← Book details Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 155

Sashe 90

Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

       Koda AK ya kammala karyawa fita sukai shi da Huzaifa da little, dan yanason rage damuwar Mammah dake cin ransa suk da yaji daɗin abinda Mahma tayi. Sai da suka fita ya samu damar yin waya da Hajiya Iya ta wayar Khalipha daketa ƙoƙarin danne damuwarsa.
      Sun jima suna wayar da Hajiya iya harma da Huzaifa da little dataji daɗin gani tare dasu dan video call ne. A bakin Hajiya iyan ne ma yakejin wai Farah ta fita da akwati a gidan tun ɗazun, kuma su basusan ina ta nufaba dan bataima kowa maganaba.
     Murmushi AK yayi, cikin rashin damuwa yace, “Karki damu Granny gidan Mammah ta tafi, kuma Mahma zatai maganinta ne ta dawo da ƙafafunta”.
    Baki Hajiya iya ta taɓe da faɗin, “Kai nifa yanzu kam taitayi dan bata cikin lissafina. Tunda ALLAH ya baka ƴar mutunci da nakeda tabbacin zata share hawayenka in ALLAH ya yarda. Fatana dai ka riƙemin yarinya da ƙyau Moddibo, dan wlhy inhar Inno tai kuka akanka kaima sai kayi”.
       Fiska ya ɓata yana wani ɗan yatsinata. Yace, “Oh kukuma naku salon kenan Granny?”.
      “Ai mun wucema haka, dan wlhy bazan baka Inno ba saina shimfiɗa maka dokoki, ko ɗaya ka tsallaka kuwa saika haɗu da fushina”.
      “To lallai naku babbane, nikam sai anjimanki”.
       “Zakaci ubanka Kabirune yaro, bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.
     “Ahaka dai kuka gani kuka nane”. Ya faɗa a hasale saboda zagar masa uba da tayi. Itako Hajiya iya dama tayine danta hasalashi ɗin dan haka ta hau dariya. Huzaifa fa ma dai dariyar yakeyi. Hajiya iya tace, “Kaima ai ina zuwa kanka dan uwarka Balkisu, tuzurun banza kana neman tsofewa a gida babu aure. Why bara dai na dawo ƴar kowa na samu aura maka zanyi a dangi, da wani shegen kansa uwa sheƙar angulu”.
      A take shima ya shanye tasa dariyar yana ɓata fuska, “To kin kuma dawo kaina? Kefa ALLAH Granny kinada matsa kiyita zagema mutum iyaye babu laifin zaune babu na tsaye.  Sai ki nema wanda zaki samoma mata a ƙauye badai niba wlhy”.
      “An zageka ɗin mai kama da zucbibin ƴan Lagos, bara dai na dawo kaga yanda zanyi maganinka wlhy, inba hakaba nasa Bashir ɗin yima uwarka kishiya itama wlhy. (Daddynsa take nufi😂) dan haka ya waro idanu waje da faɗin, “Kai! Wai ke Granny miyasa lamarin naki kullum gaba yakeyi?, sam bakison zaman lafiya?”.
     “Oh bama kasan yana yin gaba ba saina dawo Nigeria”. Tai maganar tana yanke kiran.
       “Tsohuwarnan akwai tarin matsaloli a kanta yasin”.
    Cewar Huzaifa rai ɓace. Shi adole yaji haushi ance za'a saka aima Mommy kishiya😹.
     “Ai indai Granny ce ta wuce duk yanda kake tunaninta”. Cewar AK yana wani ɓata fuska shima. Little da baisan anaiba wasansa kawai yake zabgawa.
      Biyawa sukai ta gidan Dr Mahmud suka ɗaukesa dan gona zasuje duba masu aikin shinkafa, daga na su leƙa company da ayanzu haka an fara zuba aikinsa shima. Kasancewar sun tahoma Little da kayan ciye-ciye ko damuwa baiyiba, sai uban rashinji yake zubawa a gonar alamar yana cikin ƙoshin lafiya.
        Huzaifa akwai son irin wannan wajajen, dan haka ya shiga cikin gonar sosai yana duba aikin da yaba ƙyawun da yayi. Da wannan damar AK da Dr Mahmud suka tattauna akan abinda ya shafesu game da ginin company nin shinkafa da kuma aikin shinkafar, dan a shirinsa so yake ya koma london zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu, kuma da Little yake shirin komawar, baisan kuma yanda zasu kwashe da Baffah ba akan hakan.............✍

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

________________________

*page 44*

...........A gajiye suka shigo gidan gab da magriba, dama sun ajiye Dr Mahmud a gidansa. Little kuwa yayi barci jikin Abbansa dan Huzaifa ne yay driving ɗin.
        Koda Huzaifa yay fakin a inda ya dace AK fita yay ɗauke da little a kafaɗa, kai tsaye sashen Hajiya iya ya nufa batare da ya saurari maganar da Huzaifa ke masaba. Kasancewar bayan tafiyarsu Abidah ta shigo ta gyara masa sashen sai ko ina ya kasance ƙal ga kuma ƙamshi, sosai yakejin kewar rashin Granny a sashen. Dan haka baima son zama ya yini a gidan sam.
      A hankali ya kwantar da little dake barcinsa. Duk da ya ɓata jikinsa sosai a can bai tadashiba, sai dai shi ya cire nasa kayan ya nufi bayi a gurguje saboda lokacin sallar magrib yayi.
     Wankan ma a gaggauce ya yisa ya fito, jallabiya kawai ya zura ya ɗan saka turare ya fito yana addu'ar ALLAH yasa kar little ya farka harya dawo.

     Bayan an idar da salla bai zaunaba ya nufo gida saboda tunanin barin little da yayi shi kaɗai. Koda ya leƙo yaga barcinsa yake har yanzu sai ya koma massallacin. Sai da akai sallar isha'i suka taho shi da ƴan uwansa da Baffah gwanin sha'awa.
       A gajiye yake matuƙa, dan haka ya wuce sashen hajiya iya kai tsaye yana cema Mas'ood yasa cikinsu Safiyya wani ya kawo masa tea da abinci kaɗan saboda little karya farka ya nema. Da to Mas'ood ya amsa masa cikin girmamawa.
      Harya nufi hanyar sashen hajiya iya baffah dake ƙoƙarin shigewa nasa sashe shima ya juyi ya dubi AK ɗin. “Karfa suga mun musu ƙarfa-ƙarfa akan yaron nan, daga zuwa ya gaida Bilkisu”.
      Juyiwa AK yay zuciyarsa na harbawa, harga ALLAH baya fatan abinda zaisa Baffah yace ya sake rabuwa da little ɗin a yanzu, danshi yanzu haka yana shiryama zuciyarsa tafiya da yaron nema london. Amma yanzu sai ya ɗan murmusa, murya a sanyaye yace, “Baffah zai koma ai sonake saina tashi tafiya”.
      “Sai da safe”. Baffah ya faɗa yana shigewarsa. Shima cigaba yay da tafiya zuciyarsa na masa rauni akan iya sake rabuwa da gudan jinin nasa gaskiya.
Chapter 90 · 0% Book details