← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 155

Sashe 23

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

          A yau kam Zinneerah ta sake tabbatarwa ashe itama mutum ce mai daraja kamar kowa, dan yanda ƴan uwanta da Mamanta suka kasance da ita ya jefa zuciyarta cikin matsanancin farin ciki. Kowa burinsa yaga dariyarta a gidan, ko yaya tai ɗan shiru sai ance mata mike damunta?. Abinci kam saita zaɓa wanda ranta keso ake bata taci.
        Dawowar maigidan kuma aka sake ninka tattalin da ake mata, dan shima da aka kaita ta gaidashi bayan yaci abinci ya huta janta yay tayi da hira cikin kulawa, tun tana ɗan noƙewa bata iya amsawa harta saki jiki dashi ta fara amsa masa. Ta jima a wajensa tare da sauran ƙannenta kafin ta dawo sashen Maman Sadiq suka cigaba da shirmensu ita da ƙanen nata.

      Haka rayuwa ta cigaba da yima Zinneerah daɗi a gidan mijin mamanta kuma kawunta, a hankali tana sakin jiki da kowa da komai nagidan. Har zuwa yau kuma da zata cika kwanaki uku babu wanda yay mata tambaya akan cikin jikinta balle jin ba'asin sanin inda ubansa yake. Itakuma bataima kowa maganaba dan addu'arta bai wucema ace kowa yaƙi tambayar tataba tunda batasan wace amsa zata basunba.
        Yau ma duk suna zaune tsakar gida gab da magriba, tunda yaran suka dawo daga islamiyya anan suka yada zango inda suka sameta tana gurzama Maman Halima kuɓewa da zatai miyar tuwon dare. Anan suka shiririce bata labari tana musu dariya da biye musu kamar yanda ta saba.
      Ƴammata ne biyu suka shigo gidan da sallama a bakinsu ciki-ciki. Sai ƙananu biyu dake biye dasu da ledoji a hannu. Idanu Zinneerah ta zuba musu kawai dan bata sansuba, hakama sauran yaran kallonsu kawai suke babu wanda yay magana. Sai Aliyu ne cikin tsalle yake faɗin, “Gasu Zainab gasu Luba”.
          Ko kallon inda Aliyun yake basuyiba suka nufi ƙofar ɗakin uwarsu, dai-dai Maman Sadiq na fitowa ne uwar tasu ta shigo itama da ɗayar yarinyar da zasuyi sa'anni da Zinneerah. Cike da fara'a a fuskar Maman Sadiq ta shiga faɗin, “A'a ƴan bikine tafe. Sannunku da zuwa”.
      A ɗan yatsine Saude da suke kira Maman Sakina ta amsa idanunta akan Zinneerah ko ƙyaftawa batayi. Ganin kallon ƙurillar da take matane ya saka Zinneerah faɗin, “Sannu da zuwa ina yini”.
     “Lafiya” tace kawai tana nufar ƙofar ɗakin nata itama.
     (Ashe tsugunne bata ƙareba kenan) Zinneerah ta ayyana a ranta zuciyarta fal tunanin waɗannan kuma daga ina?. Bata da mai bata amsa, dan haka ta miƙe dan ganin lokacin sallama yayi gashi wasu masallatan har an fara kira.
       Alwala tace su Sadiq suje suyi su tafi massallaci, ita kuma suka shige sashen Maman Halima ita dasu ƴan biyu domin gabatar da tasu sallar. Daga haka bata sake jin ɗuriyar Saude da ƴaƴanta ba a gidan, bakuma ta tambayaba har suka gama hira ta miƙe ita dasu Abdul suka nufi sashen mahaifiarsu dansu kwanta.

