← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 155

Sashe 19

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 9*
________________________

*_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_*

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_*

*_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_*

*_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_*

_Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_.

*MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.*

*AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON*

*AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*.

*_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_*

*ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*.

*KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻

_______________________

*Page 9*

..........Jin kamar ana nufo ɗakin ya sata miƙewa zumbur taja hijjab ɗinta da Khaliphan ya kawo mata saboda salla ta saka da sauri. Ƙirjinta ne ya sake ƙarfin bugawa fiye da ko yaushe lokacin da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin. Haka yakeyi mata a duk sanda zai shigo sai yayi sallama ta amsa sannan yake shigowa.
     Yanzu ma bai shigo ɗinba sai da ta amsa ya turo ƙofar ya shigo. Kallo guda tai masa tai saurin maida idanunta ƙasa saboda kwarjinin da yake mata da cika ido. Sai dai kuma luguden dakan da ƙirjinta ke mata ne ya tilastata sake ɗago kanta badan ta shirya ba. Naziru ne biye da bayansa. Sai matarsa. Sai wasu mata biyu da batasan daga inaba. Sai dai shigowar ta ƙarshen ya sakata wani irin zabura tana binta da kallon ƙurilla maiban mamaki.
       Yanda take kallon matar da yanda itama matar take kallonta tana tafiya da ƴar sassarfa ne yaja hankalin su Khalipha garesu baki ɗaya. Kusan mini ɗaya matarnan da Zinneerah na kallon juna batare da sun saniba, sai can Zinneerah ta fara janye nata tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya a ɓoye. Kanta ta maida ƙasa tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da suka cika mata ido da batasan na minene ba.
         Jin yanda ɗakin yay shiru ɗayar matar da suke tare da itama al'ajabi ke neman halakawa ta katse shirun da faɗin, “Baiwar ALLAH sannu kinji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya ƙara lafiya”.
        Kusan a tare duk sukace amin, banda matarnan mai kama da Zinneerah da gaba ɗaya hankalinta bayama tare da ita. har yanzu kuma idonta nakan Zinneerahn. Sun ƙara jajanta mata da mata addu'ar samun lafiya mai ɗorewa sukai musu sallama suka fita bayan matan nan biyu sun ajema Zinneerah kuɗi. Koda zasu fitanma matarnan tana tafiya tana waigen Zinneerah har suka fice. Shi dai Khalipha yana tsayene yana kallonsu da nazari tun shigowarsu har suka fice.
        Wayarsa da ke ring a aljihu ta sashi sauke numfashi da warware hannayensa daya harɗe a ƙirji ya cirota a aljihu. Wani lallausan murmushi ya saki wanda yay dai-dai da ɗagowar Zinneerah. Sai ko ga idanunsu cikin na juna. Tai azamar maida kanta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan ba ƙaramin dukan zuciyarta wannan murmushi nashi yayiba.
        Shikam wayar ya kai a kunne yana ɗan lumshe idonu, cikin wata murya mai ɗunbin ladabi da girmamawa yace, “Assalamu alaika Yayanmu”.
     Batajin mi ake faɗa acan ɗin, sai Khalipha ne taji ya wani sake narke murya da shagwaɓa yana faɗin, “Oh Yayanmu Please ka jirani gani nan zuwa, nifa nace zan kaika da kaina yau, nanda mintuna goma insha ALLAH ina gida”.
         Bataji mi nacan ya sake cewaba. Sai Khalipha ne ya matso gaban gadon yaɗan bubbuga yana cigaba da sauraren abinda ake faɗa ɗin daga can. Ɗago kanta tayi ta kallesa dai-dai ya sake narke fuskar tamkar wani yaro ƙarami, kokuma yana a gaban wanda yake wayar. “ALLAH Yayanmu bazanyi gudu ba, kasan mashin bakamar motaba ai, kuma zanbi ta hanyan dazan samu sauƙine fa Please ”.
        Ita dai Zinneerah ganin yana neman zauta mata kwanya taso sake maida kanta ƙasa sai yay saurin mata alama da hannu wai yana zuwa. Bai jira cewartaba ya fice da hanzari. Bin bayansa tai da kallo harya fice, tsigar jikinta na wani tashi batare da tasan daliliba. Sai kawai ta fashe da kuka.
       Kuka sosai Zinneerah taci wanda yana alaƙa da wasu baƙin al'amura a gareta, sai dai ƙuruciya ta hanata fahimtar komai. Ta zame a hankali ta kwanta tana lumshe idanunta badan barciba, sai don son samun damar tunani da wassafo matar ɗazun da takesonyi harma da tuno halin data shiga a dalilin ganin nata da wanda ta lura itama matar ta shiga saboda ganinta.

     A ɓangaren Maman Sadiq kam itama tunda suka fito daga asibitin tafiya kawai take tamkar bata cikin hayyacinta, jitake kamar ta dawo ta sake ganin Zinneerah ɗin saboda abinda takeji a ranta da dukkan magudanar jinin jikinta a dalilin tozali da yarinyar. Duk da wani ɓangare na zuciyarta na ƙwaɓarta da cewar ba haka bane ta kasa yarda sam.
       Daga Naziru har matarsa hankulansu nakanta ne suna nazarin halin da take a ciki, sai dai basuce komaiba har ya maidasu gida shima ya wuce nasa gidan da matarsa. Inda sai anan suka sami damar tattaunawa akan yanayin maman Sadiq ɗin.

