Sashe 24
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ****
Sajida ce a zaune a cikin rana taną Juye-juye. Kallo daya zaka yi mata ka tabbatar bata jin dadin jikinta ga tsananin damuwa. Umma furera ce ta fito daga dakinta dauke da katuwar fanteka a cike da geron kunun kanwarta na Siyarwa zaa kai mata Surfe.Dakyar take tafiya saboda nauyi, ta cije baki ta ajiye a kasa yayin da ta dafe kashin bayanta tana sallati.
Ta juya ta dubi sajida. Ta ce "yanzu Sajida ba zaki tashi daga rana ba? Tun dazu nake faman yi da bakina amma kinki tashi, hantsin har ya fara zafi. Idan sanyi kike ji ki shiga daki ki lulluba, rana ciwon kai da zazzabi zata sake jawo miki."
Sajida ta dago da luhu-luhun idamuwanta wadanda suka kumbura a sanadiyyar koke-koke da zafin zazzabi ta dubi mahaifiyarta.Ta ce "Umma, tabbas kun kusa ku nemeni ku rasa kuma idan na tafi na tafi kenan."
Umma Furera tayi kasake a tsaye ta hada hannu ta rike ciki tana duban Sajida. Can ta karaso inda take ta ciccibo hakarkarinta ta daga ta tsaye. Tana fadin tashi daga rana mu koma inuwa sai muyi maganar. Umma Furera ta mayar da Sajida inuwa ta zaunar da ita akan wata tsohuwar tabarma ta jawo kujera ta zauna a kusa da Sajida.
Ta ce "yanzu Sajida ba zaki hakura ki fauwala Allah komai ba, akan Abdul majid ki ringa kokarin ki kashe kanki. Babu ci ba sha har kike tunanin guduwa a nemeki a rasa ki jefa iyayenki da yan'uwanki da duk wani mai sonki cikin damuwa da bacin rai dauwamammiya. Idan kika gudu kin tashe mu tsaye musamman ni da mahaifinki, zaki tasar mana da ciwon da zai iya zama ajalinmu. Ga mahaifinki ya tsufa fuk daya zuciyarsa zata iya fashewa, nima gashi girma ya zo kece abokiyar shawarata tamkar qawata nake hira dake ga dan karamin kaninki yahuza duk inda ya fita ya samo labari wajenki yake nufowa kai tsaye ya fesa miki. Idan kika tafi kika bar mu yaya zamu yi?"
Ummma furera ta fashe da kuka. Sajida ma kukan ya kece mata. Har tsawon lokaci babu mai iya lallashin wani. Sajida ta dago da jajayen idanuwanta ta dubi mahaifiyarya.
Ta ce "Umma, ina tunanin yarinyar nan Zahra da ta zo kwanakin baya, turo ta aka yi ta zo taga halinda nake ciki da Abdulmajid ta kai rahoto domin ita tasan ina lekawa ta katanga ina aron waya in bugawa Abdul majid."
Umma furera ta tsagaita da kukan ta dubi Sajida fuskarta cike da rudani. Tayi doguwar ajiyar zuciya.
Ta ce "Sajida ban fahimce ki ba. Wacce yarinya kike magana?"
Sajida ta ce "Zahrar nan wacce Baba ya shigo da ita kwananakin baya ya ce 'yar gidan mai daukar karatu ce a kofar gida. Har na ari wayarta na bugawa Abdul majid. A dalilin bamu bata kunu ba Baba ya hana ki yin kunun siyarwa har sati guda."
Umma Furera ta ce "kwarai kuwa na tuno ta
tabbas anyi haka. Ba lallai ba ne ita ta fada amma akwai alamar tambaya. Da farko ma a ina ya santa har zai kawo ta ya tafi ya barta a cikin gida? Na biyu bayan tafiyarta ne ya shigo yayi miki wannan dukan har muka dauki alhakin Yahuza. To ko budurwa Abdul majid ce take bibiyarki don ta san ya fi sonki, ko daman ita take hada miki tuggu don babanki ya raba ku duk motsin da ki kayi da Abdulmajid sai an fadawa mahaifinki?"
