Sashe 8
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
A sanqare a tsaye Bakura ya bar Samira ta na tunani hade da fargaba da karanto addu'o'i a zuci. Addu'ar Allah Ya yayyafawa zuciyarsa ruwan sanyi koma me aka yi masa a waje.
Shigarsa dakinsa ba dadewa ya fito jikinsa da ruwa da alama dai alwala ya dauro.
Ta yi sauri ta saki fuskarta ta dube shi ta yi murmushi ta ce "alwala kayi, za ka je masallaci?"
Ya amsa a ciki-ciki "eh:" Har ya kai qofar fita ya juyo ya dubeta ya ce "ina Yagana?"
Ta amsa cikin jin dadin maganar da ta samu ya yi mata.
Ta ce "ta na daki ta na karatu, saboda sun kusa fara jarabawa."
Ya sake cewa "ina Abubakar, Umar da Usman? Ta ce "su na nan a masallacin qofar gida tunda yamma, Malam Hashim ya zo su na daukar karatu."
Ya juya ya fice ba tare daya ce komai ba.
Mamaki ya sake lullu6e zuciyar Samira ta kasa gane halin da yake ciki yau, kamar ya na farin ciki kamar ya na baqin ciki. Ta shiga dakinta ta yi alwala ta yi sallar magrib. Tayi ta lazumi tana addu'a kamar yadda ta saba kullum akan Allah ya sassauta zuciyar
Bakura, ya so ta d'ari bisa d'ari kamar yadda take son sa, ya dinga sakar mata fuska, ya rage wannan muzuran da kwarjinin da ya ke yi mata don haka kawai ta ji ta na tsoransa. Kada Allah ya hada shi da wacce zai ji ya na so a rayuwarsa balle ya yi mata kishiya, duk da ta san tsautsauran ra'ayinsa ba shi da niyyar yin mata biyu a rayuwarsa. Mata basu cika burge shi ba amma ta san lallai idan ya hadu da yarinya mai tarbiyya wacce take da ladabi da biyayya za ta iya burge shi ya aure ta, ita kuma tsantsar sonsa ne ya dasa mata tsananin kishinsa. Addu'ar Samira kenan, dan duk wanda ya santa ya san ta ya san ra'ayinta.
Aka kira sallar sha'i a masallacin qofar gida, su Bakura suka bi jam'i aka tayar da sallah. Samira ma daga dakinta ta aiwatar da ta ta sallar, bayan ta idar ta yi shafa'i da wutiri da laziminta sannan ta miqe ta qarasa wajen kayan kwalliya ta sake caba ado. Aka sake saka huda, jagira, jan baki, ta sake yin daurin dankwali ta feshe jiki da turararruka designers sannan ta fito.
Ta na fitowa ta nufi dakin Zahra, ta iske Zahra ma ta idar da sallah. Cikin ladabi Zahra ta dubi mahaifiyarta tayi murmushi,
Ta ce "Mama sannu da gida. Kin yi kyau."
Samira tayi murmushi ta ce "Zahra sannu da karatu, ki fito mu ci abinci, Abbanki ya dawo ki yi masa sannu da zuwa don ya tambayeki kafin ya tafi masallaci."
Zahra ta amsa da "to Mama."
Su ka d'unguma suka fito, Zahra sanye doguwar riga baqa (abaya) kanta a lullu6e da qaramin hijab baki mai hula iyaka Rirji. A babban falon gidan suka ci karo da Bakura tare da yaransa Abubakar, Umar da Usman sun dawo daga masallaci.
Samira ta ce "yauwa sai mu wuce kan dining table mu ci abinci ko Abban Zahra? Yau da kaina na shiga kicin na dafa maka burabusko irin na ku na barebari."
Ta ga ya yi turus bai juya ya kalli dining table din ba ma balle ya bude ya ga abinda aka dafa masa balle ya burge shi.
Zahra ta ce "Abba sannu da zuwa, shugabar makarantarmu ta ce in gaisheka."
