Sashe 18
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Malam Khalipha akwai matsala kenanfa idan yarinyarnan batasan wacece ita ba, gata da ciki” Naziru ya faɗa cike da damuwa sanda suke fitowa.
Ajiyar zuciya Khalipha ya sauke yana furzar da iska. Yace, “Tabbas akwai matsala, amma ni tun daren farko da aka kawota na fahimci akwai wani ɓoyayyen al'amari tattare da ita. Dan yanda take zabura cikin dare da faɗin abarta ta tafi, da safe kuma taita barci yasa nake ganin kamar tana a wani hali. So yanzu dai sai munyi haƙuri munbi a hankali zamu kamo bakin zaren insha ALLAH”.
Numfashi Naziru ya sauke shima. ransa da damuwa yace, “Ni kuma yarinyar kama ma takemin da amaryar Yayana wlhy, sannan maganar ɗawainiyar asibin wani abune mai zaman kansa Khalipha, badan ka taimaka min ba ai bansan yaya zanyiba nikam”.
Murmushi kawai Khalipha yayi, cikin kauda maganar ƙarshe yace, “Kana nufin tana kamani da wadda kasani?”.
“Sosaima kuwa, tun jiya da aka ɗan goge mata jiki naga kamaninta da Maman Sadiq sosai wlhy. Amma dai yau zan kawo matata da yamma dan ina komawa gida da wuri irin yau ɗin, kasan mata sun fimu lura. Kaga sai muji abinda zatace itama”.
“Wannan shawaran yayi Malam Naziru, ALLAH ya jishemu alkairi”.
“Amin ya rabbi, bara nazo na wuce dan na samu damar dawowa da wuri, yau katsina zan nufa insha ALLAH. Kuma sahu ɗaya zanyi na dawo gida”.
“ALLAH ya bada nasara. Ya kuma maido mana daku lafiya”.
Godiya Naziru yayma Khalipha ya wuce. Shima Khalipha sai ya wuce nasa uzirin acikin asibitin.
★★★
Misalin ƙarfe huɗu na yamma Zinneerah na zaune a gadon jinyarta, idanunta tsaye ƙyam akan matashin cikinta, wanda yau ne karan farko data iya zaman masa wannan kallon. A duba guda da zakai mata zaka iya fahimtar ta lula duniyar tunanine. Dan har Naziru direba da matarsa sukai sallama biyu a ɗakin babu amsa.
Kallon juna sukai shi da matarsa, kafin su sake maida idanunsu ga Zinneerah wadda da'alama har yanzu batasan da shigowar tasu ba. Takowa matar Naziru tayi har inda take, ta kai hannu akan kafaɗarta tana sake rangaɗa wata sallamar. Zabura Zinneerah tayi dan kamar daga sama taji sallamar tata. Ganin Naziru tsaye a ƙofa ya saka sauke ajiyar zuciya. Ta janye hanunta data ɗora saman cikin nata tana maida dubanta ga matar Nazirun da tai tsaye ƙyam tana duban Zinneerah ɗin da alamun mamaki a fuskarta.
Kafin Zinneerah tai magana tai saurin faɗin, “Ikon ALLAH, Abban Nasiba kaga kuwa abinda nake gani?”.
Cikin nuna tamkar bai fahimceta ba yace, “Mi kika gani?”.
Ganin kallon da Zinneerah ke musu ne na alamar tsoro ya sakata wayancewa ta zauna kusa da Zinneerah ɗin tana faɗin, “Gani nai ƙanwar tawa ta lula tunani batama san da zuwan namu ba”.
A hankali Zinneerah ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da sake maida kanta ta duƙar a ƙasa.
Yayinda shi kuma Nasiru ya kasa ko motsi dan yayi zaton abinda ransa ke raya masa na kamannin yarinyar da Maman Sadiq matar tasa zata faɗa. Sai kuma yaji saɓanin hakan. Jin Zinneerah da matar tasa na gaisawa ne ya sakashi shima ƙarasowa gaban gadon ya ajiye ledan hannunsa yana dubanta da kulawa.
