Sashe 28
Kiran Rabo Book1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abu taji an saka mata a bayanta kamar wuƙa zata juya aka ce, "kina juyawa wallahi sai na farɗe miki bayanki, kawo wayar hannunki." Narma jiki ya fara rawa hannu na karkarwa ta kuma kasa miƙar wayar.
"Baza ki bayar ba sai na kashe ki?." Hannunta rawa yake yi garin ta miƙa masa wayar garin ya yanke ya da wuƙar a hannuta. Narma tayi ƙara tana kallon hannunta, shi kuma ya yi cikin duhu a guje bai sake waiwayen ta.
Hannunta jini yake yi tana kuka ga tsoron tashin hankali, sai rawa jikinta yake yi dan bata taɓa tsintar kanta a irin wanna tashin hankalin ba sai a lokacin.
*Book 1 free ne*
*Book 2&3 paid ne, akan naira 500 kacal*
*VIP group 1k*
*VIP2 on ArewaBooks.*
*domin biyan kudi ka tuntubi wannan number via WhatsApp*
wa.me/2349030398006
Dm to subscribe yours.
Nana Haleemaâ¤ï¸
*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025
Â Â Â Â Â Â Â Â©ï¸ *Nana Haleema.*
Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.
*Book 1*
*P 13.*
Omar tun daga nesa ya gane motar ya kuma ganta a tsaye a wajan, a hankali ya ƙaraso kamar zai gifta sai yaji tana kuka tana cewa, "a taimake ni don Allah, a taimaka min jinina zai ƙare."
Ɗaga pcap ɗin ya yi ya kalle ta suka haɗa ido ganinsa ta matso kusa dashi a gigice da fitar hankali sosai ta ce, "Tiger sun ƙwace min waya, sun yanke ki a hannu, jinina zai ɗare ka taimaka min zasu kashe ni." Ya kula gabaɗaya a gigice take har tana riƙe shi bata san ma tayi hakan ba saboda tsoro.
Kallon hanyar ya yi ya sake kallon ta yaga yadda take hawaye shaɓe-shaɓe tana riƙe da hannu kamar wacce aka guntulewa hannu, kallon ɗan yankan da yake hannun ta ya yi tare da yin tsaki a bayyane har lokacin bata saki rigarsa.
"Take me to hospital please, ka kaini ayi min TT kar na samu ciwo." Kamar ba zai yi mata ba magana ba sai yaji ta ce, "Don Allah ka ɗauke ni daga nan, tsoro nake ji, ka taimaka min don Allah." Yadda take kuka tana ƙoƙarin shege masa jiki ne ya saka ya riƙe hannunta ya janye ta ya buɗe gaban motar ya ce, "shiga." Ba musu ta shiga jikin ta na shaking sosai ya buɗe mazaunin driver yana kunna motar ta tashi ya ja motar ya nufi asibiti mafi kusa.
Wani private hospital suka ƙarasa ya ajjiye motar ya kalle ta yaga sai kuka take yi ta riƙe hannunta, shi wallahi mamaki take bashi, ɗan wannan yankan take yiwa kuka kamar wacce aka yanka sosai. Ya kalle ta ya ce, "Fita ki je." Ta buɗe murfin motar ta kalle shi ce, "nayi bleeding sosai in na tashi jiri zan yi."
"Ko" ya furta a bayyane yana kallon ta.
Fita ya yi daga motar ya ce, "Fito" ya furta a kausashe dan ya ga tana neman mayar dashi ɗan aikinta, jin yadda tayi magana ya saka ta sakko amma tana fitowa tayi kamar zata faɗi, da hanzari kuwa ta riƙe shi tana cewa, "na ce maka i'm dizzy bazan iya tafiya ba." Ɗan tsaki ya yi ya janye ta a jikinsa ya kalli bayan sa yaga ma'aikatan asibitin nan ya yi musu magana suka riƙe ta suka shiga da ita.
Bai shiga ba ya tsaya a jikin motar sai ga wacce ta shiga da ita tazo tayi masa magana dole ya shiga. Yana shiga ya ganta sai kuka take yi an ɗaure hannun da bandage, likitan da ya gama yi mata dressing wound ɗin ya kalle shi ya ce, "Oga ka taya mu rarrashinta taƙi yin shiru."
Kallon ta ya yi suka haɗa ido sai wani juya ido take yi kamar mage. Ƙaramin tsaki ya yi Narma ta kalle shi ta ce, "kayi clearing bill ɗin, wayata da atm ɗina duk sun ƙwace." Sai a sannan ya tuna ma da batun wayar ta bai ce komai ba ya yi musu transfer a take suka fito tare da ledar magani a hannun nurse ɗin wai baza ta iya riƙewa.