Sai su ka ga ya tsuke fuska ya kada kai zai nufi dakinsa, har ya kai qofar fita sai ya juyo ya dubi Zahra.
Ya ce " Zahra ki kula da rayuwa, ki tabbatar kin saka tsoran Allah a cikin zuciyarki a duk inda kike. Ba ruwanki da lalatattun qawaye da samari bata gari. Na sakale Kwaryata ta gari a ragaya ba na fatan kwaryar nan ta tsinke ta fado daga ragaya ta dinga garari a tsakar gida."
Yajuya ya tafi abinsa ya tafi.
Cafdijam!!! Wannan Hausa ta yiwa Uwar Zahra tsauri balle ita Zahrar kanta. Daman idan aka dunkule Hausa, ko karin magana Zahra ba ta ganewa, ta fi gane yaren kanuri sai kuma turanci. Tabbas tana jin Hausa amma ta ina za ta fahimci wannan maganar ta da?
Samira bahaushiya ce gaba da baya amma ya aka yi wannan Babarbaren ya yi ma ta Hausa cikin Hausa ba ta fahimce shi ba? Dadin dadawa ba su san kan maganar da ya ke yi ba balle su gano bakin maganar.
Hanakalin Zahra ya tashi, ta kalli mahaifiyarta ta dafe kirji. Ta ce "Mama me na yiwa Abba, wacce kwarya ya ke magana?"
Samira ta fita da sauri ta bi shi dakinsa, ta iske zai shiga wanka, ta dube shi.
Ta ce "Sweety Zahra ta damu ta na tambayar ko wanni laifi ta yi maka."
Ya girgiza kai ya ce "ba laifin komai ta yi min ba dama ba lallai ne ku gane abinda na ke nufi ba yanzu sai a nan gaba."
Ya juya zai shiga bandaki Samira ta qara dakatar da shi. Ta ce "sai kayi wanka za ka fito mu ci abinci ko na kawo maka na ka kan daning table din nan dakinka?"
Ya girgiza kai ya ce "ba zan ci ba na qoshi."
Hankalin Samira ya tashi ta fara magana kamar mai shirin fashewa da kukan kissa da nuna damuwa.
Ta ce "haba Yayana, maigidana, abin qaunata. Ya zan dage in yi maka abincin daka fi so a rayuwarka wato burabuskon gero, kuma ka ce ba za ka ci ba. Mu yaya za' ayi mu iya ci...?"
Kafin ta rufe bakinta ya dakatar da ita ya ce "ki je ke da yaranki ku ci, ni na qoshi. zan yi wanka in kwanta idan kin shigo kada ki kunna min fitila, jada ki tashe ni ba zanyi hira ba yau. Ka da ki kuskure abinda na fada miki wannan doka ce."
Samira ta juya sadan-sadan ta fice daga dakin ba tare da ta sake cewa komai ba kuma bata san me hakan yake nufi ba.
Sai ta ji ya yi magana ya ce "ka da ku damu ke da yaranki babu wanda ya yi min wani laifi a cikinku."
Ta juyo da murna ta dube shi ta ce "kawai yanayi ne ya canja?"
Ya ce "yanayi ne kawai, yau na ga mai kama da Zuhuriyya sak kamar an tsaga kara shine hankalina ya tashi."
"Mai kama da Zuhuriyya fa ka ce? A ina? Bakura ka san abinda kake fada kuwa?" Samira ta tambaya cike da mamaki.
Ya daga mata hannu ya dakatar da ita. Ya ce " tambayoyin sun isa haka. Sai da safe."
Samira ta fito zuciyarta cike da mamaki da kokonton anya kuwa Bakura ba shi da wata aljana a jikinsa? Ko dai aljanun ne su ka tashi yau?"