Itama batare data sake ɗagowa ta kallesaba ta shiga gaishesa kamar yanda ta saba. Da kulawa ya amsa mata da sake tambayarta ƙarfin jikinta. Tace taji sauƙi.
Sun jima a ɗakin tare da ita, sai dai su kaɗai suke ƴar hirarsu jefi-jefi. Zinneerah na zaune shiru tana saurarensu kanta a ƙasa. Sai da Naziru ya tambayeta ko Khalipha ya shigo? Ne ta girgiza masa akai alamar a'a kawai batare da tayi magana ba.
Fara kiraye-kirayen sallar magriba da akai ne yasa sukai mata sallama suka fito.
Suna fita ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa a gadon ta kwanta ta lumshe idanunta da sake maida hannunta akan cikinta kamar ɗazun. Batasan wane tunani zatai akan wannan cikinba a rayuwarta. Dan yazo mata a yanayin MAKAUNIYAR ƘADDARA. shin tayaya wai aka samar da shi ne? Wanene ubansa? Kodai dama cikin basai mutum yayi aure ko ya aikata iskanci ba yake samunsa?.
Wannan tunanin shine a ranta. Dan harga ALLAH ita dai tasan duk masu haihuwar garinsu sai sunyi aure. sannan idan akaga wadda batai aureba da ciki akance mata ƴar iskace mai bin maza. A yanda kuma takejin ma'anar kalmar mai-bin maza a abaki manya shine mace mai zuwa ta aikata abu mara ƙyau da namiji. To amma ita yau gashi bata a cikin duk waɗancan kason mutanen amma gata da ciki. Bata taɓa aure ba. Bakuma ta taɓa iskanci irin na waɗancan matanba. To kenan bayan waɗanan dalilan mace zata iya samun ciki ta wata sigar kenan kamar yanda itama a yanzu take tsamanin ta hakan ta sameshi?.
Lokacin da Zinneerah ke wancan tunani a waje tsakanin Naziru da natarsa kam tattaunawa sukeyi suma akan abin al'ajabin da suka gani. Dan suna fitowa Matar tasa ke faɗin, “Abban Nasiba wlhy ɗazunfa waskewa nayi dan naga yarinyar nan ta tsorata. Kasan kuwa mina gani tattare da yarinyar nan?”.
Kansa ya girgiza mata kawai batare da yace komaiba. Itama batare data damu da hakan da yayinba tace, “Wai shin kai bakaga kamarta da Maman Sadiq ɗin gidan babban yaya bane?”.
A yanzu kam gaba ɗaya ya tattara hankakinsa gareta. Cike da zumuɗi yace, “Wannan dalilin yasa na kawoki nan Faɗima. Dan inata kokwanto, kinsan akan hakan jiya har gidan Yaya naje na sake ganin Maman Sadiq kuwa?”.
“Ikon ALLAH, to amma ita yanzu ai kaga yan uwanta ko?”.
“Inafa, bata iya faɗa mana komai akantaba wlhy, da alama akwai saka hannu a al'amarinta gaskiya, dan kamar bata da isashshiyar kafiya, kamar kuma mai tare da sammu ko jinnu. Amma ni yanzu kinsan wane tunani nayi?”.
Kanta ta girgiza masa.
Ya sauke numfashi yana bin Khalipha dake fitowa daga wata baƙar mota data faka a kusa dasu da ido. Tinted glass ɗin motar yasa basuga wanda ke zaune matsayin driver ba. Sai Khalipha ɗin daketa faman ɗaga masa hannu yana murmushi har motar ta sake ficewa a harabar asibitin.
Inda su Nazirun suke ya ƙaraso yana faɗin, “A'a malam Naziru kune anan haka?”.
Cike da kallon alamar tambaya da Nazirun ke masa ya gyaɗa kansa. Dan mamakin wannan babbar motar da aka saukesa a ciki yakeyi. fahimtar hakan da Khalipha yasoyi ya sakashi yin murmushi da juyawa yana kallon motar da har ta gama ficewa a gate ɗin asibitin ta hau titi. Sake maido dubansa yay ga Naziru da shima motar ya koma kallo yanzun cike da basarwa.
