Sashe 52
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
...........Mamakinta ya sakashi ɗago manyan idanunsa ya zubasu cikin nata. Ɗunbin al'ajabin sabon salon nata na bayyaya ƙuru-ƙuru a cikinsu. Dan wannan salon iskancin tabbas ba nata bane aroshi tayi saboda wani dalilinta.
Itama ganin yanda ya zuba mata idanunne yasa gwuyawunta yin sanyi, ta sakar masa Murmushin ƙarfin hali da cije leɓenta na ƙasa tana janye jikinta baya.
Duk da yaji ɓacin ran ganin nata bayan ya gargaɗeta jiya da daddare akan kar tazo amma tay watsi da maganar tasa tazo, ga kuma salon isanci data shigo dashi gidan alhalin hakan ba ɗabi'arta baceba sai ya basar ya sakar mata wani lallausan murmushi daya sata sauke ajiyar zuciya babu shiri.
Su Saifudden kam dake dining jin shiru ya sakasu ɗagowa daga duƙar da kawunansu da sukayi, ganin abinda sukai tunanin zatayi bashi ya faruba duk sai suka saki numfashi. Musamman da suka hangota zaune a gefensa suna kallon juna da murmushi kamar ba yayansu ba. Itama kuma kamar ba itace ta shigo da salon rawar kai ba yanzun. Ta koma Farah ɗinta da suka sani mai tsanin miskilanci a garesu da jan aji.
Cikin magana ƙasa-ƙasa da babu wanda yake iya jiyosa. Dan saima ka ɗauka wani magana mai daɗin gaske yake faɗa mata, yace, “Wannan salon bai dace da ke ba, kowaye ya baki shawarar shigowa cikin shirawa dashi ya ɗoraki a kan keken ɓera da ta zubewar mutuncikine, da sakaki a layin masu ƙarancin tarbiyya”.
Shiru kawai tai tana kallosa cikin ido, tabbas gaskiya ya faɗa mata, dan ita kanta yanda ƙannensa duk suka zubo mata ido sanda ta shigo sai taji kamar ta muzanta a cikin idanunsu.. Dama da ƙyar ta iya dauriyar hawa kan shawarar auntynta da tace ta shigo musu gidan a salon gatse-gatse zasuji shakkarta fiye da da da take musu isa da shariya kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta ɗago tana kallon sashen dining ɗin.
Ganin duk yanda sukai ƙasa da kawunansu yasa ta wani yatsine fuska tana taɓe baki, dubanta ta maida ga Yah Adnan daya sake maida hankalinsa ga aikinsa. “Baby ku baku iya tarbar baƙo bane da masauki a gidan naku?”. Tai maganar a Farah ɗinta daya sani mai tsananin son nuna isa da miskilanci.
Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin da yakeyi. Sai dai bai ɗago ya kalletaba. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yay wani guntun murmushi na takaici ya cigaba da abinda yakeyi batare daya tanka mataba.
Ganin zata ƙara magana Khalipha yay saurin tareta da faɗin, “Sorry Aunty. muko muka iya tarar baƙi. Amma muje ki gaisa da Granny first”.
“Oh no Khalipha, zan fara wanka kafin na iya gaisuwa-gaisuwa ɗin nan naku da baya ƙarewa”.
Saurin girgiza mata kai Khalipha yay yana nuna mata Yayansu da ido, dan yasan hakan da zatai ba ƙaramin kuskure bane duk da yasan itama ta sani, tunda tafi kowa sanin halin Yayan nasu ai.......
“Kai lafiya na ganku cirko-cirko?”.
Hajiya iya dake fitowa daga ɗakinta ta faɗa batare da hankalinta yakai ga Farah ba. Kafin wani ya samu damar bata amsa Farah ta miƙe tsam cikin komawa ainahin takunta ta nufi hajiya iyan. Idanu Hajiya iya ta zuba mata harta ƙaraso gareta dan ta ganeta sarai duk da zuwanta gidan uku ne kacal, kuma duk kwananta bibbiyu ta koma
“Granny barka da safiya” ta faɗa tana ɗan kai jikinta ga hajiya iyan ta rungumota kamar yanda larabawa keyi. Duk da abun yazo banbarakwai Hajiya Iya bata damuba. Dan tasan akwai banbancin al'adu da yanki a tsakaninsu, kuma ko wancan zuwan da tayiyyi haka ta dinga mata gaisuwa, shiyyasa takemata uziri idan tayi wani abun. Hannu biyu ta karɓeta tana sake faɗaɗa murmushinta. Kafin ta ɗagota tana faɗin, “Uhm lallai yau munada manyan baƙi ashe”.
