Sashe 9
Kiran Rabo Book1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi ya yi cikin ƙaunar ɗiyar ta sa ya ce, "Gaskiya bazai yu ba, ya kamata ki turo min shi mu tattauna." Ta sake ƙifta idanu wanda hakan ya zama ɗabi’arta tace, "A'a Abiy, ka ƙyale shi kawai."
"To na ƙyale shi. Sai waye kuma?." Tayi dariya ta rufe fuskar ta alamun kunya ya sake yin murmushi suka cigaba da tafiya.
Awa biyu da mintina ne suka kawo su Kano, har ƙofar gidan Hajja ya faka motar ya kalli Nayla bayan ya tsaya ya ce, "Ki shiga ki sanar da Hajja zan shigo mu gaisa." Nayla ta amsa ta fito ta ɗauki jaka ta shiga gidan dan ta sanar da Hajja zuwan Abiy ɗin.
Da sallama ta shiga cikin muryar ta mai zaƙin gaske, Hajja da take alwalar sallar azahar ta amsa yana kallon wacce ta shigo. Nan da nan fuskar Hajja ta washe Nayla ta tafi a guje ta faɗa jikinta ta ce, "Hajja ta."
Hajja tayi dariya tace, "Hauwa'u ke ce da ranar nan? Sannu da zuwa mutanen zazzau. To É—aga ni kar ki karya ni." Nayla tayi dariya ta ce, "Abiy yana waje zai shigo ku gaisa." Hajja ta tashi daga inda take ta ce, "maza jeki ki ce ya shigo, ai ban san shi ya kawo ki ba." Nayla ta juya ta fita ba jimawa suka shigo tare da Abiy.
A falo suka same ta Abiy ya zube a kan carpet ya gaishe ta. Hajja ta amsa da fara'a suka ta ce, "ya yara?."
"Lafiya lau Hajja."
"To ma sha Allah, Allah ya taimaka ya tsare." Ya amsa da amin kafin Hajja ta kalli Nayla ta tace, "Hauwa'u maza kawo masa ruwa a fridge, Yau Salma bata nan ta shiga kasuwa sai zuwa anjima zata dawo." Nayla ta ce, "Hajja ni fa shiyasa bana son zuwa wani lokacin, Na faɗa miki ki daina ƙara u ɗin nan a gaban sunana bana so." Hajja bata kula ta ba saboda sirikinta da yake wajan.
Abiy ne ya yi murmushi ita kuma ta tashi ta ƙarasa wajan fridge ta kawowa Abiy ruwan roba harda lemo. Ya ɗauki ruwan ya riƙe a hannun sa. Hajja ta ce, "Na gode fa Abdullahi da ka kawo min ƴar rigimata." Abiy yayi murmushi cikin girmamawa ya ce, "Babu komai Hajja, Allah ya ƙara lafiya."
"Amin ya Allah, Allah ya gafartawa Bilkisu."
Da Abiy da Nayla suka amsa da amin kafin Abiy ya ce, "To Hajja zan wuce, ina so na shiga Kaduna kafin duhu ya yi." Hajja ta ce, "Da wuri haka? Na ɗauka sai anjima har zan yi waya a kawo maka gurasar Kano ka kaiwa yara." Yayi murmushi ya ce, "Babu komai Hajja, a kan hanya nake daman ita kawai na sauke zan koma." Hajja ta ce, "ikon Allah, daga zuwa har zaka koma kamar ba waje mai nisa zaka koma ba? Baza ka zauna ka ci abinci ba?." Murmushi ya sake yi ya ce, "Hajja kamar wani baƙo? Babu komai wallahi" ya faɗa yana saka hannu a aljihu ya ajjiyewa Hajja kuɗi sannan ya fita Nayla ta bi bayan sa.
Yana jin godiyar da Hajja take yi yana murmushi har ya fita. Nayla da take bayansa ta tsaya kusa da shi ta ce, "Abiy Allah ya kiyaye hanya, Allah ya sauke ka Lafiya."
"Amin Mamana, ki kula kin ji? Banda yawo. Kin ga yadda gari yake babu tsoro ƙwacen waya yayi yawa, duk inda zaki je kar ki yi dare kuma ki sanar dani. Ki kuma tabbatar driver Hajja ne ya kai ki ban yarda da hawa keke ba kin ji?."
"İn sha Allah Abiy, Kuma daman Hajja bata barin fita da daddare."
"Yauwa."
"Allah ya kiyaye a gaishe da Mama" ya amsa yana shiga mota ya tafi.
