Sashe 60
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan Baffah ya fita aka kawoma su mmn sadiq abinci da ruwa. Ruwanma kawai suka sha dan a ƙoshe duk suke dama. Suna nan zaune tare da hajiya iya har akai kiran sallar magriba Khalipha yaja su Sadiq suka tafi massallaci. Bayan an idar ne sun dawo suka iske Little ya tashi. Sai dai suna toilet Zinneerah ta kaisa zaiyi fitsari. Sannu suka sakema Hajiya iya dake zaune ta idar da salla duk suka fita.
Zinneerah ta fito riƙe da little dake mata maganar da ba wani fahimta takeba sosai saboda bawani ya iya bane da ƙyau. Murmushin ƙarfin hali take masa itama tana magana ƙasa-ƙasa. Hakan yayi dai-dai da shigowar AK ɗakin da sallama. Amsa masa duk sukayi idanunsa na sauka akan Zinneerah da little ɗin. Ita dai bata yarda ta kalli sashen da yakeba, sai da a bazata suka ji little yace, “Abbah ruwa zan ca”.
Gaba ɗaya suka kalli yaron da mamaki dan AK yake kallo, kuma shine ya shigo hannunsa riƙe da goran ruwa.
Murmushi AK ɗin ya saki wanda ya sake fidda kamanninsa da little ɗin ainun yana nufosu. Ƙirjin Zinneerah ya harba da ƙarfi lokacin da yazo gab da su ya miƙama little ɗin hannu alamun yazo gareshi yana faɗin, “Oh my Sweetheart zo, zo”.
Saurin sakar masa shi tayi tana ja baya, shiko little cike da farin cikin daya bawa kowa mamaki musamman ma su su Zinneerah da suka san miskilancin yaron ya wani maƙalƙale Yah AK ɗin yana sauke ajiyar zuciya. Shi kansa AK ajiyar zuciyar ya sauke a ɓoye da sake manne yaron a jikinsa jininsa na tsinkewa. A hankali ya sumbaci goshin yaron sannan ya zauna a bakin gado ya saka masa ruwan a baki yana shafa kansa.
Baki little ya janye yana faɗin, “Ƙoshi Abbah”.
A bazata sukaga AK ɗin yayi dariya da jan hancin yaron yana faɗin, “Wannan hausan naka bai cikaba little Handsome”.
Ƙaramar dariya hajiya iya da zuciyarta ke ƙara raunana da shiga ruɗanin wannan al'amari tayi. hakama Mmn sadiq tai murmushin yaƙe kawai. Kallon Zinneerah hajiya iya tayi. “Inno na a bashi abinci ko”.
Kai ta kaɗama Hajiya iyan da nufar kulolin da aka kawoma su mmn sadiq ɗin basu ciba. Ta buɗe ta zubo abincin kaɗan a filet. Kallo ɗaya tayima little ɗin dake jikin Yah AK yana masa firar da baya fahimta dan maganar tasa ba nuna taiba ta ɗauke kai. “Malami sakko ga abincin”. Tai magana tana dubansu.
Kafaɗa ya noƙe alamar bai zuwa. Hakan yasa Zinneerah hararsa ta ɗauke kanta ta maida gasu Aliyu. “Kuma zakucine Abdull na saka muku?”.
Kai suka girgiza mata alamar a'a. Dan haka ta sake duban inda little yake ganin ko motsi baiyiba har yanzun. Zata sake magana AK ya harareta kaɗan da miƙa mata hannu alamar ta bashi abincin. Baki ta ɗan tura gaba da miƙewa takai masa. Harta juya little yace, “Aunty!”.
Juyowa tai ta kallesa, ganin ya maida kansa kamar bashi ya kiraba yasata hararsa, sai ko a cikin idon AK daya ɗago. Da sauri ta ɗauke kanta ta nufi hanyar ƙofa tana ƙunƙuni a cikin ranta.
Baya taɗan ja saboda Khalipha da zai shigo. Ya dubeta da murmushi dan zuwa yanzu kam ya yarda wannan Zinneerah ce daya sani a Shira hospital. Sai dai little ya saka zuciyarsa a tsananin ruɗani da firgici, dan inhar zai auna da ma'aunin hankali shekarun little zasu iya kaiwa dai-dai da hasashen haihuwar Zinneerah. Amma yaƙi ya yarda da cewar shine ɗan data haifa ɗin.
