Sashe 18
Kiran Rabo Book1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Omar takaici kamar ya kashe shi haka yake ji, cikin tsananin ɓacin rai da takaici da tsawa ya ce, "in na sake ganin yarinyar nan a gidan nan bazan ƙyaleta ba." Cikin ɓacin rai da fusata Didi ta ce, "Sai ta shigo! Omar sai ta shigo in ka dama ka kasheta ka kaima ka ga in za a barka da rai. Na gaji da wannan shirmen na ka, kullum kana girma amma kana cin ƙasa, sam baka aiki da hankali balle ka san abinda zaka yi."
Runtse idanu yayi yana jin zafin kalamanta, Babban abin haushin ma a gaban yarinyar da ta taɓa yi masa faɗa kwanaki a gabanta, yau ma gashi an maimaita har tana cewa yana shirme baya aiki da hankali. To shi wanne gangancin ne ma zai bari ya bar yarinyar da lafiyarta? ai in bai taɓa lafiyar jikinta ba bazai ji daɗi ba. Bai taɓa jin haushin wata halitta kamar ita ba, saboda itace mace ta farko da aka yi masa faɗa a gabanta.
Zai sake magan ta dakatar dashi cikin fushi ta ce, "Dallah Malam fita ka bani waje kafin na tsinke ka da mari." Sak ya yi yana kallon ta jin wai zata mare shi, kallon ta yake yi cikin mamaki dan abinda ta faɗa bata taɓa furtawa shi ba sai a lokacin. Ganin kallon mamakin da yake mata sai ta ce, "ko kana ganin ban isa na mare ka ɗin ba ne? In kana ganin ban isa ba ka cigaba da tsaya min kai wallahi sai na mare ka."
Kai yake gigirzawa yana kallon Nayla da take kwance a jikin Didi tana sauke numfashi ya ce, "na gama haddace fuskarta, duk abinda ya faru tayi kuka da kanta" yana faɗar hakan ya fita daga gidan cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya. Wai kamar shi Omar Tiger Didi take cewa zata mara a gaban wata yarinya, ƙarshe ma akan yarinyar take zancen zata ta dake shi.
     Didi ta kalli Nayla bayan ya fita ta ce, "Nayla yi haƙuri don Allah ki nutsu, ki dawo nutsuwarki ji." Tashi tayi da sauri ta ɗauko mata ruwa mai sanyi ta bata, ai kam Nayla ta sha ruwan nan sosai dan tana buƙatarsa. Hijjabin jikinta ta cire mata ta riƙeta ta ce, "taso mu shiga ciki." Daƙyar Didi ta iya ɗaga ta suka shiga falon Didi ta zaunar da ita akan kujera ta kunna mata fanka sannan ta zauna kusa da ita tana yi mata firfita.
Bata sake magana ba sai da taga Nayla ta ɗan nutsu hawayen da take yi ma ya tsaya sannan ta sake kawo mata ruwa ta ce, "karɓi ki sha Nayla." Nayla kallon ta tayi sai ta ɗan zabura Didi ta riƙe ta ta ce, "kar ki ji tsoro, babu abinda zai miki baya cikin gidan ma gabaɗaya. Yi haƙurk ki sha ruwa." Ba musu ya sake karɓat ruwa ta sha tana sauke numfashi kamar wacce tayi gudu.
Didi ta kalle ta ganin ta dawo nutsuwarta sai ta dafata ta ce, "ki yi haƙuri Nayla, ban saka ki shigowa gidan nan dan ki shiga wannan yanayin ba, wallahi ban san zai dawo ba da ban ce ki zo ba. Ki yi haƙuri don girman Allah, da na san hakan zai faru da ban ce ki zo ba."
Nayla jin yadda take mata magiya cikin sanyim murya sai ta ce, "Haba Didi, don Allah ki daina yi min magiya haka babu komai Didi."
"Dole na roƙeki ki yafe min ai Nayla, da ban je har gida na taho dake ba da haka bai faru ba, tun farko kin nuna bakya so amma na takura miki. Gashi na saka ki a halin tsoro da fargaba wanda ya kusa sakawa ki suma ki fita daga hankalinki, ki yafe min kin ji? bazan sake takura miki akan zuwa gidan nan ba."