    Wajan Hajja ta koma tana cewa, "Hajja me ki ke dashi a gidan nan? yunwa nake ji wallahi." Hajja ta ce, "Sarkin ci, shiyasa ki ke ƙiba ai. Duba Salma tayi abinci kafin ta shiga kasuwa." Falon Hajjan ta shiga dan a ciki kitchen yake dan gidan Hajja gidan ƴan gayu ne. Hajja ta biyo bayanta sai ta same ta ta shiga da kayan ta ɗakin da take sauka in tazo sannan ta fito.
Hajja ta kalle ta tace, "Baki zuba abincin ba?."
"Sallah zan fara yi tukunna, wai Hajja ya gidan yau babu wuta ne?."
"Wata waya ce ta solar ta katse har yanzu dai ba a zo an gyara ba." Nayla ta wara idanu ta ce, "wai kina nufin babu wuta a gidan nan?."
     "Eh yanzu dai kam babu, Wataƙila sai gobe ko jibi." Nayla ta ce, "Innalillahi! Wallahi da na sani bazan zo ba sai an gyara, Ga wayata babu chaji ina zan saka?." Ta faɗa ido na cikowa da hawaye cikin shagwaɓa. Hajja ta harare ta tace, "Sarkin shagwaɓar tsiya, gabaɗaya Abiy ya shagwaɓaki. Ki yi sallah tukkuna sai a san abinda za a yi." Nayla ta ce, "wallahi Hajja gabaɗaya raina ya ɓaci, bana son zama babu chaji" ta faɗa tana komawa cikin ɗakin tana mita ta yi alwala ta fito tayi sallar azahar sannan ta ci abinci.
    Kallon Hajja tayi da take kallon ta itama ta ce,"babu masu chaji a unguwar nan na kai?." Hajja ta ce, "a sace miki wayar ai." Nayla ta ce, "ni fa shiyasa ban cika son zuwa Kano ba wallahi, da na san babu wuta ai da na taho da power bank ɗina. Yanzu tsakani da Allah ta ya zan iya rayuwa babu chaji?."
Hajja ta ce, "In kin huta zuwa la'asar sai ki shiga wajan Aisha ki saka chaji." Nayla ta ce, "wace haka?." Hajja ta kalle ta tace, "Didi." Nayla ta wara ido ta ce, "wannan mutumin yana nan zan shiga gidan? A'a rufa min asiri kar ya naushe ni, Itama Didin in ta shigo gaiahe ki ma gaisa." Hajja tayi dariya ta ce, "babu abinda zai yi miki, ki huta sai ki shiga."
Nayla ta ce, "ni tsoronsa nake ji Hajja, Zuwana na ƙarshe harara ta ya dinga yi dan kawai ina hira da Didi. Didin ta fishi kirki shi bashi da mutunci, daman gashi da zubin abin tsoro." Hajja ta ce, "ke dai baza ki ce bashi da kirki ba, dan ya taimake ki taimakon da babu wanda ya taɓa yi miki shi a rayuwa." Ta turo baki ta ce, "ni wallahi ban so kuna tuna min wannan maganar" ta faɗa tana tashi ta shiga ɗaki. Hajja tayi dariya zuciyarta cike da farin cikin ganin jikarta ta.
     Didi kuwa cikin lokaci kaɗan ta kammala sana'ar abincin da mutane suka saka order, mai delivery ya tafi kaiwa kowa tayi wanka ta gyara gidan kamar ba ita ce tai aikin ba. Sana'arta karɓe ta, tun tana yi da kaɗan-kaɗan har ta kai ta kawo wata ran sai ta yi abinci pack ɗari da hamsin ko ɗari biyu. Sosai ta ke samun alkhairi tana kashe matsalolin gabanta, babu abinda zata cewa Allah sai godiya. Shiyasa kullum in ka ganta fes da ita, daman ga ta ƴar gayu in ta yi kwalliyya sai ka kalle ta ka sake kallo saboda babu abinda ya fi ƙarfinta.
Tana zaune bayan ta idar da sallar la'asar tana ta zullumin rashin kiranta da Omar bai yi ba tunda ya tafi Abuja, ta kuma san hakan ba halin sa bane ba. Sallama aka yi ta amsa tana jiran a shigo. Nayla ta shiga falon bayan ta sake yin sallama Didi ta amsa tana murmushi kafin ta ce, "kaii Nayla! Saukar yaushe?."
Nayla tayi murmushi ta ƙarasa ta zauna ta ce, "ɗazu da azahar nazo Didi, Ina yini."
"Lafiya lau Nayla, ya hanya?."
"Alhamdu lillah."
