Sashe 54
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Paid book 300
0023843938
Unity bank
Jamila umar tanko
08037196708
Ta yi murmushi ta ce "Wanne irin barci ka ke yi yau tunda safe. ka san qarfe nawa ne yanzu? Qarfe daya saura har yara şun kusa tasowa daga makaranta kuma kun yi baqi ina jin mahaifiyar Sajida ce da kakarta. Sau biyu babar Sajida na leqowa kicin tana tambayata ba ka tashi ba ne. To kar su ga ko ni ce ba na so ku gaisa, gara ka je ka gaishe su sannan kai ma ka ci abinci."
Bakura ya murje ido ya ce "Ki je zan yi wanka yanzu zan fito."
Ta na fita ya miqe ya shiga bandaki ya yi wanka, gami da dauro alwalar Azahar. Tunda rana ta yi zafi ba shi da niyyar fita sai da yamma, amma jin surukansa sun zo sai ya saka manyan kaya. Rigar shadda ce koriya tazarce da wando ya dauko hula ya dora, sannan ya fito.
A nutse ya wuce falo, don cin abincin safe.
Samira ya iske a zaune a falon tana ganinsa ta tambaya. "Ka je kun gaisa da bakin?"
Ya ce "So na ke in ci abinci yunwa nake ji, ko so kike in je gaban surukai yunwa ta buge ni in kwanta?
Samria ta kwashe da dariya ta ce, "Allah ya kiyaye ma, ci abincin tukunna sai ka je ku gaisa. Ba na so dai su qara leqowa su tambaya."
Bayan sun gama cin abinci, domin ita ma ruwan shayi kawai ta kurba tun safe kasancewar idan ba da Bakura ba, bata iya cin abincin kirki.
Bakura ya miqe ya ce da Samira "To zo ki raka ni in gaishe su."
Samira ta fada cike da mamaki, "Wai ni ce zan yi maka zaman auren ne Abban Yagana? Ka ji mutum, na san sanda ka je ka yi durqushe-durqushe da gaishe-gaishen dangi har aka baka 'ya? Babu inda zan je, ka je kai kadai kun fi kusa."
Bakura ya tafi fuskarsa cike da murmushi, ya qwanqwasa qofar falon Sajida cikin ladabi ya murda ya bude. A falo ya iske su, su dukka ukun su na zaune a qasa akan kafet. Sajida na ganinsa ta tsuke fuska ta kawar da kai gefe kamar ta ga maqiyinta har sai da Umma Furera ta lura da haka, ta shiga tunanin ashe daman har yanzu da matsala a zamansu? Ashe Sajida ba ta saduda an zauna da ita lafiya ba?"
Yayi sallama ya zo a nutse ya durkusa a gabansu yana mai sunkuyar da kai kasa, don kunya da girmamawa. Ya gaishe su suka amsa dukkansu a kunyace.
Umma Furera ta ce da shi, 'Wannan kakar Sajida ce ta zo jiya daga Gashuwa, don ba ta samu ta zo biki ba, sunanta lya Azumi."
Bakura ya ce "Ai jiya Malam ya fada min, Allah sarki ya yaya hanya?"
Daidai lokacin ne Bakura ya dago ido ya dubi Iya Azumi.
Ta ce, "Angona lafiya kalau."
Ita ma ta na dubansa, amma wannan karon duban da suke yiwa juna ya tashi daga surukai ya koma duban qeqe-da-qeqe mai dauke da alamar tambaya. Duba ne irin na ban mamaki da tsantsar gigita mai hade da tashin hankali tamkar su kurma ihu, haka yanayin kowannensu ya canja. Karkarwa Bakura yake yana nuna iya Azumi ita ko hannu ta dora a ka ta na hawaye da salati.
"Lafiya, me ya faru?" Haka Umma Furera da Sajida suke tambayarsu a gigice suma
. Babu wanda ya iya ba su amsa a ciknsu.
Bakura ya yi karfin hali ya ce "Innono"
Ta amsa masa "Na'am, Bakura kai ne?"
Sai su duka suka fashe da kuka mai tafe da zazzafan hawaye.