“Kanwata sai ina kuma?”.
Murmushi tai masa daɗan shafar wuya. “Yah Khalipha zan fitane kawai”.
Murmushin ya sake sakar mata shima, da matsawa ya bata hanya ta fice shikuma ya ƙarasa shigowa idanunsa na sauka akan Yayansu dake bama Little abinci a baki. Ji yay sun wani bala'in birgesa. Har yana ayyanawa a ransa inama ace yaron nan jinin yayan nasune da gaske.
Takawa Khalipha yay ya zauna kusa da yayan nasu yana mai shafa kan little ɗin. Juyowa little yay ya kallesa sai kuma ya juya ya cigaba da karɓar abincin. Kaɗan yaci abincin yace ya ƙoshi, badan AK ya gaji da bashiba ya haƙura ya barsa. Haka ya cigaba da zama a jikinsa har ya sake komawa barci.
Su Mmn Sadiq basubar gidanba sai wajen tara saura na dare. Da ƙyar aka raba little da jikin Yayah Adnan, dan lokacin da Khalipha dazai kaisu yazo amsarsa sai gashi ya farka a bazata. ya ƙanƙame AK ɗin yaƙi zuwa wajen Khalipha. Murmushi AK yay da lumshe idanun yana sunbatar little ɗin a goshi da shafar bayansa. Shi kansa ƙarfin hali kawai yakeyi, amma ji yake kamar karya rabu da yaron dan yayi bala'in shiga ransa.
Daga ƙarshe dai da ƙyar ya yarda Khalipha ya ɗaukesa dan sai da aka haɗa da masa wayo. Motar na ficewa ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya hawayen da baisan kona minene ba suna ciko masa idanu. Ƙoƙarin maidasu yay yana furzar da huci mai zafi da nufa garden ya zauna dan babu abinda yafi buƙata a yanzu kamar kaɗaici.
Yanda AK ya kaɗaice kansa Zinneerah ma harabar gidan ta fito can wajen motoci ta hau bayan ɗaya daga ciki ta zauna tare da faɗawa duniyar tunani. Gaba ɗaya zuciyarta a ruɗani da ɗimuwar kiɗima take. Shin a ina aka faɗi a ragaya ne? Wane darasi rayuwa keson karantar da ita a wannan gaɓarne bayan darasissikan data baro a shekarun baya?. Ko mahaukaci ya kalli little ya kalli Yah AK dolene ya danganta alaƙar jini a tsakaninsu. Dan abinda zai matuƙar baka mamaki ba kammaninne kawaiba. Hatta da wasu a cikin halayen Yah Adnan akwai alamunsu ga little. Kenan to.......
“Kai ina”. Ta faɗa a fili tana girgiza kanta dake matuƙar sara mata. Kamar ance ta ɗaga kai can ta hango Baffah a barandar sama yana kaikawo alamar shima akwai abinda ke damunsa, wanda bata raba ɗayan biyu zancen kamanin little ne da Yayan nasu.
“Ya ALLAH kai ne gagara misali, ka buɗemin tunani, ka yalwatamin fahimtata. Ka gafarta mini zunubaina”. Ta faɗa hawaye na silalo mata akan kumatunta masu zafi. Zurfi sosai ta ƙarayi a tunani har motar Khalipha daya kaisu mmn sadiq ta shigo gidan bata saniba. haskatan da yayne shima ya sakashi ganinta. yana gama fakin ya nufo inda take. Sau biyu yanayin sallama babu amsa, har dai ta kaisa ga ɗan bugar motar ta gefen kunnenta sannan ta kawo nannauyan numfashi tana dubansa.
“Wane irin tafiya tunanine haka da zurfi ƙanwata?”.
Murmushin yaƙe tai masa tana duƙar da kanta ƙasa. Hakan datai sai ya ƙara fiddo masa da kamanninta na baya sosai. Yay murmushi yana gyara tsaiwarsa da faɗin, “Zinneerah na tambayeki mana?.”
Gabantane ya faɗi, amma sai cikin dauriya tace, “Ina jinka Yah Khalipha”.
Kansa ya kaɗa mata yana ajiye keys ɗin hannunsa da wayarsa alamar maganar mai muhimmanci ce. “Dan ALLAH ki faɗamin gaskiya kin manta dani ko?”.
