Sashe 147
Makauniyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwana biyu dayin haka sai ga Mahma daga london. AK yaji matuƙar daɗin wannan zuwa nata, dan dama lokacin bikin su Adilah ta tabbatar masa da cikin Zinneerah ya shiga watanni bakwai insha ALLAH zatazo Nigeria. To shikam ya ƙudiri tunda tazo riƙeta zaiyi har sai matarsa ta haihu.
Sosai Zinneerah ma ta nuna farin cikinta sosai na zuwan Mahma. Dan-danan ta gyara mata ɗayan ɗakinta na falon farko duk da dama fes yake. Bakuma wani amfani take da shiba garama da ƴan Danya sukazo tariyarar Yaya Sa'a sun kwana a ciki.
Itama Mahma taji daɗin yanda suka tarbetan, tare da ɗunbin tausayin Zinneerah daketa fama, dan ga cikin nata yayi girma sosai Alhmdllh kamar ba ɗan wata bakwai ba. Kasama haƙuri tayi sai da tace, “Anya cikin nan ba ƴan biyu bane kuwa a cikinsa?”.
Cike da kunya Zinneerah tai ƙasa da kai tana murmushi kawai. Sai AK dake saurarensune yace, “Ƴan biyu kuma Mahma?”.
“Eh mana Abdul-Mutallab, ai girman cikin ne masha ALLAH kamar ba wata bakwai ba”.
Kallon Zinneerah ɗin yayi shima da ƙyau zuciyarsa na fata da tabbatar wannan zance na Mahma. Yace, “To Mahma bamu saniba dai, amma ALLAH ya tabbatar”.
“Amin to, amma baku dubaba kenan?”.
“Wlhy Mahma banason wannan bin ƙwaƙwƙwafin, komai ya fito a cikin nan ina maraba dashi da so da ƙaunarsa”.
“Alhmdllh aihaka akeso musulmi ya kasance Abdul-Mutallab, ALLAH ya rabasu lafiya”.
Da “Amin” ya amsa mata. Zinneerah kuwa tayi a zuciyarta kawai.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_______________________
*Page 67*
.............Alhmdllhi sosai zuwan Mahma ya taimakawa Zinneerah, dan tana ɗebe mata kewa da rage wasu abubuwan. Tana kwana na huɗu ma da zuwa sai ga wata dattijuwa Hajiya iya data sa aka kawo mata daga bauchi ta iso. Nanma ya haɗu ya ƙara taimakawa Zinneerah ɗin sosai. Dan Mama A'i mace ce mai ƙoƙari da haƙuri. Gashi bata da yawan hayaniya itama ga kuma tsafta. Hakan yasa tasu tazo ɗaya da AK. Duk da dai iyakacinta ɗan taya aikin gida Mahma ke musu girki, wani lokacin kuma Zinneerah ɗin kan shiga da kanta tayi. Hidimar Little kuwa dama ta koma hannun Mahma. Yanzu ma a ɗakinta yake kwana abinsa.
Haka aka cigaba da turawa har ALLAH ya sauka Tinene lafiya daga danya. Ta samu ƴarta mace mai kama da ubanta sak. A randa ta haihu a ranar aka ɗaura aurenta da Lado. Bayan arba'in zata ta tare. Baba bai gayama Sa'a da Zinneerah ba sai kusan kwanaki biyar da haihuwar ma. Dukansu sun mata addu'a da fatan alkairi, suka kuma aika musu da abinda ALLAH ya hore musu tunda duk ba sana'a sukeba. Dan Sa'a ma makaranta ta koma Dr Mahmud nason ta haɗa kwalinta na secondary da shirirta da halin Inna yasata kasa haɗawa. Tunda koda ta koma bayan baro Zinneerah Danya bata kammalaba tunda komawa tai ta fara daga js1.
Ranar tarewar ma da ƙyar AK ya yarda suka tafi ita da Sa'a. Amma ya tabbatar mata banda kwana ranar zasu dawo. dan ko little ma bai bitaba ita kaɗai ta tafi Haneef ya tafi kaisu ita da Sa'a dasu Bahijja.
Sun sami tarba mai ƙyau, dan kowa sai ji dasu yake sun zama tamkar wasu taurari a dangi baki ɗaya. Kowa nata tausayin Zinneerah da fatan ALLAH ya sauketa kafiya. itama Sa'a ALLAH ya bata nata dan har yanzu dai babu ciki.