Sajida ta girgiza kai ta ce "Abdul majid bashi da budurwa, ni kadai ce budurwarsa a duniya haka ni kadai ya taba so kuma yayi min alkawari har karshen rayuwarsa ba zai taba son wata 'ya mace ba. Yayi min
rantsuwa tun sanda ya hadu dani bai taba jin yana son wata ba. Umma, wallahi na rantse da ubangijin daya halicce ni tunda Zahra ta zo har gida tayi min gulma tayi min sanadiyyar da na daina samun damar yin magana da Abdulmajid a waya har tsawon wata guda kenan. Asanadiyyar wannan na daina cin abinci, na daina bacci sai kuka, ga zazzabi da ciwon kai. Na yi alkawari duk ranar da na yi ido hudu da Zahra sai nayi mata rashin mutuncin da ' ban taba yiwa kowa ba ldan ma son
Abdulmajid take ko a dangin Abdul majid take daman da yawansu basa sona hakika sai na nakasta ta, nakasar da itama nata sauranyin zai daina sonta ta ji yadda nake ji data rabani da nawa masoyin."
Umma furera ta rike baki ta ce "a'a Sajida kada ki jawo mana abinda za a maka mu a kotu daga mu har ke. Kada kiyi kisan da zaki jawo a kashe ki a dalilin wani Abdulmajid. klnga yarinyar nan daga gani 'yar gidan masu kudi ce, ko bata da gaskiya ubanta ya na da halin da zai fada aji a hukunta mu balle ma ki nakasta ta ko ina aka je ke ce marar gaskiya. Sajida ina raba ki da wannan banzar zuciyar taki, saurin fushi da yawan dacin rai, tsiwa da futsara."
Sajida ta hasala ta mike tsaye tana gatsine, tana murguda baki, tana zare ido irin na tsantsar futsarar da ta saba.
Ta ce "Umma, me naji kina cewa? Kina nufin in hadu da Zahra ta wuce in wuce ban tanka mata ba? Haba ashe ba'a haifeni da jini ba, daga sama na fado. Don ubanta yana da kudi sai tayi min laifi in kyaleta? Wallahi na yarda in dauwama a daure a kurkuku har karshen rayuwata da in zubawa makiyiyata ido. Ni kuwa a rayuwata me zanyi da mutumin da baya kaunata da Abdulmajid?"
Kafin Sajida ta rufe bakinta mahaifinta ya sako kai cikin gidan, domin har kofar gida yake jiwo tsiwar
Sajida duk da cewa baya gane abunda take fada amma ya san zancen bana dadi ba ne.
Sajida na ganinsa tayi shiru amma taci gaba da harare-harerenta.
Ya dubeta cikin fushi Ya ce "ke kuma hayaniyar me kike yi kamar kina magana da sa'arki? Mahaifiyar taki kike dagawa murya har kofar gida?"
Sajida tayi shiru tana ta fusge-fusgen kai alamar ko a mutu ko ayi rai, ayi duk wacce za'ayi wai da bera ya zubar da garin mage.
Umma furera tayi caraf
Ta ce "ah, ba wani abu ba ne malam. Zafin zazzabi ne yake sakata surutai barkatai."
Malam ya ce surutan zazzabi daban haka rashin kunya daban. Nasan dalilin zazzabin nata ai shiru nayi muku kawai, a dalilin raba ta da dan iskan yaron nan Abdulmajid shine yasa take kokarin kashe kanta saboda taurin kai irin nata. To bari kiji in fada miki Sajida ko ki warware ki ci gaba da walwalar ki, ko ki ci gaba da takura kanki cikin kunci ki hadiyi zuciya ki mutu a wajena duk daya ne kuma ina nan akan bakata har abada ba zaki sake haduwa da Abdulmajid ba balle ya lalata ki, daman ba aurenki zai yi ba."
Sajida ta fusata ta murguda baki ta fada cikin tsiwa "an takurawa rayuwata a gidan nan, gara in mutu ma in huta. Haka kawai kowacce yarinya ana barinta ta kula wanda take so sai ni za'a takurawa. An kulle ni a gida, an hana ni karatu, an hanani fita makarantar Islamiyya da makarantar dare sai duka da zagi kullum ba kakkautawa.."
Ba ta rufe bakinta ba ta ga ya wurgo tabarya ta gefen fuskarta, saura kiris ta same ta a kunci. Malam ne a fusace ya wawuro tabaryar ya wurgo mata bai damu da ko zai fasa mata kai koma ya kasheta ba. Da turmin zai cicciba ya wurga mata, yaji da nauyi ba zai ya dauka ba.
