← Book details Kiran Rabo Book1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 54

Sashe 11

Kiran Rabo Book1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Book 1 free ne*
*Book 2&3 paid ne, akan naira 500 kacal*
*VIP group 1k*
*VIP2 on ArewaBooks.*
*domin biyan kudi ka tuntubi wannan number via WhatsApp*
wa.me/2349030398006
Dm to subscribe yours.

Nana Haleema❤️

*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025

             ©️ *Nana Haleema.*

Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.

https://chat.whatsapp.com/K8IEI39TB803y9pEtzMmdp?mode=ems_copy_t

*Book 1*
*P 05*

Didi da ta bar wajansa wajan Nayla ta koma ta zauna kusa da ita ta ce, "na bar ki ke kaɗai ko?." Ganin Nayla a tsorace har lokacin sai ta tausasa murya ta ce, "har yanzu a tsorace ke ki ke? Ki nutsu mana." Nayla ita dai gaban ta faɗuwa yake saboda duk abinda suke faɗa tana ji, tana ji Didi tana ce masa kar ya yi mata komai duk shine ta sake firgita. Dana sanin shigowa gidan ta mamaye mata zuciya, ji take ina ma bata shigo ba ta haƙura da chajin wayar.

Didi ta kalli Nayla ganin har lokacin tsorace ta ke sai tayi dariya ta ce, "Wallahi dariya ki ke bani, yadda ki ka firgita haka kamar kin ga wani abin tsoro, In kina nuna kina tsoronsa har haka sai ya fi cewa zai latsa ki. Omar fa yana da sauƙin kai, kawai shi bashi da saurin sabo ne, amma na tabbatar miki kafin ki bar Kano zaku saba, Zaki yi mamakin yadda yake da hira da kuma yawan murmushi." Murmushin yaƙe kawai Nayla tayi dan kawai tana jin ta ne, amma ta yaya zasu saba da dashi bayan abinda ya faru.

Didi ganin tayi shiru ta dinga jan ta da hira kaɗan-kaɗan tana amsawa duk da har lokacin a tsorace take matuƙa. Agogo ta kalla sai ta kalli Didi ta ce, "Didi bara na ɗauki wayata na tafi saboda zan kira Abiy na ji ya koma gida lafiya." Didi ta kalle ta tace, "Ko dai kina so ki gudu saboda Omar?."
"A'a Didi, Abiy zan kira na tabbatar yana jiran kira na."
"To Shikenan. Ina jiranki da daddare ki zo ki taya ni hira." Nayla ta É—aga kai kawai ta tashi ta É—auki wayarta da charger tayi hanyar fita Didi na bayanta.

Tana fitowa daga falon yana shigowa gidan idanunsa ya faɗa cikin na ta. Nayla bata san lokacin da wayar charger sun suɓuce a hannunta ba, wayar ta faɗi ta ɗan yi ƙara amma bata duba ba jikinta ya cigaba da rawa. Hannunta Didi ta riƙe ta bayanta, Nayla ta sunkuyar da kai cikin tsoro. Didi ta kalle shi bata ce masa komai ta kalli Nayla ta ce, "Nayla don Allah ki kwantar da hankalinki, kin ga kin yar da wayarki" ta faɗa tana sunkuya ta ɗauki waya da charger ta riƙe mata hannunta har suka bar cikin gidan.

Ai Nayla bata iya cewa Didi komai ba, tana bata wayar ta kwasa a guje ta yi hanyar gidan Hajja. Didi tayi dariya ta dawo cikin gidan tana dariya suka sake haɗuwa da shi cikin dariya ta ce, "Kaji tsoron Allah ka daina tsorara yaran mutane don Allah, haba wannan bala'i daga haɗa ido da kai duk ta ruɗe?. Ni ban ga meye abin tsoron a nan ba." Bai ce komai ba ya sake shiga cikin gidan tayi dariya ta bi bayansa tana jinjina ƙarfin tsoron da Nayla take masa.

Nayla a haka ta faɗa cikin gida a firgice Hajja da Salma da suke zaune a falo suka ganta kamar an cillo ta Hajja ta ce, "ke lafiya?." Nayla ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "Hajja har abada bazan sake shiga gidan Didi ba, na gama shiga gidan ko me za a bani." Salma ta wara ido ta ce, "shiyasa daman da Hajja ta ce min kina can nace wallahi bazan je ba, in yaga ka shiga gidansu kamar zai yanka naman ka haka yake ji. Sam baya so ya ga an shiga gidan, ba ya ƙaunar kowa ya shiga gidan su daga shi sai Didi."

Nayla ta ce, "wallahi Salma fitsari ne kawai ban yi ba, yau ni naga bala'i ganin idona. Salma duba min wayar nan ki ga ko screen ɗinta ya samu damuwa, dan yadda ta faɗi a hannuna da na ganshi na tabbatar daƙyar bai fashe ba. Wannan halitta ta mutumin nan akwai ban tsoro, ga ido kamar na aljanu." Salma ta karɓi wayar da take miƙa mata dubawa kana ta ce, "Wallahi ya tsage. Wannan bala'i har ina? daga gidan su ya jawo miki asarar sama da naira dubu ɗari biyu. Dan screen ɗin wayar ki in bai yi haka ba ya kusa."

Nayla ta faɗi akan kujera ta dafe kai ta ce, "gabaɗaya ban shigo Kano da ƙafar dama ba, da fari gidan nan babu haske, ga tashin hankalin da na haɗu dashi sannan ga asara." Hajja da take jin ta take kallon ta tayi dariya ta ce, "wai duk tsoron Ummarun ne ya saka ki ka firgice haka?." Salma ya ce, "ba dole ba Hajja, wannan mutumin kallon sa ma tsoro yake bawa mutane balle kuma ya harare ka ko yayi magana. Ni na jima ban ga mutum bai baƙin hali kamar sa ba, sai kyaun fuska kamar shi ya tsara kansa, amma zuciya da hali baƙaƙe."