Babu kalmar da take fitowa daga bakin Innono sai "La'ilaha illallahu Muhammadul Rasulullahi sallallahu alaihi wasalam, Bakura kana raye ashe?"
Wannan dogayen salatai ne yasa Samira shigowa cikin dakin, don ta ganewa idanuwanta abinda ke faruwa.Ta iske Bakura tsaye ya kifa kai da bango yana wani kuka mai tsanani, har idanuwansa sun yi jawur.
Ta riklqe shi a gigice tana tambayarsa lafiya. Haka Sajida da mahaifiyarta suka shiga wannan rudanin suka riqe Iya Azumi su na tambayarta "lafiya".
Ta ce, "Labarin yana da tsawo, yana da ban mamaki."
Da jin baka sai Umma Furera ta dauko waya ta danno lambar maigidanta ta na sharbar kuka.
Ta ce "Malam, ka taho gidan Sajida yanzun nan akwai magana."
A gigice ya ke tambayarta "Lafiya, guduwa ta yi?"
Umma Furera ta ce "Ko daya babu abinda ya faru, illa Iya Azumi ce da Bakura suka shaida juna su na ta koke-koke. Na san lallai akwai wani 6oyayyen al'amari sun san juna. Ka san kuwa dole yau a fayyacewa Sajida komai."
Malam ya fada cikin sauri "To gani nan zuwa.
Hankalin Sajida ya tashi matuqa da jin bayanan Ummarta. Sai ta dora hannu a ka ta rusa kuka, ta ce, "Umma, ba dai tsintata ku ka yi ba, ba ke ce ki ka haife ni ba ne?"
Umma Furera ta girgiza kai ta ce, "Ni na haife ki Sajida ba tsintarki na yi ba."
Sajida ta koma gaban Iya Azumi ta durusa, ta ce "lya ki fada min gaskiya me ya faru da ni?
lya Azumi ta runtse ido hawaye ya surnano sai ta nuna Bakura. Ta ce "Bakura ne ya fi kowa sanin ko ke wacece, amma ni ban sani ba."
Sajida ta miqe da gudu ta nufi inda Bakura ke tsaye ta durqusa a gabansa cikin kuka.
Ta ce "Bakura ni wace ce? Me yake faruwa ne?"
Bakura ya matse hawaye yasa hannu ya tashi Sajida tsaye, Ya ce, "Je ki ki zauna bari Malam ya zo, bari su Zahra su dawo daga makaranta, sannan in zo in bayar da tarihin rayuwata. Zan sanar da ke ko ke wacece, amma kada ki damu kanki ki na da uwa, kina da uba ba 'yar tsuntuwa ba ce."
Sajida ta sulale ta zauna zuciyarta na dukan uku-uku, qwaqwalwarta ta kasa shiryo mata abinda zai iya kasancewa. Fatan ta dai kar ace ba Furera da Malam ba ne suka haife ta ba, kada dai ace Bakura ne Babanta..
Haka Samira ta shiga wannan hali na mamaki da tambayoyi iri-iri. Umma Furera ma kukan take da alama ta san komai.
Bakura ya fice, Samira ta bi shi da sauri zuwa qofar fita. Ta ce da shi "Ina za ka je ne?"
Ya tsaya cak ya ce da ita "Masallaci zan je yanzu zan dawo."
Samira ta tambaya
"Me yake faruwa ne Malam?" Ya ce "Yau zan ba ku tarihin rayuwata kacokan. Yau zan bayyana muku ko ni wanene, kuma daga ina na fito, mene ne asalina? Yau za ki ji ko wacece Zuhuriyya kuma ya ya take a wajena. Yau za ki tabbatar da maganata da na ce Sajida ta yi kama da Zuhuriyya. Yau za ki tabbatar da dalilina da na dage na auri Sajida dan ada ban yarda na fada muku komai ba."
Samira ta tsaya tana kallon Bakura jikinta a sanyaye. Ta fada cikin cikin siririyar murya mai tafe da rashin kuzari,
"A dawo lafiya."
Ya fice da sauri zuwa masallaci. Fitar Bakura ba Jimawa sai ga 'yan makaranta sun dawo, wato Zahra da qannenta suka yi sallama suka shigo. Da sauri Samira ta jawo su gefe ta ce da su "Ku yi sauri ku je ku cire kayan makarantarku, ku yi sallah, ku ci abinci akwai meeting a dakin Sajida in ji Abbanku."