Murmushi Farah tayi cikin basarwa, dan tanajin hausa ras yine saita gadama take, tafi yin larabcin ƴan Morocco da turanci.
Sai a yanzu suma yaran gidan suka fara gaidata, duk da mamakin a yanda ta shigo gidan ɗazun ya kasa barinsu. Binsu kawai take da kallo tana amsa musu a yatsine. Kowa ta gane a cikinsu tunda tanada hotunansu na biki, duk da sanda akai auren nasu su Meenal basu da wayo sosai, amma tana jin hirarsu bakin Khalipha koshi uban gayyar idan yaso, musamman idan ƙanwarsa tana tare dashi.
Kafe Zinneerah dake can ƙarshe tai da idanu, kamar zatai magana sai kuma ta basar abinta ta maida kallonta ga Khalipha da Hajiya Iya ke masa magana ya rakata ɗakin Moddibo ta huta.
Da to ya amsama hajiya iyan.
Shi dai oga na zaune har yanzu yana aikinsa kamarma ya manta dasu a falon, sai da Hajiya iya ta zauna a kusa dashi sannan ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda launin idonsa ya canjane ya sata sakin murmushi ta shafa fuskarsa.
“Babba da haƙuri aka sanshi, tunda ta kawo kanta karka wani saka damuwar hakan a ranka. Mu dama ai burinmu ta dinga shiga cikinmu a koda yaushe. Ba daɗin nisantarmu da kuke mukejiba”.
“Amma Granny sau nawa nake cemata tazo domin gaisheku tace batason zuwa. Sai yanzu dan son fitina. Wai kinmaga a yanda ta shigo gidannan da farko ma kuwa?.......”
“Shiii! ya isa, koma dai a wane dalili tazo ko ta shigo kai ka ɗaukesa ƙyaƙyƙyawa a ranka, ka kuma ɗauki ɗamarar canjata yanda kakeso duk da kayi sakaci tun farko, amma lokaci bai ƙure makaba”.
Huci ya ɗan furzar kawai yana jingina da kujera da lumshe idanunsa.
Sudai su Zinneerah da bajin mi su Hajiya iyan ke faɗaba sauri-sauri duk suka kammala cin abincinsu suka miƙe dan suna neman makara. Ɗakin hajiya iya ta nufa ɗakko school bag ɗinta, lokacin data fito su Yah Moos'ab duk sun fice, harsu Jamal ma. Da alama ita kaɗaice ta rage. Sau ɗaya ta kalli sashen da yake zaune har yanzu yanata faman aiki a lap-top, shi kaɗai ne a falon yanzun. Hajiya iya ta tashi zuwa kitchen saka su Baba Rahi haɗama Farah breakfast tare da Khalipha dake nuna musu yanda zasuyi.
Sum-sum ta wucesa a tunaninta baya ganinta saboda aikin da yake kamar ya kwashe dukan hankalinsa.
“Zonan”.
Ta tsinkayi muryarsa cikin kunnenta a bazata. A lokaci guda ƴan cikinta da jinin jikinta suka yamutsa na tsoro, tuna maganar su Jamal da sukace baya maimaita magana idan yay maka yasata nufosa. Zinneerah yarinyace mai tarin nutsuwa, sam bata da garaje akan komai, hakan yasa ko tafiya takeyi saika ɗauka yangace. sai dai sam ba haka bane, halittartace hakan. Komai nata cikin sanyi da nutsuwa bana sakarciba ko rawar kai.
Gabansa takai tsugunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Yayanmu gani”.
Batare daya ɗago daga abinda yakeba, a daƙile yace, “Ɗiba tissue ki kwashe wannan jambakin”.
Ɗagowa tai babu shiri ta kallesa tare da waro manyan idanunta masu tsananin haske, cikin suɓucewar baki tace, “Iyeee Yayanmu miye laifinsa? Malaman basa faɗa f.....”
Sai kuma tai saurin ɗora hannunta a baki saboda tuna a ida take.
A karan farko yaɗan ɗago ya dubeta, hararar data saka kayan cikinta sake hautsunawa ya wulla mata tare da maida kansa ga aikinsa. Da sauri takai hannu ta cira tissue ɗin dake a centre table ta kaisa kan bakinta ta kwashe pink lipstick ɗin da yay mata ƙyau sosai tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallarta. Cikin ɗan rawar murya tace, “Na kwashe”. Yanzun ma batare daya ɗagoba yay mata nuni da hannu alamar taje.