Duk da tambayar tasa tazo mata a bazata dan ba ita tai zaton jiba sai da taji dumm. Ganin ya kafeta da idanu ya sata yin murmushin yaƙe tace, “Ban gane mi kake nufi ba Yah Khalipha”.
“Nasan kin gane Zinneerah, amma tunda hakane bara na miki dallah-dallah”.
“Tun randa na ganki a gidan nan nasan nasan fuskarki, amma na rasa ina na sanki dan kin banbanta da waccan ɗin dana sani a yanzu. Nasha gwadaki naga ko zaki nuna ke kin sani amma baki nunaba, sai yau da naga mama na tabbatar da cewa kece. Shiyyasa mamaki ya kamani na rashin nuna kin sanni da kikai kafin yau”.
Tabbas taji kunya. amma sai ta dake, ta buɗe baki da zummar bashi amsa sukaji ƙamshin turarensa da takun tahowarsa. Duk kallon waje. sukai Zinneerah na haɗiye maganar da tai niyyar yi. Ganin yanda yake kallonsu ya sata jin wani iri, babu shiri ta diro akan motar tai cikin gida sum-sum duk da alamar ta zauna da Khalipha ke mata da hannunsa.
Khalipha da shi kansa kallon da Yayan nasu ke musu ya bashi mamaki, cikin dauriya yace, “Yayanmu na zata ka kwanta ma ai”.
“Shiyyasa kazo nan kake taɗi?”.
Ya faɗa yana wucesa. Saurin waro idanu Khalipha yay waje da biyo bayansa. “Ni Abdul-Mutallab, jikan Abdul-Mutallab, ƙanin Abdul-Mutallab wane ni Yayanmu”.
Ɗan juyowa yay ya dubesa. Hakan yasa kunya kama Khalipha yakai hannu yana shafa wuya da risinar da nasa idanunsa ƙasa.
Wani irin juya idanunsa da suka ɗan fara sauya kala yayi yay gaba batare da ya sake cema Khalipha ɗin komaiba, dan harga ALLAH baya cikin hankalinshi da nutsuwar. Binsa da kallo Khalipha yay harya shige sashen Hajiya Iya. Kasa binsa yayi, sai kawai shima ya nufi sashensu zuciyarsa na ƙoƙarin karkato masa wani abu daban.
★★★★
Zinneerah ta fito riƙe da little dake mata maganar da ba wani fahimta takeba sosai saboda bawani ya iya bane da ƙyau. Murmushin ƙarfin hali take masa itama tana magana ƙasa-ƙasa. Hakan yayi dai-dai da shigowar AK ɗakin da sallama. Amsa masa duk sukayi idanunsa na sauka akan Zinneerah da little ɗin. Ita dai bata yarda ta kalli sashen da yakeba, sai da a bazata suka ji little yace, “Abbah ruwa zan ca”.
Gaba ɗaya suka kalli yaron da mamaki dan AK yake kallo, kuma shine ya shigo hannunsa riƙe da goran ruwa.
Murmushi AK ɗin ya saki wanda ya sake fidda kamanninsa da little ɗin ainun yana nufosu. Ƙirjin Zinneerah ya harba da ƙarfi lokacin da yazo gab da su ya miƙama little ɗin hannu alamun yazo gareshi yana faɗin, “Oh my Sweetheart zo, zo”.
Saurin sakar masa shi tayi tana ja baya, shiko little cike da farin cikin daya bawa kowa mamaki musamman ma su su Zinneerah da suka san miskilancin yaron ya wani maƙalƙale Yah AK ɗin yana sauke ajiyar zuciya. Shi kansa AK ajiyar zuciyar ya sauke a ɓoye da sake manne yaron a jikinsa jininsa na tsinkewa. A hankali ya sumbaci goshin yaron sannan ya zauna a bakin gado ya saka masa ruwan a baki yana shafa kansa.
Baki little ya janye yana faɗin, “Ƙoshi Abbah”.
A bazata sukaga AK ɗin yayi dariya da jan hancin yaron yana faɗin, “Wannan hausan naka bai cikaba little Handsome”.
