Sashe 38
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
*** *** ***
A cikin satin Bakura ya je gidan Hajjiya Farida ta dauko masa dogon list din abubuwan da ya kamata ya zuba a lefen amarya da uwargida iri daya, kamar
yadda Bakura ya umarce ta da ta yi komai iri daya kada ta bambanta. Hakika kayan suna da yawa, kuma tsadaddu ne, don haka miliyoyi za su sha kashi, akwatuna shida-shida har da kite din gwalagwalai. Ya ce ta lissafa akwatunan bibbiyu na Mahaifin samira da mahaifiyar Samira sannan Akwatuna bibbiyu na Mahaifin Sajida, biyu na Mahaifiyarta. Sai akwati guda ta Zahra, Akwati guda-guda ta Abubakar, Umar da na Usman. Cas ya caske mata kudin ya miqa mata cek, don haka a satin ta shigar da visa tafiya qasashe biyu don hado lefen, wato London da Dubai. Ta ba shi tabbacin a cikin sati biyu komai zai kammala.
A cikin satin Bakura ya yi wa kamfanin da suke yi masa gyaran gida da kawatawa waya ya ce su zo ga aiki, turawa ne, ofishinsu ya na Abuja. Ya sanar musu yana so su zo su sake masa fenti, labulaye da gaba daya furniture gidan, na zamani, sabon yayi. Sun san Bakura, sun san halinsa akwai naira, kuma baya tsoron kashewa. Abun ka da Nasara a sarar duniya a ranar suka hawo jirgin yamma daga Abuja zuwa Kano, su uku ne mace daya, maza biyu suka fara aune-aune, gwaje-gwaje, rubuce-rubuce da lissafe-lissafe. Babu irin lallashin da magiyar da Bakura bai yiwa Samira ba a kan ta zo su zauna da ma'aikatan nan ta fada musu yadda take son a tsara gidanta, ta qi fitowa. Ta ce duk yadda yake so ya je ya yi shi da amaryarsa Sajida.
Duk da aikinsu ne, amma hankalin Bakura bai kwanta ba sai da ya yi kiran Zahra ta zo ta zauna da su ta fada musu kaloli da irin yadda take ganin zai yi kyau.
Bakura ya yi ajiyar zuciya ya dubi Zahra ya ce,
"Wancan dakin da ku ke kira dakin baqi shi ne zai zama dakin Sajida, za a zuba mata kaya iri daya dana Mamarki, sai dai kalar ta bambanta. Haka bandakunan ma duk a ciccire tiles da kayan ciki a zuba masu tsada."
Zahra ta yi 'dumm' yayin da shi ma Bakura ya kula da hakan. Da alama ba ta ji dadin batunsa ba. Babu yadda ta iya haka ta kaikace ta zabarwa Sajida kalar fenti, labule, kujeru, gadaje, talibijin, C.D, hometharter, kayan toilet da dai sauransu, wadanda darajarsu daya da na Mamarta. Haka ta tsara dakin Bakura, haka na ta da na qannenta da kicin. Kacokan farfajiyar gidan aka canja yanayinta. Duk wannan abinda ake Samira ko uffan ba ta cewa, daki ta shige ta yi kwanciyarta.
*** *** ***
A cikin satin aka duqufa aka fara gyara, aka fitar da tsofaffin kayan gidan aka rabarwa 'yan uwa da abokan arziki, masu aiki ma suka kwashi rabonsu. Aka fente gida aka zuba komai sabo daga cikinnkwalayensu. Duk da ma'aikatan su na da kayan aiki na zamani sai da gyare-gyaren ya dauke su tsawon sati biyu, amma fa gida ya tsaru. Idan wanda bai sani ba ya shigo gidan sai ya rantse da Allah batan kai ya yi ba gidan ba ne qasar waje ne. Daidai sanda aka gama gyaran gidan daidai lokacin da Hajiya Farida ta gama hado lefe. Me ya yi saura?
Hajiya Farida da kawayenta guda biyu, sai matan abokansa uku da kannensa biyu daga Maiduguri ne suka hadu suka kai lefen Sajida. Umma Furera da 'yan uwanta da maqwabta sai suka bude baki kawai su na kallon wannan abin al'ajabi, sun ga lefen da duk tsurkukin unguwarsu ba a taba kawo irinsa ba. Naira ta yi kuka, lallai ko ba a fada ba kowa ya san Sajida ta yi tuntube da kasaitaccen miji mai arziki. Sal dai Hajiya Farida da tawagarta sun shiga wani hali na mamaki da ta yadda aka yi Bakura ya fada hannun wadannan talakawa liqis, sun yi bazata ba su dauka irin wannan gida da irin wadannan mutane za su kawowa wannan uwar dukiya ba. Bayan lefen har da damin kudin dinki da buhunhunan abinci. Kai hatta nama da juices da za a sha a ci ya aiko da su, domin dirkeken SA' aka turkewa Malam a qofar gida. Allah sarki yaku-bayi, zobo, kunun aya da lemon kwalba guda goma su Umma Furera suka tanadarwa baqi, sai dan cincin.