Tana miƙewa Hajiya iya na fitowa da ga kitchen, tabi Zinneerah ɗin da kallo. “Inno lafiya baku tafi bane?”.
Ɗan juyowa Zinneerah tayi kanta a ƙasa tace, “Eh Granny yanzu zamu tafi”. Daga haka ta fice da sauri kafin hajiya iya ta sake cewa wani abu. Duban inda yake zaune Hajiya iya da zuciyarta ke ayyana mata ba lafiyaba tayi, “Moddibo mike faruwane da Inno, ko wani abu akai mata?”.
“Waye haka?”. Ya faɗa yana ɗan ɗagowa ya dubeta. Harara ta zabga masa tana kaiwa zaune. “Kaifa wulaƙancinka yawane dashi Moddibo, ita Zinneerah ɗince baka saniba ko yau na fara kiranta Inno a gabanka?”.
Ɗan murmushi yayi hankalinsa a aikinsa, a taƙaice yace, “ALLAH ya baki haƙuri”. Daga haka yaja bakinsa ya tsuke batare daya amsa mata maganar farko ba.
Ƙwafa tayi ta miƙe da sauri ta nufito ƙofar fita danta leƙa. tana fitowa maigadi na rufe gate alamar su Zinneerah sun wuce. Dawowa tai ranta daɗan damuwar ALLAH yasa ba wanine yayma Zinneerah ɗin wani abuba mara daɗi. Koda ta dawo falon bata kulashi ba saima harar inda yake da tayi ta shige ɗakinta abinta.
Murmushi yayi a karo na biyu yana girgiza kansa. dan yaga hararar da Hajiya iyan tai masa. Ajiye lap-top ɗin yayi zai miƙe Khalipha ya fito ɗauke da tire. Yaɗan bisa da kallo harya ƙaraso inda yake. “Yayanmu ga abincin Aunty”.
Kauda kansa yayi yana ƙarasa miƙewa. Sai da ya raɓa Khaliphan zai wuce sannan ya bashi amsa da, “Ka ajiye mata anan mana ta fito taci inma zatacin”.
Sanin abinda Yayan nasu ke nufi ya sakashi yin ƙaramar dariya, ganin zai shige yace, “To kaima ai baka karya ba”.
“Karka damu Besty yau ina azumine”. Ya bama Khalipha amsa yana shigewa corridor ɗin ɗakin nasa.
Itama ganin yanda ya zuba mata idanunne yasa gwuyawunta yin sanyi, ta sakar masa Murmushin ƙarfin hali da cije leɓenta na ƙasa tana janye jikinta baya.
Duk da yaji ɓacin ran ganin nata bayan ya gargaɗeta jiya da daddare akan kar tazo amma tay watsi da maganar tasa tazo, ga kuma salon isanci data shigo dashi gidan alhalin hakan ba ɗabi'arta baceba sai ya basar ya sakar mata wani lallausan murmushi daya sata sauke ajiyar zuciya babu shiri.
Su Saifudden kam dake dining jin shiru ya sakasu ɗagowa daga duƙar da kawunansu da sukayi, ganin abinda sukai tunanin zatayi bashi ya faruba duk sai suka saki numfashi. Musamman da suka hangota zaune a gefensa suna kallon juna da murmushi kamar ba yayansu ba. Itama kuma kamar ba itace ta shigo da salon rawar kai ba yanzun. Ta koma Farah ɗinta da suka sani mai tsanin miskilanci a garesu da jan aji.
Cikin magana ƙasa-ƙasa da babu wanda yake iya jiyosa. Dan saima ka ɗauka wani magana mai daɗin gaske yake faɗa mata, yace, “Wannan salon bai dace da ke ba, kowaye ya baki shawarar shigowa cikin shirawa dashi ya ɗoraki a kan keken ɓera da ta zubewar mutuncikine, da sakaki a layin masu ƙarancin tarbiyya”.
Shiru kawai tai tana kallosa cikin ido, tabbas gaskiya ya faɗa mata, dan ita kanta yanda ƙannensa duk suka zubo mata ido sanda ta shigo sai taji kamar ta muzanta a cikin idanunsu.. Dama da ƙyar ta iya dauriyar hawa kan shawarar auntynta da tace ta shigo musu gidan a salon gatse-gatse zasuji shakkarta fiye da da da take musu isa da shariya kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta ɗago tana kallon sashen dining ɗin.