Ganin yanda jikin Inna ya ƙara rincaɓewa yasa hankalin Zinneerah da Sa'a ƙara tashi, dan Karima dake gidan tana kula da ita tata ƙorafi kenan da mita. Wani lokacinma sai yaya Gajeje ta yunƙuro tazo ko matar baba tai mata wani abun Karimar na zaune taƙiyi. Kiran AK tai ta sanar masa. Bai wani ja zancenba yace ta haɗashi da Haneef dan tunma ɗazu yake nemansa ya gaza samu, itama ɗin ya nemetan yaji yaya suka sauka amma bai samuba sai yanzu data kirasa.
Umarni ya bama Haneef ɗin akan su taho da Inna kano. Batare da Zinneerah tasani ba sai da aka idar da sallar la'asar Baba ya tunkaresu da zancen. Murmushi kawai tayi bata nuna bata saniba. A ranta kuwa tana mamakin Yayansu.
Kowa yaji daɗin abinda AK ɗin yayi, dan haka ana gama shagali basu zauna akai amarya ɗakintaba suka tattaro zasu taho, wai kuma Karima zata biyosu Baba yace bata isa ba. Yaya gajeje zata bisu daga baya. Itako ta zauna Danya.
Sa'a ma da nufin kwana tazo, amma jin Zinneerah bazata kwana ba kuma za'a tafi da Inna sai kawai ta shirya ta biyosu. A shira hospital suka sauke Inna, inda Dr Mahmud yasan da zuwan nasu dan sunyi nagana da AK. Anan suka bar masa Sa'a bayan sunga komai ya dai-daita na kula da Inna. Haneef ya wuce da Zinneerah gida ya fara ajiyeta sannan suka wuce gida suma dasu Meenal.
Tun daga ranar jinyar Inna ya dawo ƙarƙashin kulawar su AK, amma Yaya Gajeje tazo daga danya tana tare da ita a asibitin. Kullum sai Zinneerah taje ta dubata kamar yanda Sa'a ma haka. Alhmdllh kuma jikin nata na ƙyau ba kamar sanda tana Danya ba. Dan magunguna masu ƙyau da tsada ake mata amfani dasu, ga kulawa ta musamman da take samu daga mazan ƴaƴan nata. Baba ma lokaci-lokaci yakanzo dubata shi da yan uwansa da amaryarsa da Karima.
A haka Zinneerah ta cigaba da turawa har aka shiga kwanakin jiran tsammani na haihuwarta. Zuwa yanzu kam sosai bata da lafiya tamkar cikin little, dan dolema aka koma da ita zaman asibiti. Kwanakinta shidda a asibitin a wata safiya ta wayi gari da naƙuda. Sai dai fa tamkar cikin little jini ya ɓalle mata ga haihuwar shiru. Hankalin AK da kowama ya tashi, hakan yasa Dr Mahmud ya bada shawarar kawai ai mata cs kafin ta jigata ƙarfinta ya ƙare.
Babu wani jayayya AK ya amince. Zuciyarsa fal tausayin halin da take ciki. Yayinda yake rayawa a ransa ko wannan tashin hankali da ta shiga a wancan karon na haihuwar little ya isa hana su Farah zaman lafiya da jin daɗi. Shikam sai yanzuma yake ganin matsalar da sukaita fuskanta na rashin jin daɗin rayuwar aurensu kullum faɗa da fitina shi da Farah ko wannan halin da suka zama sanadin jefa yarinyarnan ya isa su rasa farin cikin rayuwar aurensu ai. Dan Dr Mahmud ya tabbatar masa da haka tasha irin wannan wahalar a wancan karon ma.
Alhmdllh an yi mata cs aka ciro ƴaƴa biyu mace da namiji. Zokaga murna wajen kowa. Shikam AK duk da yana murna da samuwar tasu hankalinsa nakan matarsa. sai da yaji tabbacin kasancewarta cikin ƙoshin lafiya sannan hankalinsa ya ɗan kwanta harya amshi jariransa ƙyawawa masu lafiya yana mai jerama UBANGIJI godiya daya bashi ƙyautarsu ta silar da ALLAH ya halatta masa bayan ya cire tsammani daga hakan.
Inna daketa samun sauƙi tana zaune dan yanzu takan ɗan motsa jikin aka sanar mata da haihuwar Zinneerah. Hawaye kawai su Sa'a sukaga tanayi amma batace komaiba. Hakan yasa suka gagara fahintar na minene? Na daɗine kona nadama? Kona baƙin cikin har yanzu?.