Samira mace ce dirarriya mai tsawo da 'yar qiba. Fara ce sosai, sai dai ba ta da dogon hanci , bakinta madaidaici ta na da dara-daran idanuwa farare qal ma su kyau. Ba ta da gashi mai tsawo amma kuma ba gwaguyyaye ba ne. Mace ce mai tsafta gami da taushin murya, mai tsananin haquri domin idan ba ita ba ba mai iya zama da Bakura. Ta iya lallashi ta iya tausar ran mijinta, ta na da tausayi da kyautatawa masu aikinta. Ta na da son wasa da dariya da yaranta har da ma sauran jama'a. Ta na da ilimin addini daidai gwargwado da na boko duk da iyakacinta daga sakandire ta tsaya ba ta ci gaba ba haka kuma bayan ta auri Bakura bai bar ta ta ci gaba ba.
Samira ta fito ne daga babban gida ma'ana gidan arziki da mutunci. Mahaifin Samira mutumin Kano a unguwar yakasai yake. Ta na da qanne da yayye ba adadi kasanceyar mahaifinta mata hudu gare shi. Dukkansu su na nan da ransu reras. Amaryar gidan ma har yanzu ta na haihuwa.
Ta auri Bakura saboda ta na sonsa Zahra ce babbar 'yarsu ta fari kasancewar sunan mahaifiyarsa ne yake kiranta da Yagana. Zahra tayi matukar yin kama da Babanta ko ba'a fada maka ba idan ka kalli Bakura ka kalli Zahra ka san irin su daya.Banbancin shi namiji ita kuma mace. Da wuya ka kira shi Babanta sai dai ka dauka Yayanta ne kasancewar auren wuri yayi da haihuwar quruciya. Zahra tafi mahaifinta haske kasancewar ta dauko hasken fatar mahaifiyarta amma ba dukka ta dauko farin ba ta hada da baqar fatar mahaifinta sai ta bada kala mai kyau wato hasken duhu (chocolate colour).
Wannan kalar ta Zahra ta sake fitar mata da kyawunta, dogon hancinta siriri har baka irin na barebarin asali, bakinta dan qarami har ya fi na mahaifinta kyau, haka fararen haqoransu da wushiryar sama da qasa duk iri daya. Ga wani Iallausan gashi har qasan qeyarta bakikiirin mai tsawo. Jikinta abin sha' awa, doguwa ce siririya. Kirar kamar Bakura ba su da kiba.
Mazan kuwa Abubakar, Umar da Usman ga farin har gajeran hancin sak irin na mahaifiyarsu sak, daba dayan su sun yi kama da mahaifiyarsu, amma sun dauko tsayin mahaifinsu dogaye ne sosai. Allahu Akbar!! Allah mai halittar bayinSa duk yadda Ya so.
Kwana biyu Bakura ya kasance cikin yawan tunani da damuwa ga uwa uba rikirkicewar tunani. Ya na cikin damuwa, gigita da tsantsar son binciko wai shin menene alaqar Sajida da Zuhuriyyarsa, idan akwai.
Bakura ya taso daga wajen aiki, sai ya ji a ransa ba zai qara iya daurawa ba bari kawai ya zarce gidan su Sajida ko Allah zai sa ya samu abinda ya ke nema, ma' ana labarin asalin su Sajida. Bakura ya na tsayawa da motarsa a bakin qofar gidan su Sajida sai ya bude qofar ya fito yayin da gardawan da ke zazzaune a qofar gidan su ka zuba masa idanuwa su na kallonsa su na gasgata ni' imar da Rabbul samawati ya yi masa. Ya yi shigar fararen kaya, farin takalmi da farar hula, motarsa kuma kirar BMW 7 SERIES mai launin ruwan zuma. Ya fito ya tsaya yayin daya zare farin gilashin dake fuskarsa ya dubi jama'ar da ke zazzaune a qofar gidan daga dukkan alamu makarantar allo ce karatu su ke dauka.
Malam Yakubu shine mai makarantar wato mahaifin Sajida. Ya na zaune akan kujerar katako rike da zabgigiyar dorina, yara su na gabansa su na daukar karatu, da zarar sun kuskure sai ka ji ya faula musu bulalar. Malam kenan!