Cike da mamaki suke tambayarta. "Wanne irin mecting?"
Ta ce, "Ku je ku yi abinda na fada mu ku kawai, ko mene ne ma za ku ji in an je can."
Har Zahra ta shiga daki ta ajiye jakarta sai ta ji zuciyarta ta kasa kwanciya ta yi wuf ta fito tana neman mahaifiyarta ta leka ko'ina ba ta ganta ba, sai ta leqa dakin mahaifinta a can ta ganta.
Samira na ganin Zahra ta tambaye ta. "Lafiya?"
Zahra ta ce "Mama qararmu ta sake kaiwa wajen Abba?"
Samira ta ce "A'a, wani boyayyen al'amari Allah Ya bayyana, wata kakar Sajida ce ta zo daga wani gari. Ashe Abbanku ya santa, don haka dole Sajida tana da dangantaka da Zuhuriyya."
Mamaki ya rufe Zahra ta ce, "To bari in je in yi sallah in zo mu ji labarin."
Bakura da Malam Yakubu ne suka shigo kai tsaye dakin Sajida suka wuce suka iske Umma Furera, Sajida da Iya Azumi kowanne zugum ya doka tagumi babu mai cewa komai. Su ka sami kujera suka zauna. Haka Samira da 'ya'yanta suka shigo a nutse suka sami waje suka zazzauna. Bayan an gaggaisa sai Bakura ya fara gabatarwa iya Azumi 'ya'yansa da matarsa Samira.
Ta jawo Zahra jikinta ta rungume ta shafa kayukan, mazan tana mai shi musu albarka tana hawaye.
Fargaba marar musaltuwa, haka dimbun tashin hankali ne ya cika zuciyar Sajida. Ba Sajida kadai ba kowa ya qagu ya ji labari.
Bakura ya matse hawaye zazzafa daga cikin idanuwansa ya fara magana cikin wata marainiyar murya, mai nuna tsananin damuwa da alhini.Kai ka fi cancanta
0023843938
Unity bank
Jamila umar tanko
08037196708
Ta yi murmushi ta ce "Wanne irin barci ka ke yi yau tunda safe. ka san qarfe nawa ne yanzu? Qarfe daya saura har yara şun kusa tasowa daga makaranta kuma kun yi baqi ina jin mahaifiyar Sajida ce da kakarta. Sau biyu babar Sajida na leqowa kicin tana tambayata ba ka tashi ba ne. To kar su ga ko ni ce ba na so ku gaisa, gara ka je ka gaishe su sannan kai ma ka ci abinci."
Bakura ya murje ido ya ce "Ki je zan yi wanka yanzu zan fito."
Ta na fita ya miqe ya shiga bandaki ya yi wanka, gami da dauro alwalar Azahar. Tunda rana ta yi zafi ba shi da niyyar fita sai da yamma, amma jin surukansa sun zo sai ya saka manyan kaya. Rigar shadda ce koriya tazarce da wando ya dauko hula ya dora, sannan ya fito.
A nutse ya wuce falo, don cin abincin safe.
Samira ya iske a zaune a falon tana ganinsa ta tambaya. "Ka je kun gaisa da bakin?"
Ya ce "So na ke in ci abinci yunwa nake ji, ko so kike in je gaban surukai yunwa ta buge ni in kwanta?
Samria ta kwashe da dariya ta ce, "Allah ya kiyaye ma, ci abincin tukunna sai ka je ku gaisa. Ba na so dai su qara leqowa su tambaya."
Bayan sun gama cin abinci, domin ita ma ruwan shayi kawai ta kurba tun safe kasancewar idan ba da Bakura ba, bata iya cin abincin kirki.
Bakura ya miqe ya ce da Samira "To zo ki raka ni in gaishe su."
Samira ta fada cike da mamaki, "Wai ni ce zan yi maka zaman auren ne Abban Yagana? Ka ji mutum, na san sanda ka je ka yi durqushe-durqushe da gaishe-gaishen dangi har aka baka 'ya? Babu inda zan je, ka je kai kadai kun fi kusa."