Ihun Umma Furera ne ya qara tunzura shi ya ji dama ace ya same ta tayi ihun da hujja.
Sajida ta zura da gudu ta shige dakinta da gudu ta sakale da şakata.
Malam na huci yana ta "har fitsarar taki ta dawo kaina ina fada kina fada saboda kin raina kowa. To wallahi ba'a gidana ba, inyi wahala dake tun da aka haifeki zuwa girma sannan kice ban isa in fada miki ki ji ba to sai dai idan ba'a karkashina kike ba ki tattara kayanki ki tafi kiyi zaman kanki tunda kina ganin ke kika haifi kanki, kin girma kinfi karfin kowa. Ni kuwa idan ni na haifeki kuma da sauran numfashina a duniya wallahi ba zaki auri Abdulmajid ba ko zaki mutu.
Ya juya ya dubi furera ya ce "ke ce uwar banza da ba kya tsawatarwa 'yarki.Banga amfanin zama da ke ba tunda ya'ya biyu kin kasa ba su tarbiyya da sun kai guda goma ma ban san tabarar da za'ayi min a gidan nan ba. To bari in fada miki zamanki a gidan nan ya kusa karewa, ke ki rasa aurenki itama ta rasa Abdul majid din kuyi biyu babu. Dan haka kisa ido, idan na sake jin maganar dan iskan yaron nan Abdulmajid a gidan nan zaku ga yadda zanyi muku.Sajida albishirinki a cikin satin nan zan yi miki miji ko kina so ko bakya so shi zaki aura kuma dole ki zauna, ba zaki sake yin wata guda a gidana ba insha Allah"
Ya kade babbar rigarsa ya fice yana huci ya bar umma furera a takure a lungu ta buga tagumi. Zuciyarta sai dukan uku-uku take saboda tashin hankali. Yayin da Sajida ta kwalla ihu ta fada kan katifa tana rusa kuka kamar ranta zai fita.
Umma furera tayi ta buga kofa tana magiya Sajida ta qi bude kofa. Sai da tayi kuka ta gaji da kanta sannan ta bude kofar. Umma furera ta shiga lallashinta akan ta daure ta ci abinci amma Sajida ta qi ci.Paid book #300
Sajida ce a zaune a cikin rana taną Juye-juye. Kallo daya zaka yi mata ka tabbatar bata jin dadin jikinta ga tsananin damuwa. Umma furera ce ta fito daga dakinta dauke da katuwar fanteka a cike da geron kunun kanwarta na Siyarwa zaa kai mata Surfe.Dakyar take tafiya saboda nauyi, ta cije baki ta ajiye a kasa yayin da ta dafe kashin bayanta tana sallati.
Ta juya ta dubi sajida. Ta ce "yanzu Sajida ba zaki tashi daga rana ba? Tun dazu nake faman yi da bakina amma kinki tashi, hantsin har ya fara zafi. Idan sanyi kike ji ki shiga daki ki lulluba, rana ciwon kai da zazzabi zata sake jawo miki."
Sajida ta dago da luhu-luhun idamuwanta wadanda suka kumbura a sanadiyyar koke-koke da zafin zazzabi ta dubi mahaifiyarta.Ta ce "Umma, tabbas kun kusa ku nemeni ku rasa kuma idan na tafi na tafi kenan."
Umma Furera tayi kasake a tsaye ta hada hannu ta rike ciki tana duban Sajida. Can ta karaso inda take ta ciccibo hakarkarinta ta daga ta tsaye. Tana fadin tashi daga rana mu koma inuwa sai muyi maganar. Umma Furera ta mayar da Sajida inuwa ta zaunar da ita akan wata tsohuwar tabarma ta jawo kujera ta zauna a kusa da Sajida.
Ta ce "yanzu Sajida ba zaki hakura ki fauwala Allah komai ba, akan Abdul majid ki ringa kokarin ki kashe kanki. Babu ci ba sha har kike tunanin guduwa a nemeki a rasa ki jefa iyayenki da yan'uwanki da duk wani mai sonki cikin damuwa da bacin rai dauwamammiya. Idan kika gudu kin tashe mu tsaye musamman ni da mahaifinki, zaki tasar mana da ciwon da zai iya zama ajalinmu. Ga mahaifinki ya tsufa fuk daya zuciyarsa zata iya fashewa, nima gashi girma ya zo kece abokiyar shawarata tamkar qawata nake hira dake ga dan karamin kaninki yahuza duk inda ya fita ya samo labari wajenki yake nufowa kai tsaye ya fesa miki. Idan kika tafi kika bar mu yaya zamu yi?"