Oho masu karfin ajin ma basusan tanai ba. Dan cikin ƙanƙanin lokaci Shirawa suka cika asibitin domin taya Yayansu murna da samun wannan ƙaruwa. Waɗanda basa kusa kam irinsu Khalipha da Adilah tuni hotunan babes ya isa ga wayoyunsu.
Addu'a dai kam sun shata kamar yanda Zinneerah ma keshan tata na fatan samun lafiya. dan kowa bai gantaba itakam har AK ɗin sai da daddare. Shima ya samu tanata barci. Ya ƙureta da ido cike da tausayi da ƙauna dan dukta rame sosai fiyema da lokacin da cikin na jikinta. Sumbatar goshinta yayi da hannunta yana mai jera mata addu'ar samun lafiya.
Sauran ƴan uwa kuwa da abokan arziƙi basu sami ganintaba sai washe gari, zuwa sannan ta farka Alhmdllhi. Kuma tana gane kowa da amsama kowa gaisuwarsa.
Lokacin da taga ƴan jinjirayenta da farin cikin dake shinfiɗe a fuskar AK murmushi ta dinga zubawa itama. a ranta tana musu addu'a. A fili kuwa sai ta dinga nuna alkunya su Hajiya iya na mata dariya. Sai dai har cikin ransu hakan da tai ya musu daɗi, dan yaran yanzu daba kawaici garemu akan ƴaƴaba koda na farine balle na biyu.
Sai dai kuma wata sabuwa. wannan karonma tamkar haihuwar little ruwan nono ya zamarwa yaran damuwa. Dan da sun sha cikinsu duk sai yake kumbura suyita kuka. Ga namijin da son abinci tamkar ubansa. Hankalin AK ya tashi matuƙa da hakan. Amma da Dr Mahmud ya sanar masa haka dama sukasha fama akan little sai yaɗan sami nutsuwa. Yanzuma magunguna suka haɗa mata. Amma sai Mahma tace wanann al'amari kamar bana asibiti ba. Yanada nasaba da jinnu sai an dage sosai ma Zinneerah ɗin.
Kowa yasha mamaki, amma sanin wacece ita a wannan fanin yasa duk suka amince. Itace da kanta ta fara harhaɗama Zinneerah magungunan gargajiya ta fara amfani dasu, tace insha ALLAH komai zai daidaita.
Sosai Zinneerah ma ta nuna farin cikinta sosai na zuwan Mahma. Dan-danan ta gyara mata ɗayan ɗakinta na falon farko duk da dama fes yake. Bakuma wani amfani take da shiba garama da ƴan Danya sukazo tariyarar Yaya Sa'a sun kwana a ciki.
Itama Mahma taji daɗin yanda suka tarbetan, tare da ɗunbin tausayin Zinneerah daketa fama, dan ga cikin nata yayi girma sosai Alhmdllh kamar ba ɗan wata bakwai ba. Kasama haƙuri tayi sai da tace, “Anya cikin nan ba ƴan biyu bane kuwa a cikinsa?”.
Cike da kunya Zinneerah tai ƙasa da kai tana murmushi kawai. Sai AK dake saurarensune yace, “Ƴan biyu kuma Mahma?”.
“Eh mana Abdul-Mutallab, ai girman cikin ne masha ALLAH kamar ba wata bakwai ba”.
Kallon Zinneerah ɗin yayi shima da ƙyau zuciyarsa na fata da tabbatar wannan zance na Mahma. Yace, “To Mahma bamu saniba dai, amma ALLAH ya tabbatar”.
“Amin to, amma baku dubaba kenan?”.
“Wlhy Mahma banason wannan bin ƙwaƙwƙwafin, komai ya fito a cikin nan ina maraba dashi da so da ƙaunarsa”.
“Alhmdllh aihaka akeso musulmi ya kasance Abdul-Mutallab, ALLAH ya rabasu lafiya”.