Sai tafiya take kamar mara jini ita a lallai an yanke ta, gabaɗaya haushi take bashi yadda take langwaɓewa kamar wacce aka jiwa ciwon kirki. Suna zuwa gaban motar ta shiga bayan motar shi kuma ya shiga gaba ya ja motar da gudun gaske.
Da yake kwanciya tayi bata san inda suka nufa ba sai da taji ya tsaya yana niyar fita, ta miƙe ta gansu a wani waje mai duhu ta ce, "ina zaka je?." Kallon ta ya yi jin yadda tayi maganar a firgice bai amsa ba, "don Allah ka je dani bazan iya zama ni kaɗai ba, wallahi i'm scared." Nan da nan jikinta ya fara shaking cikin tsananin tsoro tana ganin kamar abinda ya faru zai sake faruwa.
Narma ganin ya yi mata banza yana niyar fita sai itama ta fito da sauri ta ce, "bazan iya zama ba, don Allah ka je dani tsoro nake ji."
"Inda zan je ba wajan zuwan ki bane" ya faÉ—a without looking her.
"Ni dai zan je, don Allah ka je dani." Kallon ta ya yi sai kawai ya yi gaba ta bishi a baya, kanta har sarawa yake yi saboda ciwon da ya fara yi mata.
Wani waje taga sun shiga sai gasu a gaban dandazon ƴan daba sama da su ashirin a wajan sun baje wayoyi da atm cards da kuɗi. Wajan banda warin wiwi babu abinda yake yi, ga hayaƙin taba ya cika wajan.
Ganin an shigo suka miƙe duk suka fito da makamai ɗaya daga cikin yana cewa, "wanne mai ƙarar kwanan ne yazo inda bazai fita ba?." Narma ta ɓuya a bayasa gabanta na faɗuwa tana dan sanin shigowa wajan. Haske shi suka yi da fitila shi kuma ya ɗaga pcap ɗin kansa, ganin fuskarsa ta bayyana sai suka haɗa baki suka ce, "Damisa!."
Babban cikin su ya ce, "Allah ya ja zamanın Damisa ƙi sabo, mu je madugu uban tafiya, barkono ka fi ƙarfin shiƙa. Allah ya sa ba laifi mu ka yi ba, na ganka kwatsam babu sanarwa." Omar ya bisu da kallo yana kallon wayoyin da suke ƙasa ya ce, "waye ya ƙwace waya a ƙasan gada?." Ɗaya daga cikin su ya ce, "Madugu ai ƙasan gada da yawa, daidai ina ka ke nufi?." Narma ya juya yana kalla ya ce, "fito." Sai ta riƙe rigarsa tana kwanciya a bayansa jikinta na rawa sosai. Hannunta ya jawo kafin ya saki hannun na ta ya ce, "waye ya karɓi wayarta?."
Wanda ya ƙwace mata wayar ya kalle ta ya ce, "afuwan Jan wuya ni ne." Da hannu ya yi masa alamun da ya zo, ba musu ya taso yazo yana zuwa ya daki ƙewarsa ya ce, "Sai ka ji mata ciwo?." Ya sunkuyar da kai ya ce, "afuwan madugu ban san antyn mu ba ce." Harararsa ya yi ya kalli Narma da tayi tsuru ya ce, "bata haƙuri." Kallon Narma ya yi ya ce, "ki yi hakuri Anty." Firgita tayi da maganarsa jin ta wani iri kana ji ka san a buge ya ke, ta yi tsalle cikin tsoro ta koma bayansa ta riƙe shi jiki na rawa.
Omar ya runtse ido jin jikinta a bayansa a kwance, wani iri yake ji baya so tana riƙe shi ɗin nan, shi in ba Didi ba babu macen da ya taɓa haɗa jiki da ita, ko ita tunda ya girma bai haɗa jiki da ita ba sai dai ya riƙe hannunta ko su gaisa da safe, shiyasa yake jin wani iri a jikinsa in ta riƙe shi. Daurewa ya yi ya ce, "ɗauko min wayar, sannan kar ka naga an taɓa mata komai."
Ba musu ya juya aka fara bincike wayar sai ga iPhone 16 kalar pink da atm ɗinta a baya an ɗauko ya miƙa masa yana cewa, "wallahi Allah ne ya taimaka Magudu da yanzu ba labarin nan ake yi ba, na je inda za a kwashe kuɗaɗen ciki baya nan." Omar ya karɓi wayar yana kallon su ya ce, "sauran wayoyin fa?."