Bakura ya qarasa gaban Malam Yakubu ya yi sallama sannan ya durqusa ya gaishe shi. Cikin fara'a Malam ya amsa gami da ce wa "yaro ban gane ka ba."
Bakura yayi murmushi ya ce "watakila saboda ba waccan motar ba ce shiyasa ba ka gane ni ba. Ni ne wanda na zo kwanakin baya da yamma game da maganar Sajida da Abdul Abdulmajid."
Sai Malam ya fahimta ya fada cikin sakin fuska "to, to, to na gane ka yaro, to mu je wajen motarka mu tsaya."
Su ka qarasa jikin motar su ka tsaya. Bakura ya sosa gefen kunne yayi dan murmushi ya ce "Malam yaya yara, yaya jama' a?
Malam ya ce "Alhamdulillahi, mun godewa Allah. Yaro ka taimaka mana fa matuqa domin ni a iya sanina Sajida ba ta da waya. Ashe waya ya hada mata take labewa su na yin magana ba tare da mun sani ba. Har takai ta kawo Sajida za ta yi min dubara ta fita ta je su hadu a wani a waje ban sani ba. Saboda yaron nan fa na cire Sajida daga makarantar boko ta na aji biyar na sakandire. Saboda a hanyar makarantar bokon ne ya ke tare ta su dinga zance. Ni dai na fada duk lokacin da ta yarda Abdul majid ya lalata ma ta rayuwa, ma ana ta bari ya yaudare ta, ya san ta 'ya mace ya cuce ta kuma daga lokacin da na aurar da ita na yi bincike aka tabbatar min ba cikekkiyar budurwa ba ce sai na yanka ta."
Bakura ya yi shiru na wani dan lokaci kansa a sunkuye a qasa kamar mai tunani. Can ya dago da kansa ya yi ajiyar zuciya.
Ya ce "Allah ya kyauta." Malam yakubu ya dubi Bakura ya ce "wai daman ka san Sajida da Abdul majid ne ko ka na da labariKai ka fi cancanta 1
Shigarsa dakinsa ba dadewa ya fito jikinsa da ruwa da alama dai alwala ya dauro.
Ta yi sauri ta saki fuskarta ta dube shi ta yi murmushi ta ce "alwala kayi, za ka je masallaci?"
Ya amsa a ciki-ciki "eh:" Har ya kai qofar fita ya juyo ya dubeta ya ce "ina Yagana?"
Ta amsa cikin jin dadin maganar da ta samu ya yi mata.
Ta ce "ta na daki ta na karatu, saboda sun kusa fara jarabawa."
Ya sake cewa "ina Abubakar, Umar da Usman? Ta ce "su na nan a masallacin qofar gida tunda yamma, Malam Hashim ya zo su na daukar karatu."
Ya juya ya fice ba tare daya ce komai ba.
Mamaki ya sake lullu6e zuciyar Samira ta kasa gane halin da yake ciki yau, kamar ya na farin ciki kamar ya na baqin ciki. Ta shiga dakinta ta yi alwala ta yi sallar magrib. Tayi ta lazumi tana addu'a kamar yadda ta saba kullum akan Allah ya sassauta zuciyar
Bakura, ya so ta d'ari bisa d'ari kamar yadda take son sa, ya dinga sakar mata fuska, ya rage wannan muzuran da kwarjinin da ya ke yi mata don haka kawai ta ji ta na tsoransa. Kada Allah ya hada shi da wacce zai ji ya na so a rayuwarsa balle ya yi mata kishiya, duk da ta san tsautsauran ra'ayinsa ba shi da niyyar yin mata biyu a rayuwarsa. Mata basu cika burge shi ba amma ta san lallai idan ya hadu da yarinya mai tarbiyya wacce take da ladabi da biyayya za ta iya burge shi ya aure ta, ita kuma tsantsar sonsa ne ya dasa mata tsananin kishinsa. Addu'ar Samira kenan, dan duk wanda ya santa ya san ta ya san ra'ayinta.