Ƙaramar dariya hajiya iya da zuciyarta ke ƙara raunana da shiga ruɗanin wannan al'amari tayi. hakama Mmn sadiq tai murmushin yaƙe kawai. Kallon Zinneerah hajiya iya tayi. “Inno na a bashi abinci ko”.
Kai ta kaɗama Hajiya iyan da nufar kulolin da aka kawoma su mmn sadiq ɗin basu ciba. Ta buɗe ta zubo abincin kaɗan a filet. Kallo ɗaya tayima little ɗin dake jikin Yah AK yana masa firar da baya fahimta dan maganar tasa ba nuna taiba ta ɗauke kai. “Malami sakko ga abincin”. Tai magana tana dubansu.
Kafaɗa ya noƙe alamar bai zuwa. Hakan yasa Zinneerah hararsa ta ɗauke kanta ta maida gasu Aliyu. “Kuma zakucine Abdull na saka muku?”.
Kai suka girgiza mata alamar a'a. Dan haka ta sake duban inda little yake ganin ko motsi baiyiba har yanzun. Zata sake magana AK ya harareta kaɗan da miƙa mata hannu alamar ta bashi abincin. Baki ta ɗan tura gaba da miƙewa takai masa. Harta juya little yace, “Aunty!”.
Juyowa tai ta kallesa, ganin ya maida kansa kamar bashi ya kiraba yasata hararsa, sai ko a cikin idon AK daya ɗago. Da sauri ta ɗauke kanta ta nufi hanyar ƙofa tana ƙunƙuni a cikin ranta.
Baya taɗan ja saboda Khalipha da zai shigo. Ya dubeta da murmushi dan zuwa yanzu kam ya yarda wannan Zinneerah ce daya sani a Shira hospital. Sai dai little ya saka zuciyarsa a tsananin ruɗani da firgici, dan inhar zai auna da ma'aunin hankali shekarun little zasu iya kaiwa dai-dai da hasashen haihuwar Zinneerah. Amma yaƙi ya yarda da cewar shine ɗan data haifa ɗin.
“Kanwata sai ina kuma?”.
Murmushi tai masa daɗan shafar wuya. “Yah Khalipha zan fitane kawai”.
Murmushin ya sake sakar mata shima, da matsawa ya bata hanya ta fice shikuma ya ƙarasa shigowa idanunsa na sauka akan Yayansu dake bama Little abinci a baki. Ji yay sun wani bala'in birgesa. Har yana ayyanawa a ransa inama ace yaron nan jinin yayan nasune da gaske.
Takawa Khalipha yay ya zauna kusa da yayan nasu yana mai shafa kan little ɗin. Juyowa little yay ya kallesa sai kuma ya juya ya cigaba da karɓar abincin. Kaɗan yaci abincin yace ya ƙoshi, badan AK ya gaji da bashiba ya haƙura ya barsa. Haka ya cigaba da zama a jikinsa har ya sake komawa barci.
Su Mmn Sadiq basubar gidanba sai wajen tara saura na dare. Da ƙyar aka raba little da jikin Yayah Adnan, dan lokacin da Khalipha dazai kaisu yazo amsarsa sai gashi ya farka a bazata. ya ƙanƙame AK ɗin yaƙi zuwa wajen Khalipha. Murmushi AK yay da lumshe idanun yana sunbatar little ɗin a goshi da shafar bayansa. Shi kansa ƙarfin hali kawai yakeyi, amma ji yake kamar karya rabu da yaron dan yayi bala'in shiga ransa.
Daga ƙarshe dai da ƙyar ya yarda Khalipha ya ɗaukesa dan sai da aka haɗa da masa wayo. Motar na ficewa ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya hawayen da baisan kona minene ba suna ciko masa idanu. Ƙoƙarin maidasu yay yana furzar da huci mai zafi da nufa garden ya zauna dan babu abinda yafi buƙata a yanzu kamar kaɗaici.
Yanda AK ya kaɗaice kansa Zinneerah ma harabar gidan ta fito can wajen motoci ta hau bayan ɗaya daga ciki ta zauna tare da faɗawa duniyar tunani. Gaba ɗaya zuciyarta a ruɗani da ɗimuwar kiɗima take. Shin a ina aka faɗi a ragaya ne? Wane darasi rayuwa keson karantar da ita a wannan gaɓarne bayan darasissikan data baro a shekarun baya?. Ko mahaukaci ya kalli little ya kalli Yah AK dolene ya danganta alaƙar jini a tsakaninsu. Dan abinda zai matuƙar baka mamaki ba kammaninne kawaiba. Hatta da wasu a cikin halayen Yah Adnan akwai alamunsu ga little. Kenan to.......