"Ma sha Allah, sannu da zuwa. Tunda kika koma Wancan lokacin baki sake dawowa ba, na cewa Hajja Nayla tayi mana yaji kenan."
Nayla tayi murmushi ta ce, "Wallahi Abiy ne sam baya son zama na a Kano, kuma ga makaranta shiyasa dole ina can. A cikin kwanakin nan na kammala tahfiz ɗin da na shiga shiyasa." Didi tayi dariya ta ce, "baya so ki yi nisa dashi ne." Nayla murmushi ta yi kafin ta ce, "Didi don Allah zan saka chaji." Didi ta ce, "Kamar wata baƙuwa Nayla? Jeki ki saka mana." Nayla ta tashi ta saka chaji ta dawo ta zauna.
Didi ta kalle ta ganin sai murmushi ta yi sai tayi murmushi itama ta ce, "kwanaki na ga kun sha biki sai rawa ki ke, na ce Nayla akwai son rawa." Nayla ta kulle fuskar ta tana dariya ta ce, "Didi ashe kin ga status É—in."
"Na gani tunda gashi na faÉ—a miki." Nayla ta sake yin dariya amma bata ce komai ba.
Didi ta ce, "yanzu kuma na gama aikin abincin order bara na duba miki abinci." Nayla ta ce, "Na ƙoshi Didi, ina zuwa gidan Hajja na ci abinci." Didi ta ce, "Daman ke ai bakya cin abincina, baki taɓa ci ba, kullum kin ƙoshi ki ke cewa."
"Ba haka bane ba wallahi, ina zuwa na ci abinci bana jin yunwa."
"Amma dai zaki mana shekara ko?." Nayla ta wara ido ta ce, "taɓ! Ai ko sati biyu bana tunanin zan yi a nan." Didi tayi dariya ta ce, "Abiy yafi so ya dinga ganin ki kullum, da gaskiyarsa."
Nayla ta murmusa tana jin daɗin zama da Didi, saboda mace ce mai fara'a da wasa ga saurin sabo. Ta zama tamkar jikar Hajja itama, tana matuƙar girmama Hajja sosai, ko me yake damunta Hajja take iya faɗawa ta bata shawara. Shiyasa duk wani mai zuwa gidan Hajja ya san Didi saboda gidan zuwan ta ne, ko biki ake a ɓangaren Hajja Didi na zuwa kuma an santa sosai. Didi ta miƙe ta shiga ɗaki tunawa akwai abinda zata yi tabar Nayla a zaune tana ƙarewa falon kallo.
     “Wacece ke!?.â€
"To na ƙyale shi. Sai waye kuma?." Tayi dariya ta rufe fuskar ta alamun kunya ya sake yin murmushi suka cigaba da tafiya.
Awa biyu da mintina ne suka kawo su Kano, har ƙofar gidan Hajja ya faka motar ya kalli Nayla bayan ya tsaya ya ce, "Ki shiga ki sanar da Hajja zan shigo mu gaisa." Nayla ta amsa ta fito ta ɗauki jaka ta shiga gidan dan ta sanar da Hajja zuwan Abiy ɗin.
Da sallama ta shiga cikin muryar ta mai zaƙin gaske, Hajja da take alwalar sallar azahar ta amsa yana kallon wacce ta shigo. Nan da nan fuskar Hajja ta washe Nayla ta tafi a guje ta faɗa jikinta ta ce, "Hajja ta."
Hajja tayi dariya tace, "Hauwa'u ke ce da ranar nan? Sannu da zuwa mutanen zazzau. To É—aga ni kar ki karya ni." Nayla tayi dariya ta ce, "Abiy yana waje zai shigo ku gaisa." Hajja ta tashi daga inda take ta ce, "maza jeki ki ce ya shigo, ai ban san shi ya kawo ki ba." Nayla ta juya ta fita ba jimawa suka shigo tare da Abiy.
A falo suka same ta Abiy ya zube a kan carpet ya gaishe ta. Hajja ta amsa da fara'a suka ta ce, "ya yara?."
"Lafiya lau Hajja."
"To ma sha Allah, Allah ya taimaka ya tsare." Ya amsa da amin kafin Hajja ta kalli Nayla ta tace, "Hauwa'u maza kawo masa ruwa a fridge, Yau Salma bata nan ta shiga kasuwa sai zuwa anjima zata dawo." Nayla ta ce, "Hajja ni fa shiyasa bana son zuwa wani lokacin, Na faɗa miki ki daina ƙara u ɗin nan a gaban sunana bana so." Hajja bata kula ta ba saboda sirikinta da yake wajan.