“Yaya dai malam Nazir?”.
Murmushi Naziru yayi a karon farko ƙasan zuciyarsa fal saƙe-sake akan tunanin da alama Khalipha ɗan masu da shi ne. Dan shi tunma randa suka ɗakkosa a Jigawa yaso fahimtar hakan. Amma shi Khalipha kamar bayason nuna shiɗin wanine.......
Gyaran muryar da Khalipha yayine ya katse tunaninsa. Shi kuma Khalipha ya maida dubansa ga matar Nazirun suka fara gaisawa. Bayan sun gama gaisawarne Naziru yay masa bayanin itama abinda matar tasa ta faɗa game da kamannin yarinyar da matar yayan nasa.
Khalipha yace, “To inaga mafita ɗayace damu kamar akan wannan tunain naku, mizai hana kubi hanyar data dace ita matar yayan naka tazo asibitin nan ko zamu sami wani bakin zaren, idan kuma babu damar yin hakan mu haƙura har yarinyar ta samu sauƙi sosai sai mu kaita gidan yayan naka mu da kanmu”.
“Lallai wannan shawaran taka yayi Khalipha, kuma na gamsu da shi. Insha ALLAH zanyi iya duk ƙoƙarina zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu Maman Sadiq tazo asibitin nan kafin yarinyar nan ta kammala kwanakinta inaga kamar zaifi sauƙi”.
Daga Khalipha har matarsa sun gamsu da hakan, dan haka sukai sallama yay cikin asibitin su kuma suka fito don tafiya gida.
__________________★
A haka kwanaki suka cigaba da tafiya, Zinneerah na cigaba da jiyya da samun kulawa ga Khalipha, Naziru ma yana iya bakin ƙoƙarinsa ganin yazo dubata koda hidimar Khalipha ɗin da baya gajiyawa.
Sosai ta samu sauƙi, dan yanzu Alhmdllh ko zaburan daren nan nason a barta ta fita batayi saboda Khalipha bai barin asibitin da wuri saboda ita kawai. Kasancewar suna sakata barci da wuri dan ta sami hutu sosai yakan zauna yayta mata addu'oi yana tofa mata, itako bama tasan yanayiba dan tuni tayi barcinta.
Yawan kulawa da samun abinci mai inganci da takeyi yanzu ya sakata canjawa a zaman asibitin tamkar bamai zaman jinyaba. Tayi wani fresh da ita ga cikin nata nata sake nuna kansa. A duk sanda ta dubi cikin takan zauna taita kuka maiban tausayi. Dan takan rasa wane irin kalar tunani zatayi akan wannan MAKAUNIYAR ƘADDARA data riski rayuwarta?. Gaka da ciki amma bakasan ta hanyar daka samosaba balle ai tunanin wanene ubansa kuma. Ita yanzu ma da'an sallameta daga asibitin nan batasan indama ta dosaba kuma. Dan koda sha'awa bata son tunawa da Danya a ranta ma balle ai tunanin komawarta can.
Har yanzu su Khalipha basusan sunantaba, tun kuma waccan ranar basu sake neman jin wacece itaba. Tamaƙi yarda ta saki jiki dasu gaba ɗaya.
Yauma kamar kullum tana zaune a ɗakin da tab ɗin Khalipha dakan bata wai tayi game ko kallo haka danta rage kaɗaici. Game ɗin takeyi fuskarta na fidda murmushi mai ƙayatarwa, a kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin nishaɗi, shiyyasa shi kansa Khaliphan yake ɗaukar Tab ɗin ya bata dazaran ya shigo cikin asibitin. Shekaran jiyama a wajenta ta kwana.