Nayla ta ce, "babu komai Didi, don Allah ki daina bani haƙuri." Didi ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "ransa ne a ɓace sosai kin tarar dashi akan gaɓa shiyasa, zaki ga ni kaina bai ƙyale ni ba saboda in ransa ya ɓaci ya kan rasa hankalinsa na wani lokaci sai daga baya yake fahimtar abinda ya faru. Bayan fitar ki baƙon da ya zo shine silar ɓacin ransa, na tabbatar ba dan haka ba da bazai kalle ki ba, saboda nayi masa magana ranar da ya yi miki wannan abun."
Nayla ta riƙe hannun Didi ta ce, "babu komai Didi ya wuce." Ta yi murmushi ta ce, "na gode. Amma ki rage tsoronsa har haka, ki koyi dakewa koda zaku haɗu a wani waje" tayi murmushi ta ce, "Dan na san baza ki sake shigowa gidan nan ba, Nayla ban ga laifinki ba Omar abin tsoro ne a wajan wanda bai san shi ba, amma in ka san shi normal mutum ne kamar kowa" ta faɗa tana ƴar dariya tana kallon Nayla da take yaƙe.
Didi ta ce, "ina jin aure zan masa wataƙila zafin kansa ya ragu." Nayla bata san san da murmushi ya subce mata ba, ta wara ido ta ce, "Aure! Kuma sai a samu wacce zata aure shi? Taɓɗi! amma sai dai mai taɓin hankali." Sai bayan tayi magana ta fahimci a bayyane tayi maganar. Didi tayi dariya sosai ganin ta saka Nayla murmushi ta ce, "Ni da nake cewa ƴar gida za a yi dake? Shikenan tuwo na mai na, Yayar amarya kuma Yayar ango."
Wani irin numfashi Nayla ta sauke mai nuni da ta rasa abinda zata ce. Didi tayi dariya ta ce, "wato kin kasa magana ma kenan?." Nayla tayi murmushi kawai bata ce komai ba. Didi ta ce, "mu je na raka ki wajan Hajja in na soya awara sai na kawo miki." Ai kamar jira Nayla take ta miƙe tana neman hijjabinta.
Didi ta bita da kallo dan ƙananun kaya ne a jikinta ta ɗora dogon hijjabi ta fito ta ce, "Irin wannan kyau haka Nayla? gaskiya ina yiwa ƙanina kamu." Taɓe fuska Nayla tayi ta kalle ta tace, "Didi wallahi kina saka zuciyata cikin fargaba, don Allah ki daina faɗar haka bana so." Didi tayi dariya tana cewa, "na daina faɗa, yi haƙuri." Nayla ta saka hijjabin ta, itama Didi ta saka suka fito.
Ganin tana dafe kai ya saka Didi ta ce, "ciwon kai ko?." Ta ɗaga mata kai alamun eh, Didi ta ce, "sannu, Allah ya ye." Ta amsa da amin suka fita ƙofar gidan. Nayla ganin Didi bata rufe gidan ba sai ta ce, "baki kulle ƙofar ba." Didi tayi murmushi ta ce, "a tunanin ki za a shiga ayi mana sata ne? Gidan su Omar Damisa ne fa, gidan nan ko almajiri baya shiga yayi bara balle ɓarayi." Nayla ta ce, "Ya ci suna Tiger ɗin ai, ba shi da sabo." Didi ta yi murmushi Nayla ta girgiza kai bata kuma cewa komai ba amma zuciyar ta tana jinjina girman baƙin halin sa.
      A zaune suka samu su Hajja ita da Salma suna cin abinci. Didi ta ce, "Hajja ga Nayla na dawo da ita na kuma yi mata laifi, a taya ni roƙon ta tayi haƙuri." Hajja ta ce, "me ya faru ke da ƙanwarki?." Didi ta ce, "ita da Omar suka gamu wallahi, gamuwar bata yi daɗi ba sam kuma duk ni ce sila. Ni nazo har goda muka tafi, da ban mata dole ba da baza ta je ba, yanzu haka kanta ciwo yake yi."
Salma ta yi dariya ta ce, "Shiyasa ni da gidanki sai kallo daga nesa." Didi ta zaunar da Nayla ta ce, "ki yi haƙuri Nayla." Nayla ta ce, "Haba Didi, tun a can ki ke bani haƙuri, don Allah ki bari."
"Na bari, Na gode sosai Allah ya baki miji na gari. Zan koma gida yanzu amma zan shigo anjima." Nayla ta ce, "to Didi." Didi ta fita zuciyar taduk babu daɗi akan abinda Omar ya yi mata.