Abiy ne ya yi murmushi ita kuma ta tashi ta ƙarasa wajan fridge ta kawowa Abiy ruwan roba harda lemo. Ya ɗauki ruwan ya riƙe a hannun sa. Hajja ta ce, "Na gode fa Abdullahi da ka kawo min ƴar rigimata." Abiy yayi murmushi cikin girmamawa ya ce, "Babu komai Hajja, Allah ya ƙara lafiya."
"Amin ya Allah, Allah ya gafartawa Bilkisu."
Da Abiy da Nayla suka amsa da amin kafin Abiy ya ce, "To Hajja zan wuce, ina so na shiga Kaduna kafin duhu ya yi." Hajja ta ce, "Da wuri haka? Na ɗauka sai anjima har zan yi waya a kawo maka gurasar Kano ka kaiwa yara." Yayi murmushi ya ce, "Babu komai Hajja, a kan hanya nake daman ita kawai na sauke zan koma." Hajja ta ce, "ikon Allah, daga zuwa har zaka koma kamar ba waje mai nisa zaka koma ba? Baza ka zauna ka ci abinci ba?." Murmushi ya sake yi ya ce, "Hajja kamar wani baƙo? Babu komai wallahi" ya faɗa yana saka hannu a aljihu ya ajjiyewa Hajja kuɗi sannan ya fita Nayla ta bi bayan sa.
Yana jin godiyar da Hajja take yi yana murmushi har ya fita. Nayla da take bayansa ta tsaya kusa da shi ta ce, "Abiy Allah ya kiyaye hanya, Allah ya sauke ka Lafiya."
"Amin Mamana, ki kula kin ji? Banda yawo. Kin ga yadda gari yake babu tsoro ƙwacen waya yayi yawa, duk inda zaki je kar ki yi dare kuma ki sanar dani. Ki kuma tabbatar driver Hajja ne ya kai ki ban yarda da hawa keke ba kin ji?."
"İn sha Allah Abiy, Kuma daman Hajja bata barin fita da daddare."
"Yauwa."
"Allah ya kiyaye a gaishe da Mama" ya amsa yana shiga mota ya tafi.
    Wajan Hajja ta koma tana cewa, "Hajja me ki ke dashi a gidan nan? yunwa nake ji wallahi." Hajja ta ce, "Sarkin ci, shiyasa ki ke ƙiba ai. Duba Salma tayi abinci kafin ta shiga kasuwa." Falon Hajjan ta shiga dan a ciki kitchen yake dan gidan Hajja gidan ƴan gayu ne. Hajja ta biyo bayanta sai ta same ta ta shiga da kayan ta ɗakin da take sauka in tazo sannan ta fito.
Hajja ta kalle ta tace, "Baki zuba abincin ba?."
"Sallah zan fara yi tukunna, wai Hajja ya gidan yau babu wuta ne?."
"Wata waya ce ta solar ta katse har yanzu dai ba a zo an gyara ba." Nayla ta wara idanu ta ce, "wai kina nufin babu wuta a gidan nan?."
     "Eh yanzu dai kam babu, Wataƙila sai gobe ko jibi." Nayla ta ce, "Innalillahi! Wallahi da na sani bazan zo ba sai an gyara, Ga wayata babu chaji ina zan saka?." Ta faɗa ido na cikowa da hawaye cikin shagwaɓa. Hajja ta harare ta tace, "Sarkin shagwaɓar tsiya, gabaɗaya Abiy ya shagwaɓaki. Ki yi sallah tukkuna sai a san abinda za a yi." Nayla ta ce, "wallahi Hajja gabaɗaya raina ya ɓaci, bana son zama babu chaji" ta faɗa tana komawa cikin ɗakin tana mita ta yi alwala ta fito tayi sallar azahar sannan ta ci abinci.
    Kallon Hajja tayi da take kallon ta itama ta ce,"babu masu chaji a unguwar nan na kai?." Hajja ta ce, "a sace miki wayar ai." Nayla ta ce, "ni fa shiyasa ban cika son zuwa Kano ba wallahi, da na san babu wuta ai da na taho da power bank ɗina. Yanzu tsakani da Allah ta ya zan iya rayuwa babu chaji?."
Hajja ta ce, "In kin huta zuwa la'asar sai ki shiga wajan Aisha ki saka chaji." Nayla ta ce, "wace haka?." Hajja ta kalle ta tace, "Didi." Nayla ta wara ido ta ce, "wannan mutumin yana nan zan shiga gidan? A'a rufa min asiri kar ya naushe ni, Itama Didin in ta shigo gaiahe ki ma gaisa." Hajja tayi dariya ta ce, "babu abinda zai yi miki, ki huta sai ki shiga."
