← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 125 OF 155

Sashe 125

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*

_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._

*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*

*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*

_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻

Available

_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil

Location
kaduna buh mn tura Kaya ko Ina saidai inmutum ya amshi kayanshi zebada kudin delivery

WhatsApp 08062991549
Call 08064532391

Instagram:glow_with_mgs

Facebook:mg's skincare

*_Karku bari ayi babu ku guys, siyan nagari maida kuɗi gida._*

________________________

*Page 59*

............Koda ya dawo bedroom ɗin wanka kawai ya shiga batare daya tada Zinneerah ba. Harko ya fito ya kammala shirinsa tsaf cikin ƙananun kayan da sukai masa matuƙar ƙyau da ƙara fidda kwarjininsa da ƙuruciya bata farkaba. Yana tsaka da saka turare ya jiyo ana danna door bell, ajiye turaren yayi ya ɗauka wayarsa da ƙarasowa gaban gadon saitin da take kwance. Wani lallausan murmushi yake saki yana ƙarema fuskarta kallo musamman bakin daya tsuƙe. A hankali ya ranƙwafo ya sumbaci bakin da hancinta da goshinta, yana motsa laɓɓansa a hankali wajen ambaton, “ALLAH ya albarkaci rayuwarki”.
     Daga haka ya fice abinsa. Yana buɗe ƙofar da Hajiya iya da Moos'ab ya kawo yaci karo. Ta zuba masa harara da faɗin, “Shegen gida kamar na ƴan yankan kai, sai ka danna ƙararrawa an gama yarfaka za'a buɗe maka”.
     “Oh-oh daga zuwanki sai neman faɗa, yi haƙuri ni yau bana faɗa”.
       “A lallai ai naga alama a goshin ka ma ja'iri mara kunya”. Hajiya iya ta faɗa tana turesa da shigowa cikin falon abinta.
    Murmushi ya ɗanyi dakai hannu ya murza goshinsa. A ransa yana faɗin ‘Mi matarnan ke nufi dani?’. Bashi da mai bashi amsa dan haka yay ƙoƙarin bin bayanta. hannunta ya riƙo ganin ta nufi sashen Zinneerah. “Kinga inda zakiyi nan madam”.
       “Kai ni sakeni naje na fara ganin Inno tukunna, haka kawai ka wani tattaromu sai kace ƴaƴanka”.
       “Uhm ke dama ba'ayi miki dai-dai, ai Innon taki na inda zan kaikin ko”.
     “Ato muje naga abuta dan nikam ban yarda da wannan munafurcin nakaba yau Moddibo”.
    Murmushi kawai yayi batare da yace mata komaiba suka nufi sashensa. Kamar jira suna isa falon saiga sallamar Haneef. Zaunar da hajiya iya yayi sannan ya amsa da cewa “Shigo da su”. 
    Kasancewar dama Haneef na tare da Mahma da  Gwaggo Maryama da duk hankalinsu ke tashe da wannan kira na AK ɗin sai ya matsa musu alamar su shiga. Shi kuma ya juya.
Chapter 125 · 0% Book details