Hajja Farida suka shigowa Samira da albishirin cewar ta kwantar da hankalinta tamkar tsumma a randa. Yarinya dai ba kishiyarta ba ce mai aikinta ce, domin babu wayewa a tare da ita. Su ka yi wa Samira hudubar ta saki ranta ta dinka lefenta ta dinga caba ado, yadda ita kanta yarinyar da 'yan uwanta masu kawo amarya za su kidime. Haka shi ma mijin zai san ya yi kuskure wajen jajabo bakauyiya, 'yar talakawa likis.
Hakika Samira ta dauki shawararsu ta dan saki ranta, don haka ta shiga gyaran jiki ciki da waje.
Abu kamar wasa qaramar magana ta zama babba,in ji wani mawaqi. Auren Bakura da Sajida ya tabbata. Sai dai tun ranar da Bakura da Sajida suka hadu a zaure ba su sake ganin juna ba. Haka daidai da sakon daya Sajida ba ta ta6a saduda ta furta da bakinta ta ce yarda za ta auri Bakura ba. Ko da yaushe zillo take ana riqo ta kamar wata kifi. Duk da dinbin dukiyar da ta ga an kawo an jibge a gidansu kace-kace, bai sa Sajida ta ji digon son auren nan ba. Ta rame, ta Jejjeme, saboda tsananin kiyayyar auren. Sai kuka, sai tabara da tsiwar da take tafka musu a cikin gidan.
Dole ce tasa Umma Furera ta shiga cikin qawayen Sajida suka yi ta fita tare don aiwatar da abubuwan biki, kamar su kai dinkunan da amarya za ta saka ranar biki, da buga katin gayyatar biki. Haka Malam da almajiransa suma suka bazama suka shiga kasuwa don siyo fenti, tabarmin da zaa shimfidawa baqi su zauna 'yan daurin aure da katin gayyata. Domin daga dukkan alamu manyan baqi, jiga-jigan masu kudi, masu sarauta, 'yan kasuwa, da 'yan siyasa ne za zu halicci daurin auren nan. hakuri yake bayarwa baya gajiyawa. ta qona gidan, Allah ya kiyaye."
A cikin satin Bakura ya je gidan Hajjiya Farida ta dauko masa dogon list din abubuwan da ya kamata ya zuba a lefen amarya da uwargida iri daya, kamar
yadda Bakura ya umarce ta da ta yi komai iri daya kada ta bambanta. Hakika kayan suna da yawa, kuma tsadaddu ne, don haka miliyoyi za su sha kashi, akwatuna shida-shida har da kite din gwalagwalai. Ya ce ta lissafa akwatunan bibbiyu na Mahaifin samira da mahaifiyar Samira sannan Akwatuna bibbiyu na Mahaifin Sajida, biyu na Mahaifiyarta. Sai akwati guda ta Zahra, Akwati guda-guda ta Abubakar, Umar da na Usman. Cas ya caske mata kudin ya miqa mata cek, don haka a satin ta shigar da visa tafiya qasashe biyu don hado lefen, wato London da Dubai. Ta ba shi tabbacin a cikin sati biyu komai zai kammala.
A cikin satin Bakura ya yi wa kamfanin da suke yi masa gyaran gida da kawatawa waya ya ce su zo ga aiki, turawa ne, ofishinsu ya na Abuja. Ya sanar musu yana so su zo su sake masa fenti, labulaye da gaba daya furniture gidan, na zamani, sabon yayi. Sun san Bakura, sun san halinsa akwai naira, kuma baya tsoron kashewa. Abun ka da Nasara a sarar duniya a ranar suka hawo jirgin yamma daga Abuja zuwa Kano, su uku ne mace daya, maza biyu suka fara aune-aune, gwaje-gwaje, rubuce-rubuce da lissafe-lissafe. Babu irin lallashin da magiyar da Bakura bai yiwa Samira ba a kan ta zo su zauna da ma'aikatan nan ta fada musu yadda take son a tsara gidanta, ta qi fitowa. Ta ce duk yadda yake so ya je ya yi shi da amaryarsa Sajida.
Duk da aikinsu ne, amma hankalin Bakura bai kwanta ba sai da ya yi kiran Zahra ta zo ta zauna da su ta fada musu kaloli da irin yadda take ganin zai yi kyau.
Bakura ya yi ajiyar zuciya ya dubi Zahra ya ce,
"Wancan dakin da ku ke kira dakin baqi shi ne zai zama dakin Sajida, za a zuba mata kaya iri daya dana Mamarki, sai dai kalar ta bambanta. Haka bandakunan ma duk a ciccire tiles da kayan ciki a zuba masu tsada."