Aka kira sallar sha'i a masallacin qofar gida, su Bakura suka bi jam'i aka tayar da sallah. Samira ma daga dakinta ta aiwatar da ta ta sallar, bayan ta idar ta yi shafa'i da wutiri da laziminta sannan ta miqe ta qarasa wajen kayan kwalliya ta sake caba ado. Aka sake saka huda, jagira, jan baki, ta sake yin daurin dankwali ta feshe jiki da turararruka designers sannan ta fito.
Ta na fitowa ta nufi dakin Zahra, ta iske Zahra ma ta idar da sallah. Cikin ladabi Zahra ta dubi mahaifiyarta tayi murmushi,
Ta ce "Mama sannu da gida. Kin yi kyau."
Samira tayi murmushi ta ce "Zahra sannu da karatu, ki fito mu ci abinci, Abbanki ya dawo ki yi masa sannu da zuwa don ya tambayeki kafin ya tafi masallaci."
Zahra ta amsa da "to Mama."
Su ka d'unguma suka fito, Zahra sanye doguwar riga baqa (abaya) kanta a lullu6e da qaramin hijab baki mai hula iyaka Rirji. A babban falon gidan suka ci karo da Bakura tare da yaransa Abubakar, Umar da Usman sun dawo daga masallaci.
Samira ta ce "yauwa sai mu wuce kan dining table mu ci abinci ko Abban Zahra? Yau da kaina na shiga kicin na dafa maka burabusko irin na ku na barebari."
Ta ga ya yi turus bai juya ya kalli dining table din ba ma balle ya bude ya ga abinda aka dafa masa balle ya burge shi.
Zahra ta ce "Abba sannu da zuwa, shugabar makarantarmu ta ce in gaisheka."
Sai su ka ga ya tsuke fuska ya kada kai zai nufi dakinsa, har ya kai qofar fita sai ya juyo ya dubi Zahra.
Ya ce " Zahra ki kula da rayuwa, ki tabbatar kin saka tsoran Allah a cikin zuciyarki a duk inda kike. Ba ruwanki da lalatattun qawaye da samari bata gari. Na sakale Kwaryata ta gari a ragaya ba na fatan kwaryar nan ta tsinke ta fado daga ragaya ta dinga garari a tsakar gida."
Yajuya ya tafi abinsa ya tafi.
Cafdijam!!! Wannan Hausa ta yiwa Uwar Zahra tsauri balle ita Zahrar kanta. Daman idan aka dunkule Hausa, ko karin magana Zahra ba ta ganewa, ta fi gane yaren kanuri sai kuma turanci. Tabbas tana jin Hausa amma ta ina za ta fahimci wannan maganar ta da?
Samira bahaushiya ce gaba da baya amma ya aka yi wannan Babarbaren ya yi ma ta Hausa cikin Hausa ba ta fahimce shi ba? Dadin dadawa ba su san kan maganar da ya ke yi ba balle su gano bakin maganar.
Hanakalin Zahra ya tashi, ta kalli mahaifiyarta ta dafe kirji. Ta ce "Mama me na yiwa Abba, wacce kwarya ya ke magana?"
Samira ta fita da sauri ta bi shi dakinsa, ta iske zai shiga wanka, ta dube shi.
Ta ce "Sweety Zahra ta damu ta na tambayar ko wanni laifi ta yi maka."
Ya girgiza kai ya ce "ba laifin komai ta yi min ba dama ba lallai ne ku gane abinda na ke nufi ba yanzu sai a nan gaba."
Ya juya zai shiga bandaki Samira ta qara dakatar da shi. Ta ce "sai kayi wanka za ka fito mu ci abinci ko na kawo maka na ka kan daning table din nan dakinka?"
Ya girgiza kai ya ce "ba zan ci ba na qoshi."