Wanda yake zaune ya ce, "Damisa ganimar yau ce." Ya bisu da kallo É—aya bayan É—aya kana ya ce, "tattaro min su duka." A tare suka haÉ—a baki suka ce, "Haba Damisa wannan yawa ka ke yi fa, wannan ba halin ka bane." Fuska ya sake É—aurewa ya ce, "Ku tattaro min ko na tattara har da ku." Babban ciki ya ce, "gaskiya Madugu hakan bai yi ba, ka san wahalar da muka sha....." kallon da ya yi masa ya saka ya ce, "Kawai dan kaine wallahi, amma da ka san babu wani da ya isa ya saka mu bada wayar nan koda gwamna ne wallahi, ku bashi."
Tattaro wayoyin suka yi suka zuba a wata jaka aka miƙa masa ya karɓa yana kallon su duk sun ɗaure fuska alamun basu ji daɗin hakan ba. Ya sake kallon su ya ce, "Ku riƙe kawai" ya faɗa yana miƙa musu.
" ka je dasu kawai, amma kawai dan babu yadda zamu yi da kai ne."
"Ban son wannan ɗabi'ar da ku ke yi, in ba ku daina ba...." Sai ya katse maganar ya karkaɗa musu yatsansa. Ya motsa zai bar wajan ta sake riƙe shi gam.
Tsaki ya yi ya ce, "Malama ki sake ni!." Yadda ya yi maganar a kausashe ya saka ta sakinsa amma duk da haka tana rike da gefen rigarsa suka fita daga wajan. Bayan motar ta shiga a tsorace ya cilla mata wayar ta ya ce, "Kano ba Abuja bane ki san inda zaki dinga shiga." Bata ce komai ba ya ja motar kai tsaye police station ya wuce.
Nan ma sai da ta bishi ya samu dpo yana niyar fita suka gaisa ya bashi wayar ya ce, "wayoyin da aka ƙwace yau ne, ku saka a duniya a mene masu su a basu wayar." Dpo ya kalle shi ya ce, "ina wanda suka ƙwace wayoyin su ke?."
"Ni dai wayoyin na kawo maka in na mayar shikenan." Ya karɓa ya ce, "amma samun masu aikata laifin ya fi samun wayoyin amfani. Tiger da zaka taimaka a kama su da kayi babban aiki."
"Baza ki bayar ba sai na kashe ki?." Hannunta rawa yake yi garin ta miƙa masa wayar garin ya yanke ya da wuƙar a hannuta. Narma tayi ƙara tana kallon hannunta, shi kuma ya yi cikin duhu a guje bai sake waiwayen ta.
Hannunta jini yake yi tana kuka ga tsoron tashin hankali, sai rawa jikinta yake yi dan bata taɓa tsintar kanta a irin wanna tashin hankalin ba sai a lokacin.
*Book 1 free ne*
*Book 2&3 paid ne, akan naira 500 kacal*
*VIP group 1k*
*VIP2 on ArewaBooks.*
*domin biyan kudi ka tuntubi wannan number via WhatsApp*
wa.me/2349030398006
Dm to subscribe yours.
Nana Haleemaâ¤ï¸
*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025
Â Â Â Â Â Â Â Â©ï¸ *Nana Haleema.*
Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.
*Book 1*
*P 13.*
Omar tun daga nesa ya gane motar ya kuma ganta a tsaye a wajan, a hankali ya ƙaraso kamar zai gifta sai yaji tana kuka tana cewa, "a taimake ni don Allah, a taimaka min jinina zai ƙare."
Ɗaga pcap ɗin ya yi ya kalle ta suka haɗa ido ganinsa ta matso kusa dashi a gigice da fitar hankali sosai ta ce, "Tiger sun ƙwace min waya, sun yanke ki a hannu, jinina zai ɗare ka taimaka min zasu kashe ni." Ya kula gabaɗaya a gigice take har tana riƙe shi bata san ma tayi hakan ba saboda tsoro.
Kallon hanyar ya yi ya sake kallon ta yaga yadda take hawaye shaɓe-shaɓe tana riƙe da hannu kamar wacce aka guntulewa hannu, kallon ɗan yankan da yake hannun ta ya yi tare da yin tsaki a bayyane har lokacin bata saki rigarsa.