Bakura ya tafi fuskarsa cike da murmushi, ya qwanqwasa qofar falon Sajida cikin ladabi ya murda ya bude. A falo ya iske su, su dukka ukun su na zaune a qasa akan kafet. Sajida na ganinsa ta tsuke fuska ta kawar da kai gefe kamar ta ga maqiyinta har sai da Umma Furera ta lura da haka, ta shiga tunanin ashe daman har yanzu da matsala a zamansu? Ashe Sajida ba ta saduda an zauna da ita lafiya ba?"
Yayi sallama ya zo a nutse ya durkusa a gabansu yana mai sunkuyar da kai kasa, don kunya da girmamawa. Ya gaishe su suka amsa dukkansu a kunyace.
Umma Furera ta ce da shi, 'Wannan kakar Sajida ce ta zo jiya daga Gashuwa, don ba ta samu ta zo biki ba, sunanta lya Azumi."
Bakura ya ce "Ai jiya Malam ya fada min, Allah sarki ya yaya hanya?"
Daidai lokacin ne Bakura ya dago ido ya dubi Iya Azumi.
Ta ce, "Angona lafiya kalau."
Ita ma ta na dubansa, amma wannan karon duban da suke yiwa juna ya tashi daga surukai ya koma duban qeqe-da-qeqe mai dauke da alamar tambaya. Duba ne irin na ban mamaki da tsantsar gigita mai hade da tashin hankali tamkar su kurma ihu, haka yanayin kowannensu ya canja. Karkarwa Bakura yake yana nuna iya Azumi ita ko hannu ta dora a ka ta na hawaye da salati.
"Lafiya, me ya faru?" Haka Umma Furera da Sajida suke tambayarsu a gigice suma
. Babu wanda ya iya ba su amsa a ciknsu.
Bakura ya yi karfin hali ya ce "Innono"
Ta amsa masa "Na'am, Bakura kai ne?"
Sai su duka suka fashe da kuka mai tafe da zazzafan hawaye.
Babu kalmar da take fitowa daga bakin Innono sai "La'ilaha illallahu Muhammadul Rasulullahi sallallahu alaihi wasalam, Bakura kana raye ashe?"
Wannan dogayen salatai ne yasa Samira shigowa cikin dakin, don ta ganewa idanuwanta abinda ke faruwa.Ta iske Bakura tsaye ya kifa kai da bango yana wani kuka mai tsanani, har idanuwansa sun yi jawur.
Ta riklqe shi a gigice tana tambayarsa lafiya. Haka Sajida da mahaifiyarta suka shiga wannan rudanin suka riqe Iya Azumi su na tambayarta "lafiya".
Ta ce, "Labarin yana da tsawo, yana da ban mamaki."
Da jin baka sai Umma Furera ta dauko waya ta danno lambar maigidanta ta na sharbar kuka.
Ta ce "Malam, ka taho gidan Sajida yanzun nan akwai magana."
A gigice ya ke tambayarta "Lafiya, guduwa ta yi?"
Umma Furera ta ce "Ko daya babu abinda ya faru, illa Iya Azumi ce da Bakura suka shaida juna su na ta koke-koke. Na san lallai akwai wani 6oyayyen al'amari sun san juna. Ka san kuwa dole yau a fayyacewa Sajida komai."
Malam ya fada cikin sauri "To gani nan zuwa.
Hankalin Sajida ya tashi matuqa da jin bayanan Ummarta. Sai ta dora hannu a ka ta rusa kuka, ta ce, "Umma, ba dai tsintata ku ka yi ba, ba ke ce ki ka haife ni ba ne?"
Umma Furera ta girgiza kai ta ce, "Ni na haife ki Sajida ba tsintarki na yi ba."
Sajida ta koma gaban Iya Azumi ta durusa, ta ce "lya ki fada min gaskiya me ya faru da ni?
lya Azumi ta runtse ido hawaye ya surnano sai ta nuna Bakura. Ta ce "Bakura ne ya fi kowa sanin ko ke wacece, amma ni ban sani ba."
Sajida ta miqe da gudu ta nufi inda Bakura ke tsaye ta durqusa a gabansa cikin kuka.