Ai Didi tana fita Nayla ta zare hijjabinta ta cillar ta ɗaga wuya sama ta kalli Salma ta ce, "Salma duba wuya na ki ga babu yanka da wuƙa." Salma ta kalli wuyan ta ce, "babu komai, Meye ya faru?." Nayla ta ce, "wannan mutumin an yi ɗan tijara kuma ɗan bala'i. Ina shiga ban ma kula dashi ba fa, ina ganinsa sai nayi ta'awizi ashe yaji haushi, wai korar shaiɗan nayi masa, to meye marabarsa da shaiɗan ɗin?."
Salma ta ce, "shine ya shaƙe ki?."
"Ke faɗar tashin hankalin da na shiga ai ɓata baki ne, ba na jin ma abinda yake cewa saboda tsoro da fargaba. Kawai naga ya ɗora min wuƙa a wuya daga nan ƙwaƙwalwata taje hutun rabin lokaci, dan numfashi na kaɗan ya rage bai ɗauke ba."
Salma ta ce, "to shi wai bashi da hankali ne ko ne? Faɗa masa aka yi in yayi miki wani abun ƙyale shi za a yi?." Nayla ta ce, "shima ya san wasa yake yi ai, babban abin mamakin ma wallahi har ita Didin bai bari ba, kin ji yadda yake zazzaga bala'i kamar ba ita yayarsa ba?. Sai magana yake akan shi bashi da dangi da sauran su."
Salma ta ce, "wannn mutum dai ya zama annoba a unguwar nan, almajiri fa baya shiga gidan saboda tsoro." Nayla ta ce, "haka Didi take faÉ—a min yanzu, ke ni naga bala'i ai. Ruwa kuwa ina jin na sha yafi leda uku." Hajja da take jin ta tayi dariya ta ce, "kin cika tsoro ne kawai Hauwa'u."
"Hajja tsoro halak ne, dan naji tsoronsa ai ban yi laifi ba, da tuni an kawo miki ni ya yanka min wuya."
"Haba dai, shima ai bazai fara ba, tsorataki yake yi kawai."
Salma ta ce, "amma abin yayi yawa wuƙa fa? Wai bashi da dangi ne?." Hajja ta ce, "kin taɓa ganin wanda bashi da dangi?." Salma ta ce, "to suna ina? Ai ko dan wannan jagaliyancin da yake yi ya ci ace na gaba dashi sun tsawatar masa." Hajja ta yi murmushi ta ce, "wai ba gidan babar ku Sa'adatu zaku je ba?." Nayla ta miƙe ta ce, "bara na canja kaya mu tafi" ta faɗa tana shiga ciki dan ta canja kaya su tafi.
Runtse idanu yayi yana jin zafin kalamanta, Babban abin haushin ma a gaban yarinyar da ta taɓa yi masa faɗa kwanaki a gabanta, yau ma gashi an maimaita har tana cewa yana shirme baya aiki da hankali. To shi wanne gangancin ne ma zai bari ya bar yarinyar da lafiyarta? ai in bai taɓa lafiyar jikinta ba bazai ji daɗi ba. Bai taɓa jin haushin wata halitta kamar ita ba, saboda itace mace ta farko da aka yi masa faɗa a gabanta.
Zai sake magan ta dakatar dashi cikin fushi ta ce, "Dallah Malam fita ka bani waje kafin na tsinke ka da mari." Sak ya yi yana kallon ta jin wai zata mare shi, kallon ta yake yi cikin mamaki dan abinda ta faɗa bata taɓa furtawa shi ba sai a lokacin. Ganin kallon mamakin da yake mata sai ta ce, "ko kana ganin ban isa na mare ka ɗin ba ne? In kana ganin ban isa ba ka cigaba da tsaya min kai wallahi sai na mare ka."
Kai yake gigirzawa yana kallon Nayla da take kwance a jikin Didi tana sauke numfashi ya ce, "na gama haddace fuskarta, duk abinda ya faru tayi kuka da kanta" yana faɗar hakan ya fita daga gidan cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya. Wai kamar shi Omar Tiger Didi take cewa zata mara a gaban wata yarinya, ƙarshe ma akan yarinyar take zancen zata ta dake shi.
     Didi ta kalli Nayla bayan ya fita ta ce, "Nayla yi haƙuri don Allah ki nutsu, ki dawo nutsuwarki ji." Tashi tayi da sauri ta ɗauko mata ruwa mai sanyi ta bata, ai kam Nayla ta sha ruwan nan sosai dan tana buƙatarsa. Hijjabin jikinta ta cire mata ta riƙeta ta ce, "taso mu shiga ciki." Daƙyar Didi ta iya ɗaga ta suka shiga falon Didi ta zaunar da ita akan kujera ta kunna mata fanka sannan ta zauna kusa da ita tana yi mata firfita.