Da “Amin” ya amsa mata. Zinneerah kuwa tayi a zuciyarta kawai.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_______________________
*Page 67*
.............Alhmdllhi sosai zuwan Mahma ya taimakawa Zinneerah, dan tana ɗebe mata kewa da rage wasu abubuwan. Tana kwana na huɗu ma da zuwa sai ga wata dattijuwa Hajiya iya data sa aka kawo mata daga bauchi ta iso. Nanma ya haɗu ya ƙara taimakawa Zinneerah ɗin sosai. Dan Mama A'i mace ce mai ƙoƙari da haƙuri. Gashi bata da yawan hayaniya itama ga kuma tsafta. Hakan yasa tasu tazo ɗaya da AK. Duk da dai iyakacinta ɗan taya aikin gida Mahma ke musu girki, wani lokacin kuma Zinneerah ɗin kan shiga da kanta tayi. Hidimar Little kuwa dama ta koma hannun Mahma. Yanzu ma a ɗakinta yake kwana abinsa.
Haka aka cigaba da turawa har ALLAH ya sauka Tinene lafiya daga danya. Ta samu ƴarta mace mai kama da ubanta sak. A randa ta haihu a ranar aka ɗaura aurenta da Lado. Bayan arba'in zata ta tare. Baba bai gayama Sa'a da Zinneerah ba sai kusan kwanaki biyar da haihuwar ma. Dukansu sun mata addu'a da fatan alkairi, suka kuma aika musu da abinda ALLAH ya hore musu tunda duk ba sana'a sukeba. Dan Sa'a ma makaranta ta koma Dr Mahmud nason ta haɗa kwalinta na secondary da shirirta da halin Inna yasata kasa haɗawa. Tunda koda ta koma bayan baro Zinneerah Danya bata kammalaba tunda komawa tai ta fara daga js1.
Ranar tarewar ma da ƙyar AK ya yarda suka tafi ita da Sa'a. Amma ya tabbatar mata banda kwana ranar zasu dawo. dan ko little ma bai bitaba ita kaɗai ta tafi Haneef ya tafi kaisu ita da Sa'a dasu Bahijja.
Sun sami tarba mai ƙyau, dan kowa sai ji dasu yake sun zama tamkar wasu taurari a dangi baki ɗaya. Kowa nata tausayin Zinneerah da fatan ALLAH ya sauketa kafiya. itama Sa'a ALLAH ya bata nata dan har yanzu dai babu ciki.
Ganin yanda jikin Inna ya ƙara rincaɓewa yasa hankalin Zinneerah da Sa'a ƙara tashi, dan Karima dake gidan tana kula da ita tata ƙorafi kenan da mita. Wani lokacinma sai yaya Gajeje ta yunƙuro tazo ko matar baba tai mata wani abun Karimar na zaune taƙiyi. Kiran AK tai ta sanar masa. Bai wani ja zancenba yace ta haɗashi da Haneef dan tunma ɗazu yake nemansa ya gaza samu, itama ɗin ya nemetan yaji yaya suka sauka amma bai samuba sai yanzu data kirasa.
Umarni ya bama Haneef ɗin akan su taho da Inna kano. Batare da Zinneerah tasani ba sai da aka idar da sallar la'asar Baba ya tunkaresu da zancen. Murmushi kawai tayi bata nuna bata saniba. A ranta kuwa tana mamakin Yayansu.
Kowa yaji daɗin abinda AK ɗin yayi, dan haka ana gama shagali basu zauna akai amarya ɗakintaba suka tattaro zasu taho, wai kuma Karima zata biyosu Baba yace bata isa ba. Yaya gajeje zata bisu daga baya. Itako ta zauna Danya.
Sa'a ma da nufin kwana tazo, amma jin Zinneerah bazata kwana ba kuma za'a tafi da Inna sai kawai ta shirya ta biyosu. A shira hospital suka sauke Inna, inda Dr Mahmud yasan da zuwan nasu dan sunyi nagana da AK. Anan suka bar masa Sa'a bayan sunga komai ya dai-daita na kula da Inna. Haneef ya wuce da Zinneerah gida ya fara ajiyeta sannan suka wuce gida suma dasu Meenal.
Tun daga ranar jinyar Inna ya dawo ƙarƙashin kulawar su AK, amma Yaya Gajeje tazo daga danya tana tare da ita a asibitin. Kullum sai Zinneerah taje ta dubata kamar yanda Sa'a ma haka. Alhmdllh kuma jikin nata na ƙyau ba kamar sanda tana Danya ba. Dan magunguna masu ƙyau da tsada ake mata amfani dasu, ga kulawa ta musamman da take samu daga mazan ƴaƴan nata. Baba ma lokaci-lokaci yakanzo dubata shi da yan uwansa da amaryarsa da Karima.