Ɗan harbawar da zuciyarta yayi yasata dakatawa dayin game ɗin, haka yau ta tashi da wannan tsinkewar zuciya da batasan dalili ba, jin abin na ƙara ƙarfi ne ya sakata ajiye tab ɗin ta Khalipha gefe ta zame ta kwanta tana ambaton ‘hazbunallahu wani'imal wakil’ a ranta ko zataji ɗan daɗi............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Ajiyar zuciya Khalipha ya sauke yana furzar da iska. Yace, “Tabbas akwai matsala, amma ni tun daren farko da aka kawota na fahimci akwai wani ɓoyayyen al'amari tattare da ita. Dan yanda take zabura cikin dare da faɗin abarta ta tafi, da safe kuma taita barci yasa nake ganin kamar tana a wani hali. So yanzu dai sai munyi haƙuri munbi a hankali zamu kamo bakin zaren insha ALLAH”.
Numfashi Naziru ya sauke shima. ransa da damuwa yace, “Ni kuma yarinyar kama ma takemin da amaryar Yayana wlhy, sannan maganar ɗawainiyar asibin wani abune mai zaman kansa Khalipha, badan ka taimaka min ba ai bansan yaya zanyiba nikam”.
Murmushi kawai Khalipha yayi, cikin kauda maganar ƙarshe yace, “Kana nufin tana kamani da wadda kasani?”.
“Sosaima kuwa, tun jiya da aka ɗan goge mata jiki naga kamaninta da Maman Sadiq sosai wlhy. Amma dai yau zan kawo matata da yamma dan ina komawa gida da wuri irin yau ɗin, kasan mata sun fimu lura. Kaga sai muji abinda zatace itama”.
“Wannan shawaran yayi Malam Naziru, ALLAH ya jishemu alkairi”.
“Amin ya rabbi, bara nazo na wuce dan na samu damar dawowa da wuri, yau katsina zan nufa insha ALLAH. Kuma sahu ɗaya zanyi na dawo gida”.
“ALLAH ya bada nasara. Ya kuma maido mana daku lafiya”.
Godiya Naziru yayma Khalipha ya wuce. Shima Khalipha sai ya wuce nasa uzirin acikin asibitin.
★★★
Misalin ƙarfe huɗu na yamma Zinneerah na zaune a gadon jinyarta, idanunta tsaye ƙyam akan matashin cikinta, wanda yau ne karan farko data iya zaman masa wannan kallon. A duba guda da zakai mata zaka iya fahimtar ta lula duniyar tunanine. Dan har Naziru direba da matarsa sukai sallama biyu a ɗakin babu amsa.
Kallon juna sukai shi da matarsa, kafin su sake maida idanunsu ga Zinneerah wadda da'alama har yanzu batasan da shigowar tasu ba. Takowa matar Naziru tayi har inda take, ta kai hannu akan kafaɗarta tana sake rangaɗa wata sallamar. Zabura Zinneerah tayi dan kamar daga sama taji sallamar tata. Ganin Naziru tsaye a ƙofa ya saka sauke ajiyar zuciya. Ta janye hanunta data ɗora saman cikin nata tana maida dubanta ga matar Nazirun da tai tsaye ƙyam tana duban Zinneerah ɗin da alamun mamaki a fuskarta.
Kafin Zinneerah tai magana tai saurin faɗin, “Ikon ALLAH, Abban Nasiba kaga kuwa abinda nake gani?”.
Cikin nuna tamkar bai fahimceta ba yace, “Mi kika gani?”.
Ganin kallon da Zinneerah ke musu ne na alamar tsoro ya sakata wayancewa ta zauna kusa da Zinneerah ɗin tana faɗin, “Gani nai ƙanwar tawa ta lula tunani batama san da zuwan namu ba”.
A hankali Zinneerah ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da sake maida kanta ta duƙar a ƙasa.
Yayinda shi kuma Nasiru ya kasa ko motsi dan yayi zaton abinda ransa ke raya masa na kamannin yarinyar da Maman Sadiq matar tasa zata faɗa. Sai kuma yaji saɓanin hakan. Jin Zinneerah da matar tasa na gaisawa ne ya sakashi shima ƙarasowa gaban gadon ya ajiye ledan hannunsa yana dubanta da kulawa.