“Kai ina”. Ta faɗa a fili tana girgiza kanta dake matuƙar sara mata. Kamar ance ta ɗaga kai can ta hango Baffah a barandar sama yana kaikawo alamar shima akwai abinda ke damunsa, wanda bata raba ɗayan biyu zancen kamanin little ne da Yayan nasu.
“Ya ALLAH kai ne gagara misali, ka buɗemin tunani, ka yalwatamin fahimtata. Ka gafarta mini zunubaina”. Ta faɗa hawaye na silalo mata akan kumatunta masu zafi. Zurfi sosai ta ƙarayi a tunani har motar Khalipha daya kaisu mmn sadiq ta shigo gidan bata saniba. haskatan da yayne shima ya sakashi ganinta. yana gama fakin ya nufo inda take. Sau biyu yanayin sallama babu amsa, har dai ta kaisa ga ɗan bugar motar ta gefen kunnenta sannan ta kawo nannauyan numfashi tana dubansa.
“Wane irin tafiya tunanine haka da zurfi ƙanwata?”.
Murmushin yaƙe tai masa tana duƙar da kanta ƙasa. Hakan datai sai ya ƙara fiddo masa da kamanninta na baya sosai. Yay murmushi yana gyara tsaiwarsa da faɗin, “Zinneerah na tambayeki mana?.”
Gabantane ya faɗi, amma sai cikin dauriya tace, “Ina jinka Yah Khalipha”.
Kansa ya kaɗa mata yana ajiye keys ɗin hannunsa da wayarsa alamar maganar mai muhimmanci ce. “Dan ALLAH ki faɗamin gaskiya kin manta dani ko?”.
Duk da tambayar tasa tazo mata a bazata dan ba ita tai zaton jiba sai da taji dumm. Ganin ya kafeta da idanu ya sata yin murmushin yaƙe tace, “Ban gane mi kake nufi ba Yah Khalipha”.
“Nasan kin gane Zinneerah, amma tunda hakane bara na miki dallah-dallah”.
“Tun randa na ganki a gidan nan nasan nasan fuskarki, amma na rasa ina na sanki dan kin banbanta da waccan ɗin dana sani a yanzu. Nasha gwadaki naga ko zaki nuna ke kin sani amma baki nunaba, sai yau da naga mama na tabbatar da cewa kece. Shiyyasa mamaki ya kamani na rashin nuna kin sanni da kikai kafin yau”.
Tabbas taji kunya. amma sai ta dake, ta buɗe baki da zummar bashi amsa sukaji ƙamshin turarensa da takun tahowarsa. Duk kallon waje. sukai Zinneerah na haɗiye maganar da tai niyyar yi. Ganin yanda yake kallonsu ya sata jin wani iri, babu shiri ta diro akan motar tai cikin gida sum-sum duk da alamar ta zauna da Khalipha ke mata da hannunsa.
Khalipha da shi kansa kallon da Yayan nasu ke musu ya bashi mamaki, cikin dauriya yace, “Yayanmu na zata ka kwanta ma ai”.
“Shiyyasa kazo nan kake taɗi?”.
Ya faɗa yana wucesa. Saurin waro idanu Khalipha yay waje da biyo bayansa. “Ni Abdul-Mutallab, jikan Abdul-Mutallab, ƙanin Abdul-Mutallab wane ni Yayanmu”.
Ɗan juyowa yay ya dubesa. Hakan yasa kunya kama Khalipha yakai hannu yana shafa wuya da risinar da nasa idanunsa ƙasa.
Wani irin juya idanunsa da suka ɗan fara sauya kala yayi yay gaba batare da ya sake cema Khalipha ɗin komaiba, dan harga ALLAH baya cikin hankalinshi da nutsuwar. Binsa da kallo Khalipha yay harya shige sashen Hajiya Iya. Kasa binsa yayi, sai kawai shima ya nufi sashensu zuciyarsa na ƙoƙarin karkato masa wani abu daban.
★★★★