Ummma furera ta fashe da kuka. Sajida ma kukan ya kece mata. Har tsawon lokaci babu mai iya lallashin wani. Sajida ta dago da jajayen idanuwanta ta dubi mahaifiyarya.
Ta ce "Umma, ina tunanin yarinyar nan Zahra da ta zo kwanakin baya, turo ta aka yi ta zo taga halinda nake ciki da Abdulmajid ta kai rahoto domin ita tasan ina lekawa ta katanga ina aron waya in bugawa Abdul majid."
Umma furera ta tsagaita da kukan ta dubi Sajida fuskarta cike da rudani. Tayi doguwar ajiyar zuciya.
Ta ce "Sajida ban fahimce ki ba. Wacce yarinya kike magana?"
Sajida ta ce "Zahrar nan wacce Baba ya shigo da ita kwananakin baya ya ce 'yar gidan mai daukar karatu ce a kofar gida. Har na ari wayarta na bugawa Abdul majid. A dalilin bamu bata kunu ba Baba ya hana ki yin kunun siyarwa har sati guda."
Umma Furera ta ce "kwarai kuwa na tuno ta
tabbas anyi haka. Ba lallai ba ne ita ta fada amma akwai alamar tambaya. Da farko ma a ina ya santa har zai kawo ta ya tafi ya barta a cikin gida? Na biyu bayan tafiyarta ne ya shigo yayi miki wannan dukan har muka dauki alhakin Yahuza. To ko budurwa Abdul majid ce take bibiyarki don ta san ya fi sonki, ko daman ita take hada miki tuggu don babanki ya raba ku duk motsin da ki kayi da Abdulmajid sai an fadawa mahaifinki?"
Sajida ta girgiza kai ta ce "Abdul majid bashi da budurwa, ni kadai ce budurwarsa a duniya haka ni kadai ya taba so kuma yayi min alkawari har karshen rayuwarsa ba zai taba son wata 'ya mace ba. Yayi min
rantsuwa tun sanda ya hadu dani bai taba jin yana son wata ba. Umma, wallahi na rantse da ubangijin daya halicce ni tunda Zahra ta zo har gida tayi min gulma tayi min sanadiyyar da na daina samun damar yin magana da Abdulmajid a waya har tsawon wata guda kenan. Asanadiyyar wannan na daina cin abinci, na daina bacci sai kuka, ga zazzabi da ciwon kai. Na yi alkawari duk ranar da na yi ido hudu da Zahra sai nayi mata rashin mutuncin da ' ban taba yiwa kowa ba ldan ma son
Abdulmajid take ko a dangin Abdul majid take daman da yawansu basa sona hakika sai na nakasta ta, nakasar da itama nata sauranyin zai daina sonta ta ji yadda nake ji data rabani da nawa masoyin."
Umma furera ta rike baki ta ce "a'a Sajida kada ki jawo mana abinda za a maka mu a kotu daga mu har ke. Kada kiyi kisan da zaki jawo a kashe ki a dalilin wani Abdulmajid. klnga yarinyar nan daga gani 'yar gidan masu kudi ce, ko bata da gaskiya ubanta ya na da halin da zai fada aji a hukunta mu balle ma ki nakasta ta ko ina aka je ke ce marar gaskiya. Sajida ina raba ki da wannan banzar zuciyar taki, saurin fushi da yawan dacin rai, tsiwa da futsara."
Sajida ta hasala ta mike tsaye tana gatsine, tana murguda baki, tana zare ido irin na tsantsar futsarar da ta saba.
Ta ce "Umma, me naji kina cewa? Kina nufin in hadu da Zahra ta wuce in wuce ban tanka mata ba? Haba ashe ba'a haifeni da jini ba, daga sama na fado. Don ubanta yana da kudi sai tayi min laifi in kyaleta? Wallahi na yarda in dauwama a daure a kurkuku har karshen rayuwata da in zubawa makiyiyata ido. Ni kuwa a rayuwata me zanyi da mutumin da baya kaunata da Abdulmajid?"