Bata sake magana ba sai da taga Nayla ta ɗan nutsu hawayen da take yi ma ya tsaya sannan ta sake kawo mata ruwa ta ce, "karɓi ki sha Nayla." Nayla kallon ta tayi sai ta ɗan zabura Didi ta riƙe ta ta ce, "kar ki ji tsoro, babu abinda zai miki baya cikin gidan ma gabaɗaya. Yi haƙurk ki sha ruwa." Ba musu ya sake karɓat ruwa ta sha tana sauke numfashi kamar wacce tayi gudu.
Didi ta kalle ta ganin ta dawo nutsuwarta sai ta dafata ta ce, "ki yi haƙuri Nayla, ban saka ki shigowa gidan nan dan ki shiga wannan yanayin ba, wallahi ban san zai dawo ba da ban ce ki zo ba. Ki yi haƙuri don girman Allah, da na san hakan zai faru da ban ce ki zo ba."
Nayla jin yadda take mata magiya cikin sanyim murya sai ta ce, "Haba Didi, don Allah ki daina yi min magiya haka babu komai Didi."
"Dole na roƙeki ki yafe min ai Nayla, da ban je har gida na taho dake ba da haka bai faru ba, tun farko kin nuna bakya so amma na takura miki. Gashi na saka ki a halin tsoro da fargaba wanda ya kusa sakawa ki suma ki fita daga hankalinki, ki yafe min kin ji? bazan sake takura miki akan zuwa gidan nan ba."
Nayla ta ce, "babu komai Didi, don Allah ki daina bani haƙuri." Didi ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "ransa ne a ɓace sosai kin tarar dashi akan gaɓa shiyasa, zaki ga ni kaina bai ƙyale ni ba saboda in ransa ya ɓaci ya kan rasa hankalinsa na wani lokaci sai daga baya yake fahimtar abinda ya faru. Bayan fitar ki baƙon da ya zo shine silar ɓacin ransa, na tabbatar ba dan haka ba da bazai kalle ki ba, saboda nayi masa magana ranar da ya yi miki wannan abun."
Nayla ta riƙe hannun Didi ta ce, "babu komai Didi ya wuce." Ta yi murmushi ta ce, "na gode. Amma ki rage tsoronsa har haka, ki koyi dakewa koda zaku haɗu a wani waje" tayi murmushi ta ce, "Dan na san baza ki sake shigowa gidan nan ba, Nayla ban ga laifinki ba Omar abin tsoro ne a wajan wanda bai san shi ba, amma in ka san shi normal mutum ne kamar kowa" ta faɗa tana ƴar dariya tana kallon Nayla da take yaƙe.
Didi ta ce, "ina jin aure zan masa wataƙila zafin kansa ya ragu." Nayla bata san san da murmushi ya subce mata ba, ta wara ido ta ce, "Aure! Kuma sai a samu wacce zata aure shi? Taɓɗi! amma sai dai mai taɓin hankali." Sai bayan tayi magana ta fahimci a bayyane tayi maganar. Didi tayi dariya sosai ganin ta saka Nayla murmushi ta ce, "Ni da nake cewa ƴar gida za a yi dake? Shikenan tuwo na mai na, Yayar amarya kuma Yayar ango."
Wani irin numfashi Nayla ta sauke mai nuni da ta rasa abinda zata ce. Didi tayi dariya ta ce, "wato kin kasa magana ma kenan?." Nayla tayi murmushi kawai bata ce komai ba. Didi ta ce, "mu je na raka ki wajan Hajja in na soya awara sai na kawo miki." Ai kamar jira Nayla take ta miƙe tana neman hijjabinta.
Didi ta bita da kallo dan ƙananun kaya ne a jikinta ta ɗora dogon hijjabi ta fito ta ce, "Irin wannan kyau haka Nayla? gaskiya ina yiwa ƙanina kamu." Taɓe fuska Nayla tayi ta kalle ta tace, "Didi wallahi kina saka zuciyata cikin fargaba, don Allah ki daina faɗar haka bana so." Didi tayi dariya tana cewa, "na daina faɗa, yi haƙuri." Nayla ta saka hijjabin ta, itama Didi ta saka suka fito.