"Take me to hospital please, ka kaini ayi min TT kar na samu ciwo." Kamar ba zai yi mata ba magana ba sai yaji ta ce, "Don Allah ka ɗauke ni daga nan, tsoro nake ji, ka taimaka min don Allah." Yadda take kuka tana ƙoƙarin shege masa jiki ne ya saka ya riƙe hannunta ya janye ta ya buɗe gaban motar ya ce, "shiga." Ba musu ta shiga jikin ta na shaking sosai ya buɗe mazaunin driver yana kunna motar ta tashi ya ja motar ya nufi asibiti mafi kusa.
Wani private hospital suka ƙarasa ya ajjiye motar ya kalle ta yaga sai kuka take yi ta riƙe hannunta, shi wallahi mamaki take bashi, ɗan wannan yankan take yiwa kuka kamar wacce aka yanka sosai. Ya kalle ta ya ce, "Fita ki je." Ta buɗe murfin motar ta kalle shi ce, "nayi bleeding sosai in na tashi jiri zan yi."
"Ko" ya furta a bayyane yana kallon ta.
Fita ya yi daga motar ya ce, "Fito" ya furta a kausashe dan ya ga tana neman mayar dashi ɗan aikinta, jin yadda tayi magana ya saka ta sakko amma tana fitowa tayi kamar zata faɗi, da hanzari kuwa ta riƙe shi tana cewa, "na ce maka i'm dizzy bazan iya tafiya ba." Ɗan tsaki ya yi ya janye ta a jikinsa ya kalli bayan sa yaga ma'aikatan asibitin nan ya yi musu magana suka riƙe ta suka shiga da ita.
Bai shiga ba ya tsaya a jikin motar sai ga wacce ta shiga da ita tazo tayi masa magana dole ya shiga. Yana shiga ya ganta sai kuka take yi an ɗaure hannun da bandage, likitan da ya gama yi mata dressing wound ɗin ya kalle shi ya ce, "Oga ka taya mu rarrashinta taƙi yin shiru."
Kallon ta ya yi suka haɗa ido sai wani juya ido take yi kamar mage. Ƙaramin tsaki ya yi Narma ta kalle shi ta ce, "kayi clearing bill ɗin, wayata da atm ɗina duk sun ƙwace." Sai a sannan ya tuna ma da batun wayar ta bai ce komai ba ya yi musu transfer a take suka fito tare da ledar magani a hannun nurse ɗin wai baza ta iya riƙewa.
Sai tafiya take kamar mara jini ita a lallai an yanke ta, gabaɗaya haushi take bashi yadda take langwaɓewa kamar wacce aka jiwa ciwon kirki. Suna zuwa gaban motar ta shiga bayan motar shi kuma ya shiga gaba ya ja motar da gudun gaske.
Da yake kwanciya tayi bata san inda suka nufa ba sai da taji ya tsaya yana niyar fita, ta miƙe ta gansu a wani waje mai duhu ta ce, "ina zaka je?." Kallon ta ya yi jin yadda tayi maganar a firgice bai amsa ba, "don Allah ka je dani bazan iya zama ni kaɗai ba, wallahi i'm scared." Nan da nan jikinta ya fara shaking cikin tsananin tsoro tana ganin kamar abinda ya faru zai sake faruwa.
Narma ganin ya yi mata banza yana niyar fita sai itama ta fito da sauri ta ce, "bazan iya zama ba, don Allah ka je dani tsoro nake ji."
"Inda zan je ba wajan zuwan ki bane" ya faÉ—a without looking her.
"Ni dai zan je, don Allah ka je dani." Kallon ta ya yi sai kawai ya yi gaba ta bishi a baya, kanta har sarawa yake yi saboda ciwon da ya fara yi mata.
Wani waje taga sun shiga sai gasu a gaban dandazon ƴan daba sama da su ashirin a wajan sun baje wayoyi da atm cards da kuɗi. Wajan banda warin wiwi babu abinda yake yi, ga hayaƙin taba ya cika wajan.
Ganin an shigo suka miƙe duk suka fito da makamai ɗaya daga cikin yana cewa, "wanne mai ƙarar kwanan ne yazo inda bazai fita ba?." Narma ta ɓuya a bayasa gabanta na faɗuwa tana dan sanin shigowa wajan. Haske shi suka yi da fitila shi kuma ya ɗaga pcap ɗin kansa, ganin fuskarsa ta bayyana sai suka haɗa baki suka ce, "Damisa!."