Ganin duk yanda sukai ƙasa da kawunansu yasa ta wani yatsine fuska tana taɓe baki, dubanta ta maida ga Yah Adnan daya sake maida hankalinsa ga aikinsa. “Baby ku baku iya tarbar baƙo bane da masauki a gidan naku?”. Tai maganar a Farah ɗinta daya sani mai tsananin son nuna isa da miskilanci.
Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin da yakeyi. Sai dai bai ɗago ya kalletaba. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yay wani guntun murmushi na takaici ya cigaba da abinda yakeyi batare daya tanka mataba.
Ganin zata ƙara magana Khalipha yay saurin tareta da faɗin, “Sorry Aunty. muko muka iya tarar baƙi. Amma muje ki gaisa da Granny first”.
“Oh no Khalipha, zan fara wanka kafin na iya gaisuwa-gaisuwa ɗin nan naku da baya ƙarewa”.
Saurin girgiza mata kai Khalipha yay yana nuna mata Yayansu da ido, dan yasan hakan da zatai ba ƙaramin kuskure bane duk da yasan itama ta sani, tunda tafi kowa sanin halin Yayan nasu ai.......
“Kai lafiya na ganku cirko-cirko?”.
Hajiya iya dake fitowa daga ɗakinta ta faɗa batare da hankalinta yakai ga Farah ba. Kafin wani ya samu damar bata amsa Farah ta miƙe tsam cikin komawa ainahin takunta ta nufi hajiya iyan. Idanu Hajiya iya ta zuba mata harta ƙaraso gareta dan ta ganeta sarai duk da zuwanta gidan uku ne kacal, kuma duk kwananta bibbiyu ta koma
“Granny barka da safiya” ta faɗa tana ɗan kai jikinta ga hajiya iyan ta rungumota kamar yanda larabawa keyi. Duk da abun yazo banbarakwai Hajiya Iya bata damuba. Dan tasan akwai banbancin al'adu da yanki a tsakaninsu, kuma ko wancan zuwan da tayiyyi haka ta dinga mata gaisuwa, shiyyasa takemata uziri idan tayi wani abun. Hannu biyu ta karɓeta tana sake faɗaɗa murmushinta. Kafin ta ɗagota tana faɗin, “Uhm lallai yau munada manyan baƙi ashe”.
Murmushi Farah tayi cikin basarwa, dan tanajin hausa ras yine saita gadama take, tafi yin larabcin ƴan Morocco da turanci.
Sai a yanzu suma yaran gidan suka fara gaidata, duk da mamakin a yanda ta shigo gidan ɗazun ya kasa barinsu. Binsu kawai take da kallo tana amsa musu a yatsine. Kowa ta gane a cikinsu tunda tanada hotunansu na biki, duk da sanda akai auren nasu su Meenal basu da wayo sosai, amma tana jin hirarsu bakin Khalipha koshi uban gayyar idan yaso, musamman idan ƙanwarsa tana tare dashi.
Kafe Zinneerah dake can ƙarshe tai da idanu, kamar zatai magana sai kuma ta basar abinta ta maida kallonta ga Khalipha da Hajiya Iya ke masa magana ya rakata ɗakin Moddibo ta huta.
Da to ya amsama hajiya iyan.
Shi dai oga na zaune har yanzu yana aikinsa kamarma ya manta dasu a falon, sai da Hajiya iya ta zauna a kusa dashi sannan ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda launin idonsa ya canjane ya sata sakin murmushi ta shafa fuskarsa.
“Babba da haƙuri aka sanshi, tunda ta kawo kanta karka wani saka damuwar hakan a ranka. Mu dama ai burinmu ta dinga shiga cikinmu a koda yaushe. Ba daɗin nisantarmu da kuke mukejiba”.
“Amma Granny sau nawa nake cemata tazo domin gaisheku tace batason zuwa. Sai yanzu dan son fitina. Wai kinmaga a yanda ta shigo gidannan da farko ma kuwa?.......”
“Shiii! ya isa, koma dai a wane dalili tazo ko ta shigo kai ka ɗaukesa ƙyaƙyƙyawa a ranka, ka kuma ɗauki ɗamarar canjata yanda kakeso duk da kayi sakaci tun farko, amma lokaci bai ƙure makaba”.
Huci ya ɗan furzar kawai yana jingina da kujera da lumshe idanunsa.