Hankalin Samira ya tashi ta fara magana kamar mai shirin fashewa da kukan kissa da nuna damuwa.
Ta ce "haba Yayana, maigidana, abin qaunata. Ya zan dage in yi maka abincin daka fi so a rayuwarka wato burabuskon gero, kuma ka ce ba za ka ci ba. Mu yaya za' ayi mu iya ci...?"
Kafin ta rufe bakinta ya dakatar da ita ya ce "ki je ke da yaranki ku ci, ni na qoshi. zan yi wanka in kwanta idan kin shigo kada ki kunna min fitila, jada ki tashe ni ba zanyi hira ba yau. Ka da ki kuskure abinda na fada miki wannan doka ce."
Samira ta juya sadan-sadan ta fice daga dakin ba tare da ta sake cewa komai ba kuma bata san me hakan yake nufi ba.
Sai ta ji ya yi magana ya ce "ka da ku damu ke da yaranki babu wanda ya yi min wani laifi a cikinku."
Ta juyo da murna ta dube shi ta ce "kawai yanayi ne ya canja?"
Ya ce "yanayi ne kawai, yau na ga mai kama da Zuhuriyya sak kamar an tsaga kara shine hankalina ya tashi."
"Mai kama da Zuhuriyya fa ka ce? A ina? Bakura ka san abinda kake fada kuwa?" Samira ta tambaya cike da mamaki.
Ya daga mata hannu ya dakatar da ita. Ya ce " tambayoyin sun isa haka. Sai da safe."
Samira ta fito zuciyarta cike da mamaki da kokonton anya kuwa Bakura ba shi da wata aljana a jikinsa? Ko dai aljanun ne su ka tashi yau?"
Samira mace ce dirarriya mai tsawo da 'yar qiba. Fara ce sosai, sai dai ba ta da dogon hanci , bakinta madaidaici ta na da dara-daran idanuwa farare qal ma su kyau. Ba ta da gashi mai tsawo amma kuma ba gwaguyyaye ba ne. Mace ce mai tsafta gami da taushin murya, mai tsananin haquri domin idan ba ita ba ba mai iya zama da Bakura. Ta iya lallashi ta iya tausar ran mijinta, ta na da tausayi da kyautatawa masu aikinta. Ta na da son wasa da dariya da yaranta har da ma sauran jama'a. Ta na da ilimin addini daidai gwargwado da na boko duk da iyakacinta daga sakandire ta tsaya ba ta ci gaba ba haka kuma bayan ta auri Bakura bai bar ta ta ci gaba ba.
Samira ta fito ne daga babban gida ma'ana gidan arziki da mutunci. Mahaifin Samira mutumin Kano a unguwar yakasai yake. Ta na da qanne da yayye ba adadi kasanceyar mahaifinta mata hudu gare shi. Dukkansu su na nan da ransu reras. Amaryar gidan ma har yanzu ta na haihuwa.
Ta auri Bakura saboda ta na sonsa Zahra ce babbar 'yarsu ta fari kasancewar sunan mahaifiyarsa ne yake kiranta da Yagana. Zahra tayi matukar yin kama da Babanta ko ba'a fada maka ba idan ka kalli Bakura ka kalli Zahra ka san irin su daya.Banbancin shi namiji ita kuma mace. Da wuya ka kira shi Babanta sai dai ka dauka Yayanta ne kasancewar auren wuri yayi da haihuwar quruciya. Zahra tafi mahaifinta haske kasancewar ta dauko hasken fatar mahaifiyarta amma ba dukka ta dauko farin ba ta hada da baqar fatar mahaifinta sai ta bada kala mai kyau wato hasken duhu (chocolate colour).
Wannan kalar ta Zahra ta sake fitar mata da kyawunta, dogon hancinta siriri har baka irin na barebarin asali, bakinta dan qarami har ya fi na mahaifinta kyau, haka fararen haqoransu da wushiryar sama da qasa duk iri daya. Ga wani Iallausan gashi har qasan qeyarta bakikiirin mai tsawo. Jikinta abin sha' awa, doguwa ce siririya. Kirar kamar Bakura ba su da kiba.