Hajja ta ce, "ai kam yana da kirki sosai, kaf unguwar nan ni kaɗai ce nake kiransa da Ummaru ya amsa har yayi min magana. Duk da nima ɗin kafin ya amsa sai ya ce bana son sunan amma sai na faɗa, kuma zai gaishe ni wani lokacin da fara'a sannan ya tafi. Kawai shi baya so a raɓi yayarsa ne saboda mutanen unguwar nan suna yi musu wata fassara mara daɗin ji. Shiyasa sa baya son kowa ya shiga gidan su dan baya ƙaunar munafurci da gulma."

Nayla ta ce, "to mu ina ruwan mu da wata fasaara da ake musu Hajja? Shima ya san in ba dan Didi ɗin ba waye zai shiga gidan nan? To Didi tana da kirki sosai, tun ɗazu naso fitowa amma ta hana ni ta ce sai yanzu zan fito, shima ƙaryar zan kira Abiy ne ma ya saka ta ƙyale ni. Har tana cewa na dawo da daddare, to in ba aljanna ake bayarwa ba me zai kai ni gidan nan na ta?."

Salma ta ce, "bashi da mutunci bai san mutunci ba, ai ko dan yayarsa ya kamata ya dinga ɗagawa mutane ƙafa. Ni fa shiyasa wallahi bana ma shiga gidan dan bana so na haɗu dashi kwata-kwata, In ta shigo gidan nan ta dinga yi min mitar bana shiga inda take, kin san ni babu ɓoye-ɓoye kai tsaye na ce mata Omar yana gidan bazan iya shiga ba.." Nayla ta ce, "ina yaga kirki? shi ai abin alfaharinsa ne ma a shiga gidan su. Nima ba dan chaji ba da sai dai ta shigo ta ganni, duk abinda zata ce bazan je ba."

Hajja tayi dariya ta ce, "ke dai kawai ya firgita ki ne Hauwa'u."
"Wallahi sosai Hajja, haka na saka Didi a gaba ina kuka tana rarrashi." Hajja tayi dariya sosai ta ce, "ke fa babu abinda zaki cewa Omar wallahi, ya taimake ki a lokacin da ake gab da tuntsurar miki da budurcinki. Ba dan shi ba da yanzu ana zancen an yi miki fyaÉ—e shekarun baya."

"Hmmm!" Shine abinda Nayla tace kawai tana sauke numfashi. Salma ta ce, "Kai Hajja! daman wai shine ya taimake ta?." Hajja ta ce, "Ke duk labarin da ake yi baki sani ba?."
"Ban taɓa tsayawa na fahimta ba ai."
"Shine wallahi. Haka ya ɗauko ta kamar jaririya saboda a tsorace take sosai sai kuka take yi daman ita sarkin shagwaɓa. Gashi babu riga a jikinta sun yaga rigar atamfar da take jikinta, hakan ya saka shi ya cire rigarsa ta sama ya saka mata sannan ya dawo da ita."

"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Don Allah Hajja ki daina faɗar haka bana so wallahi" Nayla ta faɗa da ƙarfi tana runtse ido. Salma ta sake cewa, "Hajja wai kina nufin rigarsa ya sakawa Nayla?." Hajja ta ce, "ƙwarai kuwa."
"Tab! amma ya cuce ta wallahi."
"Meye na cuta shi da ya yi taimako? Kuma magana ake ta shekaru takwas ko tara baya."
"To Hajja shekara tara baya a ƙalla tana da shekara sha uku ko sha huɗu."

Hajja ta kalli Nayla da har lokacin idon ta yake a kulle ta ce, "Kuma da yake tana da girman jiki ƙirjinta a cike yake shiyasa ma suka so lalata ta." Nayla tashi tayi ta bar falon cikin takaici da baƙin cikin wannan labari, ta tsani ta ji ana bada labarin nan ko kusa.

Salma ta ce, "Gaskiya Hajja ki daina bada labarin nan, hakan yana nufin fa ya gama ganin halittarta tun shekarun baya. Yanzu kallon raini yake mata shiyasa ma yake tsoratata."

Hajja ta ce, "to sai me? Da ya gani ɗin wani abun yayi mata? Da ya barta a wajan su da ba lalata ta zasu yi ba?. Ni tun daga lokacin nake ƙaunarsa saboda abinda ya yi mata, daga ranar ya fara riƙe amfani da makami dan a kanta ya fara zubar da jini, akan taimakon ta ya fara saka makami a jikin mutum. Haka yazo gidan nan yana faɗa kamar ƙanwar sa aka ao cutarwa. Ni yayi min, kuma har gobe ina kallon sa da wannan ƙimar."

Salma tayi shiru bata ce komai ba Hajja ma tayi shiru dan da alama tana taya ƴar uwarta kishi dan ance ya ɗauko ta babu riga. Ita kuma bata ga abin fushi ba, taimako ne kuma ya wuce wataƙila ma shi ya manta.

Omar kuwa bayan Nayla ta fita shima fita ya yi bai dawo ba sai bayan an yi sallar magriba as usually shi da mutanen sa. A falon ta suka baje suka ci abinci kamar yadda ya saba ciyar da su kafin ya sake fita. Bai dawo ba sai tara na dare ya same ta a zaune da waya a hannunta tana dannnawa.

Kallon sa tayi bayan ya shigo ta ce, "baka faÉ—a min me ya faru a Abujaa É—in ba." Zama yayi ya kalle ta ya ce, "wani É—an aiki zan yi zuwa wani satin."
Chapter 11 · 0% Book details