        Tunda suka shiga cikin gida ta buɗe ɗakinta ta shige saita kasa zaune ta kasa tsaye, kaikawo taketa famanyi a ciki, duk da masifar kishiyarsu Saude da take jiyowa akan taƙi fita ta ɗora girkin rana ga lokacin kaima yara abincin rana makaranta ya kusa bata fito ɗinba. Sai Uwargidansu da sukaje asibiti tare ce ta jiyo tana bama Sauden amsa da “Haba dai Maman Sakina, kodan himma irinta Maman Sadiq ai yakamata ki fara tunanin anya lafiya kuwa? Amma sai ki ɓige da neman fitina daga shigowarmu gidan dai”.
         A harzuƙe da masifar da dama Sauden jira take ta hayayyaƙoma Uwargidan nasu.....
       “Yaya! Yaya! Ƴar ayi jikan nasaba”.
Muryar mai-gidan dake shigowa ta katse masifar Sauden ta koma ƙunƙuni ciki-ciki. Baibi takantaba sai uwargidan tashi dake masa sannu ya duba. “Mike faruwa kuma daga dawowarku Binta?”.
      “Babufa komai Alhaji, fitinace irin ta Saude da baƙarewa take a gidan nan ba. Kawai dan Maman Sadiq bata fito ba shine take tsogumin batazo ta ɗora abinciba wai lokacin kaima yara makaranta ya kusa”.
       Ɗan tsaki yayi yana girgiza kansa. Yace, “Ina ita Hauwa'un take?”.
      “Tana ɗakinta, inaga dai akwai abinda ke damuntane, dan tunda muka baro asibitin naga yanayinta ya canja, na bartane muzo gida taɗan huta dama ko wani abune ya tada hankalinta acan ɗin tunda wajene bana daɗin rai ba”.
     Baice komaiba ya nufi ɗakin Maman Sadiq ɗin, wadda duk tanajin mi'ake a tsakar gidan amma taƙi yin ko tari dan abinda ya isheta ya girmi fitinar Saude. Labulen ya ɗaga yana dubanta daga bakin ƙofar, yitai kamar bata gansaba, hakanne yasa ya shigo ciki yana faɗin, “Hauwa'u lafiyarki kuwa”.
       Juyowa tai ta kallesa tamkar yanzune tasan da zuwansa. Tace, “Ashe ka shigo? ALLAH yasa dai lafiya?”.
        “Ai ke za'a tambaya ko lafiya Hauwa'u? Mike faruwa ne?”.
    Tamkar jira take ya tambayeta sai ga hawaye sharrr. Zumbur ya miƙe daga ɗan zaman da yay a hannun kujera yace, “Subahanallahi, wai mike faruwa ne? Ko wani abun ya faru acan inda kukaje dubiyan?”.
      Hawayen ta share, tace, “Lallai Alhaji akwai matsala wlhy, dan ALLAH inason na sake komawa asibitin nan yanzun”.
      “Ki koma asibiti kuma? Akan wane dalili to?. Kimin bayanin dazan gane mana”.
      Wasu hawayen ta sake sharewa. Muryarta na rawar tahowar sabon kuka tace, “Alhaji yarinyarnan da mukaje dubawa wadda Nazirun ya kaɗe wlhy kamar Zinneerah, kai inamji a jikina itace duk da kuwa rabon dana ganta tun tana ƙarama”.
        Shima kansa da mamaki yace, “Zinneerah dai tamu dake a Danya?”.
      Cike da ɗanjin nauyinsa ta gyaɗa kanta, dan shi mutumne mai kara, duk da ɗan uwantane dama can, auren zumincine akai musu bayan aurenta ya mutu, ya sota tun tana budurwa ALLAH baiyi zata zama matarsaba a lokacin sai da ta fito yace shifa yana sota har yanzun. Da farko taso ta tirje dangi sukai mata caa akan rashin dacewar hakan. Dan kowa yasan irin son da ya nuna mata. Haka dole ta haƙura akayi aka kawota nan Kano gidansa dan dama can anan yake zaune shi shekara da shekaru, to gashi yanzun har ALLAH ya azurtasu da ƴaƴa uku duk maza. Tana kuma samun kulawa da soyayyar mijinta mai tsafta da saka kwanciyar hankali, ga Uwargidanta mutuniyar kirki, Saude ce dai sai a hankali, dan dama tun farko fitinar Sauden tasata son zamewa daga auren nasa.....
       “Wai tunanin mi kuma kika tafi haka ne?”.
      Kallonsa tai da sauri tana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗan girgiza kansa kawai yana miƙewa. “Kinga ki kwantar da hankalinki tunda dai tana asibitin babu inda zataje, bara na kira Nazirun anjima yazo sai mu koma insha ALLAH dan wannan ba al'amarin da za'ai wasa bane”.
     Cikin jin daɗi tace, “To Yaya ALLAH ya saka da alkairi”.
       “Saboda ƴarki ce ke kaɗai kikemin godiya kenan?”.
       Ƙasa tai da kanta tana murmushi. “A'a kayi haƙuri bankai canba”.
        Fita yay yana murmushin shima. Saude dake laɓe a jikin Window ɗinta tana irga mintunan shigarsa ɗakin taja tsaki ganin ya fito yana murmushi. Afili tace, “Shegiya munafika, zanyi maganinki a gidannan wlhy. Oho ita dai maman sadiq bama tasan tanaiba, dan bayar fitar maigidan fitowatai ta ƙara gawayi a wuta ta ɗora ruwan abinci, dan dama tunkan su fita tayi miya shiyyasa bata damu da tsegumin Sauden ba ashe.

★★★★
Chapter 19 · 0% Book details