Ta ce "Bakura ni wace ce? Me yake faruwa ne?"
Bakura ya matse hawaye yasa hannu ya tashi Sajida tsaye, Ya ce, "Je ki ki zauna bari Malam ya zo, bari su Zahra su dawo daga makaranta, sannan in zo in bayar da tarihin rayuwata. Zan sanar da ke ko ke wacece, amma kada ki damu kanki ki na da uwa, kina da uba ba 'yar tsuntuwa ba ce."
Sajida ta sulale ta zauna zuciyarta na dukan uku-uku, qwaqwalwarta ta kasa shiryo mata abinda zai iya kasancewa. Fatan ta dai kar ace ba Furera da Malam ba ne suka haife ta ba, kada dai ace Bakura ne Babanta..
Haka Samira ta shiga wannan hali na mamaki da tambayoyi iri-iri. Umma Furera ma kukan take da alama ta san komai.
Bakura ya fice, Samira ta bi shi da sauri zuwa qofar fita. Ta ce da shi "Ina za ka je ne?"
Ya tsaya cak ya ce da ita "Masallaci zan je yanzu zan dawo."
Samira ta tambaya
"Me yake faruwa ne Malam?" Ya ce "Yau zan ba ku tarihin rayuwata kacokan. Yau zan bayyana muku ko ni wanene, kuma daga ina na fito, mene ne asalina? Yau za ki ji ko wacece Zuhuriyya kuma ya ya take a wajena. Yau za ki tabbatar da maganata da na ce Sajida ta yi kama da Zuhuriyya. Yau za ki tabbatar da dalilina da na dage na auri Sajida dan ada ban yarda na fada muku komai ba."
Samira ta tsaya tana kallon Bakura jikinta a sanyaye. Ta fada cikin cikin siririyar murya mai tafe da rashin kuzari,
"A dawo lafiya."
Ya fice da sauri zuwa masallaci. Fitar Bakura ba Jimawa sai ga 'yan makaranta sun dawo, wato Zahra da qannenta suka yi sallama suka shigo. Da sauri Samira ta jawo su gefe ta ce da su "Ku yi sauri ku je ku cire kayan makarantarku, ku yi sallah, ku ci abinci akwai meeting a dakin Sajida in ji Abbanku."
Cike da mamaki suke tambayarta. "Wanne irin mecting?"
Ta ce, "Ku je ku yi abinda na fada mu ku kawai, ko mene ne ma za ku ji in an je can."
Har Zahra ta shiga daki ta ajiye jakarta sai ta ji zuciyarta ta kasa kwanciya ta yi wuf ta fito tana neman mahaifiyarta ta leka ko'ina ba ta ganta ba, sai ta leqa dakin mahaifinta a can ta ganta.
Samira na ganin Zahra ta tambaye ta. "Lafiya?"
Zahra ta ce "Mama qararmu ta sake kaiwa wajen Abba?"
Samira ta ce "A'a, wani boyayyen al'amari Allah Ya bayyana, wata kakar Sajida ce ta zo daga wani gari. Ashe Abbanku ya santa, don haka dole Sajida tana da dangantaka da Zuhuriyya."
Mamaki ya rufe Zahra ta ce, "To bari in je in yi sallah in zo mu ji labarin."
Bakura da Malam Yakubu ne suka shigo kai tsaye dakin Sajida suka wuce suka iske Umma Furera, Sajida da Iya Azumi kowanne zugum ya doka tagumi babu mai cewa komai. Su ka sami kujera suka zauna. Haka Samira da 'ya'yanta suka shigo a nutse suka sami waje suka zazzauna. Bayan an gaggaisa sai Bakura ya fara gabatarwa iya Azumi 'ya'yansa da matarsa Samira.
Ta jawo Zahra jikinta ta rungume ta shafa kayukan, mazan tana mai shi musu albarka tana hawaye.
Fargaba marar musaltuwa, haka dimbun tashin hankali ne ya cika zuciyar Sajida. Ba Sajida kadai ba kowa ya qagu ya ji labari.
Bakura ya matse hawaye zazzafa daga cikin idanuwansa ya fara magana cikin wata marainiyar murya, mai nuna tsananin damuwa da alhini.Kai ka fi cancanta