     Washe gari da safe bayan sallar asuba gari yay ɗan sha suka tafi gaida mutanen gidan kamar yanda Maman ta horesu. Sashen Alhaji suka fara zuwa wanda yaran gidan ke kira da Abba. Yana zaune a falonsa madaidaici da redio a hannunsa da alama kunnawa zaiyi, shigowar tasu ya sakashi ajewa yana dubansu da kulawa. Aliyu yaje jikinsa ya zauna, suko duk suka durƙusa a ƙasa suna gaidashi. Da fara'a yake amsa musu yana shafa kan Aliyu, ya ɗan duba Zinneerah da kanta ke a ƙasa, “Ɗiyata ya jiki-jikin?”.
       Takanji kunya idan sukai mata tambaya akan jikinta, ta ƙara ƙasa da kanta da cemasa “Alhmdllh Abba”. “Masha ALLAH ai haka akeso, ALLAH ya saukeki lafiya”. Daga haka ya maida hankalinsa kan Aliyu.
       Itace ta fara miƙewa, sauran yaranma duk suka miƙe suka fito a tare. Suna gab da shiga sashen Maman Halima Aliyu ma ya iso garesu da gudu yana faɗin, “Aunty! Kinga kuɗin makarantana Abba ya bani”. Juyowa Zinneerah tai tana murmushi, tace, “kace ka gode ko?”. Kansa ya kaɗa mata yana riƙo hannunta suka ƙarasa shiga sashen Maman Halima itama.
         A falo suka isketa tanama Hussaina faɗa akan zubar da suga da tai ƙasa, ganinsu ya sata dubansu tana murmushi. Itama har ƙasa suka durƙusa gaisheta, ta amsa musu da fara'a da kulawa tana tambayar Zinneerah yaya jikinta. Nanma dai cike da kunya ta amsa kanta a ƙasa. Sunɗan jima anan fiye da sashen Abba. Daga haka suka shiga na Maman Sakina.. 
       Suma dai a falon suka samesu sunata hayaniya, dan ɗakinta yafi na kowa yawan yara a gidan. Yanda suka wani watsoma Zinneerah idanu gaba ɗayansu har uwar sai duk taji ta muzanta. amma haka ta daure takai ƙasa tana gaida Maman Sakina ɗin. A ɗan yatsine ta amsa mata. Carab Luba dake kwance a kujera ta miƙe idonta akan Zinneerah. “Tab ɗi jan, jama'a wai kuna ganin abinda nake gani kuwa? Wai wannan ƴar yarinyarce da ciki”. Kusan a tare suka sheƙe da dariya, Sakina tace, “Kinsan ƴan ƙauyen nan sai a hankali, amma dubetafa sa'a tace, koma na girmeta kamar”. Cikin taɓe baki uwar tace inako sukaga hankali, ai kamar dabbobi suke basu banbance komai sai shirme. Nanma dariyar suka kwashe dashi su duka harsu Zainab ƙananu.
       Tsam Zinneerah ta miƙe daga durƙuson da tai batare da tace komaiba ta kama hannun Aliyu suka fito zuwa sashen uwarsu.
       Suna shigowa Abdul ke faɗama Mamansu abinda akaima Auntynsu a sashen Maman Sakina. Wai su Sakinar ne ke dariyar Zinneerah ƴar ƙarama da ita tanada ciki. Shine mamansu tace wai ai kusan mutanen ƙauye ba hankaline dasuba kamar tumaki suke. Ran maman Sadiq ya ɓaci, amma saita shanye bata nunaba. Hasalina batace komaiba ta cigaba da haɗa musu abin karin da takeyi. Itama Zinneerah komai bataceba tamayi kamar ba a gabanta akai abinba.
     Bayan sun kammala karyawan ne Zinneerah tahau gyaran ɓangaren kamar yanda ta saba tun zuwanta gidan, su Sadiq kuma suka shiga shirin tafiya Islamiyya dan suna hutun boko. Tsaf ta gyara ko ina ta saka musu ƙamshi, ganin komai ya mata tsaf yanda takeso sai taje itama tayi wanka. Ta fito tana cikin shiryawa Mama ta shigo ɗakin.
        Sai da ta ƙarasa abinda takeyine Mama tace, “Zauna magana nazo muyi”. Zama Zinneerah tayi inda Mama ta nuna mata babu musu, Mama taɗan sauke numfashi tana dubanta, itako kanta a ƙasa tamkar ko yaushe.
       “Zinneerah!”.
Maman ta kirayi sunanta a karo na farko. Batare data ɗagoba tace, “Na'am mama”..  
       “Zinneerah tun zuwanki gidannan nake jiran naji miya baroki da gida? Amma shiru bakice dani komaiba. Ya kamata nasani ai, sannan nasan kuma  ta yanda zamu nema mijinki shima dan yasan inda kike ko hankalinsa zai kwanta, tunda nasan duk inda yake kodan cikin dake jikinki basai samu nutsuwar zuciyaba”.
       Yawu Zinneerah ta haɗiye da ƙyar wani abu na tattarowa a ƙirjinta. Ganin taƙi magana Mama tace, “Ke nake saurare”.
       Maimakon amsa sai kawai Zinneerah ta saka mata kuka. Idanu kawai Mama ta zuba mata kamar yau ta fara ganinta, bata kawo komai a rantaba sai tunanin harda matsalar mijin ƙila ta barota da gidan.
       “Abinda ya faru ya riga ya faru, dan haka kuka baida wani amfani a yanzu. Ki sanarmin nasan madafar kamawa wajen samo mafita”.
       Yanda Mama tai maganar babu wasa ya saka Zinneerah bata amsa cikin dauriya da matsanancin tsoro. “Nima bansan ya akai na baro gida ba, nawayi garine kawai naga kaina a asibiti”
           “Nikam ban fahimceki ba, sai kimin bayani dalla-dalla”. Mama ta faɗa tana tsareta da idanu.
     Maimakon amsa sai hawaye Zinneerah ke faman sharewa. Shigowar Alhaji ya hana Mama sake cewa komai...........✍

     *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_TYPING📲_*

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*page 11*
________________________

*_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_*

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_*

*_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_*

*_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_*

_Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_.

*MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.*

*AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON*

*AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*.

*_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_*

*ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*.

*KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻

_______________________

*Page 11*
Chapter 23 · 0% Book details