Sudai su Zinneerah da bajin mi su Hajiya iyan ke faɗaba sauri-sauri duk suka kammala cin abincinsu suka miƙe dan suna neman makara. Ɗakin hajiya iya ta nufa ɗakko school bag ɗinta, lokacin data fito su Yah Moos'ab duk sun fice, harsu Jamal ma. Da alama ita kaɗaice ta rage. Sau ɗaya ta kalli sashen da yake zaune har yanzu yanata faman aiki a lap-top, shi kaɗai ne a falon yanzun. Hajiya iya ta tashi zuwa kitchen saka su Baba Rahi haɗama Farah breakfast tare da Khalipha dake nuna musu yanda zasuyi.
Sum-sum ta wucesa a tunaninta baya ganinta saboda aikin da yake kamar ya kwashe dukan hankalinsa.
“Zonan”.
Ta tsinkayi muryarsa cikin kunnenta a bazata. A lokaci guda ƴan cikinta da jinin jikinta suka yamutsa na tsoro, tuna maganar su Jamal da sukace baya maimaita magana idan yay maka yasata nufosa. Zinneerah yarinyace mai tarin nutsuwa, sam bata da garaje akan komai, hakan yasa ko tafiya takeyi saika ɗauka yangace. sai dai sam ba haka bane, halittartace hakan. Komai nata cikin sanyi da nutsuwa bana sakarciba ko rawar kai.
Gabansa takai tsugunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Yayanmu gani”.
Batare daya ɗago daga abinda yakeba, a daƙile yace, “Ɗiba tissue ki kwashe wannan jambakin”.
Ɗagowa tai babu shiri ta kallesa tare da waro manyan idanunta masu tsananin haske, cikin suɓucewar baki tace, “Iyeee Yayanmu miye laifinsa? Malaman basa faɗa f.....”
Sai kuma tai saurin ɗora hannunta a baki saboda tuna a ida take.
A karan farko yaɗan ɗago ya dubeta, hararar data saka kayan cikinta sake hautsunawa ya wulla mata tare da maida kansa ga aikinsa. Da sauri takai hannu ta cira tissue ɗin dake a centre table ta kaisa kan bakinta ta kwashe pink lipstick ɗin da yay mata ƙyau sosai tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallarta. Cikin ɗan rawar murya tace, “Na kwashe”. Yanzun ma batare daya ɗagoba yay mata nuni da hannu alamar taje.
Tana miƙewa Hajiya iya na fitowa da ga kitchen, tabi Zinneerah ɗin da kallo. “Inno lafiya baku tafi bane?”.
Ɗan juyowa Zinneerah tayi kanta a ƙasa tace, “Eh Granny yanzu zamu tafi”. Daga haka ta fice da sauri kafin hajiya iya ta sake cewa wani abu. Duban inda yake zaune Hajiya iya da zuciyarta ke ayyana mata ba lafiyaba tayi, “Moddibo mike faruwane da Inno, ko wani abu akai mata?”.
“Waye haka?”. Ya faɗa yana ɗan ɗagowa ya dubeta. Harara ta zabga masa tana kaiwa zaune. “Kaifa wulaƙancinka yawane dashi Moddibo, ita Zinneerah ɗince baka saniba ko yau na fara kiranta Inno a gabanka?”.
Ɗan murmushi yayi hankalinsa a aikinsa, a taƙaice yace, “ALLAH ya baki haƙuri”. Daga haka yaja bakinsa ya tsuke batare daya amsa mata maganar farko ba.
Ƙwafa tayi ta miƙe da sauri ta nufito ƙofar fita danta leƙa. tana fitowa maigadi na rufe gate alamar su Zinneerah sun wuce. Dawowa tai ranta daɗan damuwar ALLAH yasa ba wanine yayma Zinneerah ɗin wani abuba mara daɗi. Koda ta dawo falon bata kulashi ba saima harar inda yake da tayi ta shige ɗakinta abinta.
Murmushi yayi a karo na biyu yana girgiza kansa. dan yaga hararar da Hajiya iyan tai masa. Ajiye lap-top ɗin yayi zai miƙe Khalipha ya fito ɗauke da tire. Yaɗan bisa da kallo harya ƙaraso inda yake. “Yayanmu ga abincin Aunty”.
Kauda kansa yayi yana ƙarasa miƙewa. Sai da ya raɓa Khaliphan zai wuce sannan ya bashi amsa da, “Ka ajiye mata anan mana ta fito taci inma zatacin”.
Sanin abinda Yayan nasu ke nufi ya sakashi yin ƙaramar dariya, ganin zai shige yace, “To kaima ai baka karya ba”.
“Karka damu Besty yau ina azumine”. Ya bama Khalipha amsa yana shigewa corridor ɗin ɗakin nasa.