Ganin tana dafe kai ya saka Didi ta ce, "ciwon kai ko?." Ta ɗaga mata kai alamun eh, Didi ta ce, "sannu, Allah ya ye." Ta amsa da amin suka fita ƙofar gidan. Nayla ganin Didi bata rufe gidan ba sai ta ce, "baki kulle ƙofar ba." Didi tayi murmushi ta ce, "a tunanin ki za a shiga ayi mana sata ne? Gidan su Omar Damisa ne fa, gidan nan ko almajiri baya shiga yayi bara balle ɓarayi." Nayla ta ce, "Ya ci suna Tiger ɗin ai, ba shi da sabo." Didi ta yi murmushi Nayla ta girgiza kai bata kuma cewa komai ba amma zuciyar ta tana jinjina girman baƙin halin sa.
      A zaune suka samu su Hajja ita da Salma suna cin abinci. Didi ta ce, "Hajja ga Nayla na dawo da ita na kuma yi mata laifi, a taya ni roƙon ta tayi haƙuri." Hajja ta ce, "me ya faru ke da ƙanwarki?." Didi ta ce, "ita da Omar suka gamu wallahi, gamuwar bata yi daɗi ba sam kuma duk ni ce sila. Ni nazo har goda muka tafi, da ban mata dole ba da baza ta je ba, yanzu haka kanta ciwo yake yi."
Salma ta yi dariya ta ce, "Shiyasa ni da gidanki sai kallo daga nesa." Didi ta zaunar da Nayla ta ce, "ki yi haƙuri Nayla." Nayla ta ce, "Haba Didi, tun a can ki ke bani haƙuri, don Allah ki bari."
"Na bari, Na gode sosai Allah ya baki miji na gari. Zan koma gida yanzu amma zan shigo anjima." Nayla ta ce, "to Didi." Didi ta fita zuciyar taduk babu daɗi akan abinda Omar ya yi mata.
Ai Didi tana fita Nayla ta zare hijjabinta ta cillar ta ɗaga wuya sama ta kalli Salma ta ce, "Salma duba wuya na ki ga babu yanka da wuƙa." Salma ta kalli wuyan ta ce, "babu komai, Meye ya faru?." Nayla ta ce, "wannan mutumin an yi ɗan tijara kuma ɗan bala'i. Ina shiga ban ma kula dashi ba fa, ina ganinsa sai nayi ta'awizi ashe yaji haushi, wai korar shaiɗan nayi masa, to meye marabarsa da shaiɗan ɗin?."
Salma ta ce, "shine ya shaƙe ki?."
"Ke faɗar tashin hankalin da na shiga ai ɓata baki ne, ba na jin ma abinda yake cewa saboda tsoro da fargaba. Kawai naga ya ɗora min wuƙa a wuya daga nan ƙwaƙwalwata taje hutun rabin lokaci, dan numfashi na kaɗan ya rage bai ɗauke ba."
Salma ta ce, "to shi wai bashi da hankali ne ko ne? Faɗa masa aka yi in yayi miki wani abun ƙyale shi za a yi?." Nayla ta ce, "shima ya san wasa yake yi ai, babban abin mamakin ma wallahi har ita Didin bai bari ba, kin ji yadda yake zazzaga bala'i kamar ba ita yayarsa ba?. Sai magana yake akan shi bashi da dangi da sauran su."
Salma ta ce, "wannn mutum dai ya zama annoba a unguwar nan, almajiri fa baya shiga gidan saboda tsoro." Nayla ta ce, "haka Didi take faÉ—a min yanzu, ke ni naga bala'i ai. Ruwa kuwa ina jin na sha yafi leda uku." Hajja da take jin ta tayi dariya ta ce, "kin cika tsoro ne kawai Hauwa'u."
"Hajja tsoro halak ne, dan naji tsoronsa ai ban yi laifi ba, da tuni an kawo miki ni ya yanka min wuya."
"Haba dai, shima ai bazai fara ba, tsorataki yake yi kawai."
Salma ta ce, "amma abin yayi yawa wuƙa fa? Wai bashi da dangi ne?." Hajja ta ce, "kin taɓa ganin wanda bashi da dangi?." Salma ta ce, "to suna ina? Ai ko dan wannan jagaliyancin da yake yi ya ci ace na gaba dashi sun tsawatar masa." Hajja ta yi murmushi ta ce, "wai ba gidan babar ku Sa'adatu zaku je ba?." Nayla ta miƙe ta ce, "bara na canja kaya mu tafi" ta faɗa tana shiga ciki dan ta canja kaya su tafi.