A haka Zinneerah ta cigaba da turawa har aka shiga kwanakin jiran tsammani na haihuwarta. Zuwa yanzu kam sosai bata da lafiya tamkar cikin little, dan dolema aka koma da ita zaman asibiti. Kwanakinta shidda a asibitin a wata safiya ta wayi gari da naƙuda. Sai dai fa tamkar cikin little jini ya ɓalle mata ga haihuwar shiru. Hankalin AK da kowama ya tashi, hakan yasa Dr Mahmud ya bada shawarar kawai ai mata cs kafin ta jigata ƙarfinta ya ƙare.
Babu wani jayayya AK ya amince. Zuciyarsa fal tausayin halin da take ciki. Yayinda yake rayawa a ransa ko wannan tashin hankali da ta shiga a wancan karon na haihuwar little ya isa hana su Farah zaman lafiya da jin daɗi. Shikam sai yanzuma yake ganin matsalar da sukaita fuskanta na rashin jin daɗin rayuwar aurensu kullum faɗa da fitina shi da Farah ko wannan halin da suka zama sanadin jefa yarinyarnan ya isa su rasa farin cikin rayuwar aurensu ai. Dan Dr Mahmud ya tabbatar masa da haka tasha irin wannan wahalar a wancan karon ma.
Alhmdllh an yi mata cs aka ciro ƴaƴa biyu mace da namiji. Zokaga murna wajen kowa. Shikam AK duk da yana murna da samuwar tasu hankalinsa nakan matarsa. sai da yaji tabbacin kasancewarta cikin ƙoshin lafiya sannan hankalinsa ya ɗan kwanta harya amshi jariransa ƙyawawa masu lafiya yana mai jerama UBANGIJI godiya daya bashi ƙyautarsu ta silar da ALLAH ya halatta masa bayan ya cire tsammani daga hakan.
Inna daketa samun sauƙi tana zaune dan yanzu takan ɗan motsa jikin aka sanar mata da haihuwar Zinneerah. Hawaye kawai su Sa'a sukaga tanayi amma batace komaiba. Hakan yasa suka gagara fahintar na minene? Na daɗine kona nadama? Kona baƙin cikin har yanzu?.
Oho masu karfin ajin ma basusan tanai ba. Dan cikin ƙanƙanin lokaci Shirawa suka cika asibitin domin taya Yayansu murna da samun wannan ƙaruwa. Waɗanda basa kusa kam irinsu Khalipha da Adilah tuni hotunan babes ya isa ga wayoyunsu.
Addu'a dai kam sun shata kamar yanda Zinneerah ma keshan tata na fatan samun lafiya. dan kowa bai gantaba itakam har AK ɗin sai da daddare. Shima ya samu tanata barci. Ya ƙureta da ido cike da tausayi da ƙauna dan dukta rame sosai fiyema da lokacin da cikin na jikinta. Sumbatar goshinta yayi da hannunta yana mai jera mata addu'ar samun lafiya.
Sauran ƴan uwa kuwa da abokan arziƙi basu sami ganintaba sai washe gari, zuwa sannan ta farka Alhmdllhi. Kuma tana gane kowa da amsama kowa gaisuwarsa.
Lokacin da taga ƴan jinjirayenta da farin cikin dake shinfiɗe a fuskar AK murmushi ta dinga zubawa itama. a ranta tana musu addu'a. A fili kuwa sai ta dinga nuna alkunya su Hajiya iya na mata dariya. Sai dai har cikin ransu hakan da tai ya musu daɗi, dan yaran yanzu daba kawaici garemu akan ƴaƴaba koda na farine balle na biyu.
Sai dai kuma wata sabuwa. wannan karonma tamkar haihuwar little ruwan nono ya zamarwa yaran damuwa. Dan da sun sha cikinsu duk sai yake kumbura suyita kuka. Ga namijin da son abinci tamkar ubansa. Hankalin AK ya tashi matuƙa da hakan. Amma da Dr Mahmud ya sanar masa haka dama sukasha fama akan little sai yaɗan sami nutsuwa. Yanzuma magunguna suka haɗa mata. Amma sai Mahma tace wanann al'amari kamar bana asibiti ba. Yanada nasaba da jinnu sai an dage sosai ma Zinneerah ɗin.
Kowa yasha mamaki, amma sanin wacece ita a wannan fanin yasa duk suka amince. Itace da kanta ta fara harhaɗama Zinneerah magungunan gargajiya ta fara amfani dasu, tace insha ALLAH komai zai daidaita.