Mazan kuwa Abubakar, Umar da Usman ga farin har gajeran hancin sak irin na mahaifiyarsu sak, daba dayan su sun yi kama da mahaifiyarsu, amma sun dauko tsayin mahaifinsu dogaye ne sosai. Allahu Akbar!! Allah mai halittar bayinSa duk yadda Ya so.
Kwana biyu Bakura ya kasance cikin yawan tunani da damuwa ga uwa uba rikirkicewar tunani. Ya na cikin damuwa, gigita da tsantsar son binciko wai shin menene alaqar Sajida da Zuhuriyyarsa, idan akwai.
Bakura ya taso daga wajen aiki, sai ya ji a ransa ba zai qara iya daurawa ba bari kawai ya zarce gidan su Sajida ko Allah zai sa ya samu abinda ya ke nema, ma' ana labarin asalin su Sajida. Bakura ya na tsayawa da motarsa a bakin qofar gidan su Sajida sai ya bude qofar ya fito yayin da gardawan da ke zazzaune a qofar gidan su ka zuba masa idanuwa su na kallonsa su na gasgata ni' imar da Rabbul samawati ya yi masa. Ya yi shigar fararen kaya, farin takalmi da farar hula, motarsa kuma kirar BMW 7 SERIES mai launin ruwan zuma. Ya fito ya tsaya yayin daya zare farin gilashin dake fuskarsa ya dubi jama'ar da ke zazzaune a qofar gidan daga dukkan alamu makarantar allo ce karatu su ke dauka.
Malam Yakubu shine mai makarantar wato mahaifin Sajida. Ya na zaune akan kujerar katako rike da zabgigiyar dorina, yara su na gabansa su na daukar karatu, da zarar sun kuskure sai ka ji ya faula musu bulalar. Malam kenan!
Bakura ya qarasa gaban Malam Yakubu ya yi sallama sannan ya durqusa ya gaishe shi. Cikin fara'a Malam ya amsa gami da ce wa "yaro ban gane ka ba."
Bakura yayi murmushi ya ce "watakila saboda ba waccan motar ba ce shiyasa ba ka gane ni ba. Ni ne wanda na zo kwanakin baya da yamma game da maganar Sajida da Abdul Abdulmajid."
Sai Malam ya fahimta ya fada cikin sakin fuska "to, to, to na gane ka yaro, to mu je wajen motarka mu tsaya."
Su ka qarasa jikin motar su ka tsaya. Bakura ya sosa gefen kunne yayi dan murmushi ya ce "Malam yaya yara, yaya jama' a?
Malam ya ce "Alhamdulillahi, mun godewa Allah. Yaro ka taimaka mana fa matuqa domin ni a iya sanina Sajida ba ta da waya. Ashe waya ya hada mata take labewa su na yin magana ba tare da mun sani ba. Har takai ta kawo Sajida za ta yi min dubara ta fita ta je su hadu a wani a waje ban sani ba. Saboda yaron nan fa na cire Sajida daga makarantar boko ta na aji biyar na sakandire. Saboda a hanyar makarantar bokon ne ya ke tare ta su dinga zance. Ni dai na fada duk lokacin da ta yarda Abdul majid ya lalata ma ta rayuwa, ma ana ta bari ya yaudare ta, ya san ta 'ya mace ya cuce ta kuma daga lokacin da na aurar da ita na yi bincike aka tabbatar min ba cikekkiyar budurwa ba ce sai na yanka ta."
Bakura ya yi shiru na wani dan lokaci kansa a sunkuye a qasa kamar mai tunani. Can ya dago da kansa ya yi ajiyar zuciya.
Ya ce "Allah ya kyauta." Malam yakubu ya dubi Bakura ya ce "wai daman ka san Sajida da Abdul majid ne ko ka na da labariKai ka fi cancanta 1