Babban cikin su ya ce, "Allah ya ja zamanın Damisa ƙi sabo, mu je madugu uban tafiya, barkono ka fi ƙarfin shiƙa. Allah ya sa ba laifi mu ka yi ba, na ganka kwatsam babu sanarwa." Omar ya bisu da kallo yana kallon wayoyin da suke ƙasa ya ce, "waye ya ƙwace waya a ƙasan gada?." Ɗaya daga cikin su ya ce, "Madugu ai ƙasan gada da yawa, daidai ina ka ke nufi?." Narma ya juya yana kalla ya ce, "fito." Sai ta riƙe rigarsa tana kwanciya a bayansa jikinta na rawa sosai. Hannunta ya jawo kafin ya saki hannun na ta ya ce, "waye ya karɓi wayarta?."
Wanda ya ƙwace mata wayar ya kalle ta ya ce, "afuwan Jan wuya ni ne." Da hannu ya yi masa alamun da ya zo, ba musu ya taso yazo yana zuwa ya daki ƙewarsa ya ce, "Sai ka ji mata ciwo?." Ya sunkuyar da kai ya ce, "afuwan madugu ban san antyn mu ba ce." Harararsa ya yi ya kalli Narma da tayi tsuru ya ce, "bata haƙuri." Kallon Narma ya yi ya ce, "ki yi hakuri Anty." Firgita tayi da maganarsa jin ta wani iri kana ji ka san a buge ya ke, ta yi tsalle cikin tsoro ta koma bayansa ta riƙe shi jiki na rawa.
Omar ya runtse ido jin jikinta a bayansa a kwance, wani iri yake ji baya so tana riƙe shi ɗin nan, shi in ba Didi ba babu macen da ya taɓa haɗa jiki da ita, ko ita tunda ya girma bai haɗa jiki da ita ba sai dai ya riƙe hannunta ko su gaisa da safe, shiyasa yake jin wani iri a jikinsa in ta riƙe shi. Daurewa ya yi ya ce, "ɗauko min wayar, sannan kar ka naga an taɓa mata komai."
Ba musu ya juya aka fara bincike wayar sai ga iPhone 16 kalar pink da atm ɗinta a baya an ɗauko ya miƙa masa yana cewa, "wallahi Allah ne ya taimaka Magudu da yanzu ba labarin nan ake yi ba, na je inda za a kwashe kuɗaɗen ciki baya nan." Omar ya karɓi wayar yana kallon su ya ce, "sauran wayoyin fa?."
Wanda yake zaune ya ce, "Damisa ganimar yau ce." Ya bisu da kallo É—aya bayan É—aya kana ya ce, "tattaro min su duka." A tare suka haÉ—a baki suka ce, "Haba Damisa wannan yawa ka ke yi fa, wannan ba halin ka bane." Fuska ya sake É—aurewa ya ce, "Ku tattaro min ko na tattara har da ku." Babban ciki ya ce, "gaskiya Madugu hakan bai yi ba, ka san wahalar da muka sha....." kallon da ya yi masa ya saka ya ce, "Kawai dan kaine wallahi, amma da ka san babu wani da ya isa ya saka mu bada wayar nan koda gwamna ne wallahi, ku bashi."
Tattaro wayoyin suka yi suka zuba a wata jaka aka miƙa masa ya karɓa yana kallon su duk sun ɗaure fuska alamun basu ji daɗin hakan ba. Ya sake kallon su ya ce, "Ku riƙe kawai" ya faɗa yana miƙa musu.
" ka je dasu kawai, amma kawai dan babu yadda zamu yi da kai ne."
"Ban son wannan ɗabi'ar da ku ke yi, in ba ku daina ba...." Sai ya katse maganar ya karkaɗa musu yatsansa. Ya motsa zai bar wajan ta sake riƙe shi gam.
Tsaki ya yi ya ce, "Malama ki sake ni!." Yadda ya yi maganar a kausashe ya saka ta sakinsa amma duk da haka tana rike da gefen rigarsa suka fita daga wajan. Bayan motar ta shiga a tsorace ya cilla mata wayar ta ya ce, "Kano ba Abuja bane ki san inda zaki dinga shiga." Bata ce komai ba ya ja motar kai tsaye police station ya wuce.
Nan ma sai da ta bishi ya samu dpo yana niyar fita suka gaisa ya bashi wayar ya ce, "wayoyin da aka ƙwace yau ne, ku saka a duniya a mene masu su a basu wayar." Dpo ya kalle shi ya ce, "ina wanda suka ƙwace wayoyin su ke?."
"Ni dai wayoyin na kawo maka in na mayar shikenan." Ya karɓa ya ce, "amma samun masu aikata laifin ya fi samun wayoyin amfani. Tiger da zaka taimaka a kama su da kayi babban aiki."