yay zamansa.
Shidai fita yay kawai yana ɗan murmushi. Yasan ko mi zaiyi Farah bazata sauraresaba a yanzun, dan haka baibi takantaba dan ya bar mata saƙo a ɗakinsa. A falo ya tsaya ya aika Jamal kiran Khalipha. Babu jimawa kuwa sai gashi ya fito cikin shiri.
Tare suka fita shi da Jamal da Khalipha ɗin da zasu masa rakkiya airport.
_____________★
Zinneerah batasan da tafiyar AK ba, koda ta tashi kuma su Khalipha sun dawo gida. Kowa yaji daɗin yanda ta farka normal, sai dai jikinta duk a sanyaye, komai yinsa take kamar mara ƙashi a jiki, gashi sam bata da walwala. Abinci ma sai da Hajiya iya ta takura mata sannan tacisa tasha ruwan addu'oin da tai mata tun ɗazun kamar yanda Mahma ta faɗa.
Ta farka da abubuwa masu yawa a cikin rai. sai dai miskilancinta da rashin son nuna damuwa akan abu ya shanye kaso mafi yawa, dan haka yanayin ya rikiɗe mata kawai zuwa sanyin jiki da rashin son hayaniya.