Nayla ta ce, "ni tsoronsa nake ji Hajja, Zuwana na ƙarshe harara ta ya dinga yi dan kawai ina hira da Didi. Didin ta fishi kirki shi bashi da mutunci, daman gashi da zubin abin tsoro." Hajja ta ce, "ke dai baza ki ce bashi da kirki ba, dan ya taimake ki taimakon da babu wanda ya taɓa yi miki shi a rayuwa." Ta turo baki ta ce, "ni wallahi ban so kuna tuna min wannan maganar" ta faɗa tana tashi ta shiga ɗaki. Hajja tayi dariya zuciyarta cike da farin cikin ganin jikarta ta.
     Didi kuwa cikin lokaci kaɗan ta kammala sana'ar abincin da mutane suka saka order, mai delivery ya tafi kaiwa kowa tayi wanka ta gyara gidan kamar ba ita ce tai aikin ba. Sana'arta karɓe ta, tun tana yi da kaɗan-kaɗan har ta kai ta kawo wata ran sai ta yi abinci pack ɗari da hamsin ko ɗari biyu. Sosai ta ke samun alkhairi tana kashe matsalolin gabanta, babu abinda zata cewa Allah sai godiya. Shiyasa kullum in ka ganta fes da ita, daman ga ta ƴar gayu in ta yi kwalliyya sai ka kalle ta ka sake kallo saboda babu abinda ya fi ƙarfinta.
Tana zaune bayan ta idar da sallar la'asar tana ta zullumin rashin kiranta da Omar bai yi ba tunda ya tafi Abuja, ta kuma san hakan ba halin sa bane ba. Sallama aka yi ta amsa tana jiran a shigo. Nayla ta shiga falon bayan ta sake yin sallama Didi ta amsa tana murmushi kafin ta ce, "kaii Nayla! Saukar yaushe?."
Nayla tayi murmushi ta ƙarasa ta zauna ta ce, "ɗazu da azahar nazo Didi, Ina yini."
"Lafiya lau Nayla, ya hanya?."
"Alhamdu lillah."
"Ma sha Allah, sannu da zuwa. Tunda kika koma Wancan lokacin baki sake dawowa ba, na cewa Hajja Nayla tayi mana yaji kenan."
Nayla tayi murmushi ta ce, "Wallahi Abiy ne sam baya son zama na a Kano, kuma ga makaranta shiyasa dole ina can. A cikin kwanakin nan na kammala tahfiz ɗin da na shiga shiyasa." Didi tayi dariya ta ce, "baya so ki yi nisa dashi ne." Nayla murmushi ta yi kafin ta ce, "Didi don Allah zan saka chaji." Didi ta ce, "Kamar wata baƙuwa Nayla? Jeki ki saka mana." Nayla ta tashi ta saka chaji ta dawo ta zauna.
Didi ta kalle ta ganin sai murmushi ta yi sai tayi murmushi itama ta ce, "kwanaki na ga kun sha biki sai rawa ki ke, na ce Nayla akwai son rawa." Nayla ta kulle fuskar ta tana dariya ta ce, "Didi ashe kin ga status É—in."
"Na gani tunda gashi na faÉ—a miki." Nayla ta sake yin dariya amma bata ce komai ba.
Didi ta ce, "yanzu kuma na gama aikin abincin order bara na duba miki abinci." Nayla ta ce, "Na ƙoshi Didi, ina zuwa gidan Hajja na ci abinci." Didi ta ce, "Daman ke ai bakya cin abincina, baki taɓa ci ba, kullum kin ƙoshi ki ke cewa."
"Ba haka bane ba wallahi, ina zuwa na ci abinci bana jin yunwa."
"Amma dai zaki mana shekara ko?." Nayla ta wara ido ta ce, "taɓ! Ai ko sati biyu bana tunanin zan yi a nan." Didi tayi dariya ta ce, "Abiy yafi so ya dinga ganin ki kullum, da gaskiyarsa."
Nayla ta murmusa tana jin daɗin zama da Didi, saboda mace ce mai fara'a da wasa ga saurin sabo. Ta zama tamkar jikar Hajja itama, tana matuƙar girmama Hajja sosai, ko me yake damunta Hajja take iya faɗawa ta bata shawara. Shiyasa duk wani mai zuwa gidan Hajja ya san Didi saboda gidan zuwan ta ne, ko biki ake a ɓangaren Hajja Didi na zuwa kuma an santa sosai. Didi ta miƙe ta shiga ɗaki tunawa akwai abinda zata yi tabar Nayla a zaune tana ƙarewa falon kallo.
     “Wacece ke!?.â€