Zahra ta yi 'dumm' yayin da shi ma Bakura ya kula da hakan. Da alama ba ta ji dadin batunsa ba. Babu yadda ta iya haka ta kaikace ta zabarwa Sajida kalar fenti, labule, kujeru, gadaje, talibijin, C.D, hometharter, kayan toilet da dai sauransu, wadanda darajarsu daya da na Mamarta. Haka ta tsara dakin Bakura, haka na ta da na qannenta da kicin. Kacokan farfajiyar gidan aka canja yanayinta. Duk wannan abinda ake Samira ko uffan ba ta cewa, daki ta shige ta yi kwanciyarta.
*** *** ***
A cikin satin aka duqufa aka fara gyara, aka fitar da tsofaffin kayan gidan aka rabarwa 'yan uwa da abokan arziki, masu aiki ma suka kwashi rabonsu. Aka fente gida aka zuba komai sabo daga cikinnkwalayensu. Duk da ma'aikatan su na da kayan aiki na zamani sai da gyare-gyaren ya dauke su tsawon sati biyu, amma fa gida ya tsaru. Idan wanda bai sani ba ya shigo gidan sai ya rantse da Allah batan kai ya yi ba gidan ba ne qasar waje ne. Daidai sanda aka gama gyaran gidan daidai lokacin da Hajiya Farida ta gama hado lefe. Me ya yi saura?
Hajiya Farida da kawayenta guda biyu, sai matan abokansa uku da kannensa biyu daga Maiduguri ne suka hadu suka kai lefen Sajida. Umma Furera da 'yan uwanta da maqwabta sai suka bude baki kawai su na kallon wannan abin al'ajabi, sun ga lefen da duk tsurkukin unguwarsu ba a taba kawo irinsa ba. Naira ta yi kuka, lallai ko ba a fada ba kowa ya san Sajida ta yi tuntube da kasaitaccen miji mai arziki. Sal dai Hajiya Farida da tawagarta sun shiga wani hali na mamaki da ta yadda aka yi Bakura ya fada hannun wadannan talakawa liqis, sun yi bazata ba su dauka irin wannan gida da irin wadannan mutane za su kawowa wannan uwar dukiya ba. Bayan lefen har da damin kudin dinki da buhunhunan abinci. Kai hatta nama da juices da za a sha a ci ya aiko da su, domin dirkeken SA' aka turkewa Malam a qofar gida. Allah sarki yaku-bayi, zobo, kunun aya da lemon kwalba guda goma su Umma Furera suka tanadarwa baqi, sai dan cincin.
Hajja Farida suka shigowa Samira da albishirin cewar ta kwantar da hankalinta tamkar tsumma a randa. Yarinya dai ba kishiyarta ba ce mai aikinta ce, domin babu wayewa a tare da ita. Su ka yi wa Samira hudubar ta saki ranta ta dinka lefenta ta dinga caba ado, yadda ita kanta yarinyar da 'yan uwanta masu kawo amarya za su kidime. Haka shi ma mijin zai san ya yi kuskure wajen jajabo bakauyiya, 'yar talakawa likis.
Hakika Samira ta dauki shawararsu ta dan saki ranta, don haka ta shiga gyaran jiki ciki da waje.
Abu kamar wasa qaramar magana ta zama babba,in ji wani mawaqi. Auren Bakura da Sajida ya tabbata. Sai dai tun ranar da Bakura da Sajida suka hadu a zaure ba su sake ganin juna ba. Haka daidai da sakon daya Sajida ba ta ta6a saduda ta furta da bakinta ta ce yarda za ta auri Bakura ba. Ko da yaushe zillo take ana riqo ta kamar wata kifi. Duk da dinbin dukiyar da ta ga an kawo an jibge a gidansu kace-kace, bai sa Sajida ta ji digon son auren nan ba. Ta rame, ta Jejjeme, saboda tsananin kiyayyar auren. Sai kuka, sai tabara da tsiwar da take tafka musu a cikin gidan.
Dole ce tasa Umma Furera ta shiga cikin qawayen Sajida suka yi ta fita tare don aiwatar da abubuwan biki, kamar su kai dinkunan da amarya za ta saka ranar biki, da buga katin gayyatar biki. Haka Malam da almajiransa suma suka bazama suka shiga kasuwa don siyo fenti, tabarmin da zaa shimfidawa baqi su zauna 'yan daurin aure da katin gayyata. Domin daga dukkan alamu manyan baqi, jiga-jigan masu kudi, masu sarauta, 'yan kasuwa, da 'yan siyasa ne za zu halicci daurin auren nan. hakuri yake bayarwa baya gajiyawa. ta qona gidan, Allah ya kiyaye."