Itama batare data sake ɗagowa ta kallesaba ta shiga gaishesa kamar yanda ta saba. Da kulawa ya amsa mata da sake tambayarta ƙarfin jikinta. Tace taji sauƙi.
Sun jima a ɗakin tare da ita, sai dai su kaɗai suke ƴar hirarsu jefi-jefi. Zinneerah na zaune shiru tana saurarensu kanta a ƙasa. Sai da Naziru ya tambayeta ko Khalipha ya shigo? Ne ta girgiza masa akai alamar a'a kawai batare da tayi magana ba.
Fara kiraye-kirayen sallar magriba da akai ne yasa sukai mata sallama suka fito.
Suna fita ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa a gadon ta kwanta ta lumshe idanunta da sake maida hannunta akan cikinta kamar ɗazun. Batasan wane tunani zatai akan wannan cikinba a rayuwarta. Dan yazo mata a yanayin MAKAUNIYAR ƘADDARA. shin tayaya wai aka samar da shi ne? Wanene ubansa? Kodai dama cikin basai mutum yayi aure ko ya aikata iskanci ba yake samunsa?.
Wannan tunanin shine a ranta. Dan harga ALLAH ita dai tasan duk masu haihuwar garinsu sai sunyi aure. sannan idan akaga wadda batai aureba da ciki akance mata ƴar iskace mai bin maza. A yanda kuma takejin ma'anar kalmar mai-bin maza a abaki manya shine mace mai zuwa ta aikata abu mara ƙyau da namiji. To amma ita yau gashi bata a cikin duk waɗancan kason mutanen amma gata da ciki. Bata taɓa aure ba. Bakuma ta taɓa iskanci irin na waɗancan matanba. To kenan bayan waɗanan dalilan mace zata iya samun ciki ta wata sigar kenan kamar yanda itama a yanzu take tsamanin ta hakan ta sameshi?.
Lokacin da Zinneerah ke wancan tunani a waje tsakanin Naziru da natarsa kam tattaunawa sukeyi suma akan abin al'ajabin da suka gani. Dan suna fitowa Matar tasa ke faɗin, “Abban Nasiba wlhy ɗazunfa waskewa nayi dan naga yarinyar nan ta tsorata. Kasan kuwa mina gani tattare da yarinyar nan?”.
Kansa ya girgiza mata kawai batare da yace komaiba. Itama batare data damu da hakan da yayinba tace, “Wai shin kai bakaga kamarta da Maman Sadiq ɗin gidan babban yaya bane?”.
A yanzu kam gaba ɗaya ya tattara hankakinsa gareta. Cike da zumuɗi yace, “Wannan dalilin yasa na kawoki nan Faɗima. Dan inata kokwanto, kinsan akan hakan jiya har gidan Yaya naje na sake ganin Maman Sadiq kuwa?”.
“Ikon ALLAH, to amma ita yanzu ai kaga yan uwanta ko?”.
“Inafa, bata iya faɗa mana komai akantaba wlhy, da alama akwai saka hannu a al'amarinta gaskiya, dan kamar bata da isashshiyar kafiya, kamar kuma mai tare da sammu ko jinnu. Amma ni yanzu kinsan wane tunani nayi?”.
Kanta ta girgiza masa.
Ya sauke numfashi yana bin Khalipha dake fitowa daga wata baƙar mota data faka a kusa dasu da ido. Tinted glass ɗin motar yasa basuga wanda ke zaune matsayin driver ba. Sai Khalipha ɗin daketa faman ɗaga masa hannu yana murmushi har motar ta sake ficewa a harabar asibitin.
Inda su Nazirun suke ya ƙaraso yana faɗin, “A'a malam Naziru kune anan haka?”.
Cike da kallon alamar tambaya da Nazirun ke masa ya gyaɗa kansa. Dan mamakin wannan babbar motar da aka saukesa a ciki yakeyi. fahimtar hakan da Khalipha yasoyi ya sakashi yin murmushi da juyawa yana kallon motar da har ta gama ficewa a gate ɗin asibitin ta hau titi. Sake maido dubansa yay ga Naziru da shima motar ya koma kallo yanzun cike da basarwa.