Kafin Sajida ta rufe bakinta mahaifinta ya sako kai cikin gidan, domin har kofar gida yake jiwo tsiwar
Sajida duk da cewa baya gane abunda take fada amma ya san zancen bana dadi ba ne.
Sajida na ganinsa tayi shiru amma taci gaba da harare-harerenta.
Ya dubeta cikin fushi Ya ce "ke kuma hayaniyar me kike yi kamar kina magana da sa'arki? Mahaifiyar taki kike dagawa murya har kofar gida?"
Sajida tayi shiru tana ta fusge-fusgen kai alamar ko a mutu ko ayi rai, ayi duk wacce za'ayi wai da bera ya zubar da garin mage.
Umma furera tayi caraf
Ta ce "ah, ba wani abu ba ne malam. Zafin zazzabi ne yake sakata surutai barkatai."
Malam ya ce surutan zazzabi daban haka rashin kunya daban. Nasan dalilin zazzabin nata ai shiru nayi muku kawai, a dalilin raba ta da dan iskan yaron nan Abdulmajid shine yasa take kokarin kashe kanta saboda taurin kai irin nata. To bari kiji in fada miki Sajida ko ki warware ki ci gaba da walwalar ki, ko ki ci gaba da takura kanki cikin kunci ki hadiyi zuciya ki mutu a wajena duk daya ne kuma ina nan akan bakata har abada ba zaki sake haduwa da Abdulmajid ba balle ya lalata ki, daman ba aurenki zai yi ba."
Sajida ta fusata ta murguda baki ta fada cikin tsiwa "an takurawa rayuwata a gidan nan, gara in mutu ma in huta. Haka kawai kowacce yarinya ana barinta ta kula wanda take so sai ni za'a takurawa. An kulle ni a gida, an hana ni karatu, an hanani fita makarantar Islamiyya da makarantar dare sai duka da zagi kullum ba kakkautawa.."
Ba ta rufe bakinta ba ta ga ya wurgo tabarya ta gefen fuskarta, saura kiris ta same ta a kunci. Malam ne a fusace ya wawuro tabaryar ya wurgo mata bai damu da ko zai fasa mata kai koma ya kasheta ba. Da turmin zai cicciba ya wurga mata, yaji da nauyi ba zai ya dauka ba.
Ihun Umma Furera ne ya qara tunzura shi ya ji dama ace ya same ta tayi ihun da hujja.
Sajida ta zura da gudu ta shige dakinta da gudu ta sakale da şakata.
Malam na huci yana ta "har fitsarar taki ta dawo kaina ina fada kina fada saboda kin raina kowa. To wallahi ba'a gidana ba, inyi wahala dake tun da aka haifeki zuwa girma sannan kice ban isa in fada miki ki ji ba to sai dai idan ba'a karkashina kike ba ki tattara kayanki ki tafi kiyi zaman kanki tunda kina ganin ke kika haifi kanki, kin girma kinfi karfin kowa. Ni kuwa idan ni na haifeki kuma da sauran numfashina a duniya wallahi ba zaki auri Abdulmajid ba ko zaki mutu.
Ya juya ya dubi furera ya ce "ke ce uwar banza da ba kya tsawatarwa 'yarki.Banga amfanin zama da ke ba tunda ya'ya biyu kin kasa ba su tarbiyya da sun kai guda goma ma ban san tabarar da za'ayi min a gidan nan ba. To bari in fada miki zamanki a gidan nan ya kusa karewa, ke ki rasa aurenki itama ta rasa Abdul majid din kuyi biyu babu. Dan haka kisa ido, idan na sake jin maganar dan iskan yaron nan Abdulmajid a gidan nan zaku ga yadda zanyi muku.Sajida albishirinki a cikin satin nan zan yi miki miji ko kina so ko bakya so shi zaki aura kuma dole ki zauna, ba zaki sake yin wata guda a gidana ba insha Allah"
Ya kade babbar rigarsa ya fice yana huci ya bar umma furera a takure a lungu ta buga tagumi. Zuciyarta sai dukan uku-uku take saboda tashin hankali. Yayin da Sajida ta kwalla ihu ta fada kan katifa tana rusa kuka kamar ranta zai fita.
Umma furera tayi ta buga kofa tana magiya Sajida ta qi bude kofa. Sai da tayi kuka ta gaji da kanta sannan ta bude kofar. Umma furera ta shiga lallashinta akan ta daure ta ci abinci amma Sajida ta qi ci.Paid book #300