“Yaya dai malam Nazir?”.
Murmushi Naziru yayi a karon farko ƙasan zuciyarsa fal saƙe-sake akan tunanin da alama Khalipha ɗan masu da shi ne. Dan shi tunma randa suka ɗakkosa a Jigawa yaso fahimtar hakan. Amma shi Khalipha kamar bayason nuna shiɗin wanine.......
Gyaran muryar da Khalipha yayine ya katse tunaninsa. Shi kuma Khalipha ya maida dubansa ga matar Nazirun suka fara gaisawa. Bayan sun gama gaisawarne Naziru yay masa bayanin itama abinda matar tasa ta faɗa game da kamannin yarinyar da matar yayan nasa.
Khalipha yace, “To inaga mafita ɗayace damu kamar akan wannan tunain naku, mizai hana kubi hanyar data dace ita matar yayan naka tazo asibitin nan ko zamu sami wani bakin zaren, idan kuma babu damar yin hakan mu haƙura har yarinyar ta samu sauƙi sosai sai mu kaita gidan yayan naka mu da kanmu”.
“Lallai wannan shawaran taka yayi Khalipha, kuma na gamsu da shi. Insha ALLAH zanyi iya duk ƙoƙarina zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu Maman Sadiq tazo asibitin nan kafin yarinyar nan ta kammala kwanakinta inaga kamar zaifi sauƙi”.
Daga Khalipha har matarsa sun gamsu da hakan, dan haka sukai sallama yay cikin asibitin su kuma suka fito don tafiya gida.
__________________★
A haka kwanaki suka cigaba da tafiya, Zinneerah na cigaba da jiyya da samun kulawa ga Khalipha, Naziru ma yana iya bakin ƙoƙarinsa ganin yazo dubata koda hidimar Khalipha ɗin da baya gajiyawa.
Sosai ta samu sauƙi, dan yanzu Alhmdllh ko zaburan daren nan nason a barta ta fita batayi saboda Khalipha bai barin asibitin da wuri saboda ita kawai. Kasancewar suna sakata barci da wuri dan ta sami hutu sosai yakan zauna yayta mata addu'oi yana tofa mata, itako bama tasan yanayiba dan tuni tayi barcinta.
Yawan kulawa da samun abinci mai inganci da takeyi yanzu ya sakata canjawa a zaman asibitin tamkar bamai zaman jinyaba. Tayi wani fresh da ita ga cikin nata nata sake nuna kansa. A duk sanda ta dubi cikin takan zauna taita kuka maiban tausayi. Dan takan rasa wane irin kalar tunani zatayi akan wannan MAKAUNIYAR ƘADDARA data riski rayuwarta?. Gaka da ciki amma bakasan ta hanyar daka samosaba balle ai tunanin wanene ubansa kuma. Ita yanzu ma da'an sallameta daga asibitin nan batasan indama ta dosaba kuma. Dan koda sha'awa bata son tunawa da Danya a ranta ma balle ai tunanin komawarta can.
Har yanzu su Khalipha basusan sunantaba, tun kuma waccan ranar basu sake neman jin wacece itaba. Tamaƙi yarda ta saki jiki dasu gaba ɗaya.
Yauma kamar kullum tana zaune a ɗakin da tab ɗin Khalipha dakan bata wai tayi game ko kallo haka danta rage kaɗaici. Game ɗin takeyi fuskarta na fidda murmushi mai ƙayatarwa, a kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin nishaɗi, shiyyasa shi kansa Khaliphan yake ɗaukar Tab ɗin ya bata dazaran ya shigo cikin asibitin. Shekaran jiyama a wajenta ta kwana.
Ɗan harbawar da zuciyarta yayi yasata dakatawa dayin game ɗin, haka yau ta tashi da wannan tsinkewar zuciya da batasan dalili ba, jin abin na ƙara ƙarfi ne ya sakata ajiye tab ɗin ta Khalipha gefe ta zame ta kwanta tana ambaton ‘hazbunallahu wani'imal wakil’ a ranta ko zataji ɗan daɗi............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700