Sashe 55
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
LABARIN BAKURA
Ya ce "Sunana Muhammad, sunan kakana ne wanda ya haifi Babana aka saka min don haka ake kirana da Bakura wato Babban Baba. Ni haifaffen garin Mangono ne a cikin kasar Maiduguri. Sunan mahaifiyata wacce ta haife ni sunanta Fatukamba, Mahaifina kuwa Usman ana kiransa da Bawa. Na taso cikin matsananciyar rayuwa marar gata, kasancewar iyayena talakawa ne liqis, talaucin da har ma ya kai mu da yin bara, don haka iyayena almajirai ne masu bara da roqo.
Dadin dadawa mahaifiyata tana da larurar tabin hankali , mahaifina kuma makaho ne, wanda bai taba ganin hasken rana ba. Dama a haka suka hadu suka yi aure, suka haife ni."
Malam ya gyada kai ya ce "Allahu Akbar, Allah mai girma, tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai."
Samiia da 'ya'yanta suka bude baki su na mamakin abinda Bakura yake zanowa. Saboda bai taba basu irin wannan tarihin ba. Haka Sajida ta tsura ido ta na kallonsa zuciyarta cike da zulumi.
Iya Azumi (Innono) sai gyada kai take ta na cewa "Haka ne, duk an yi haka."
Bakura ya matse hawaye ya ce "Saboda tsantsar talaucinmu har ba mu da takamaiman gidan zama, a bakin bola a cikin kasuwa muke yini ni da mahaifiyata, mahaifina kuma a bakin tasha yake zama yana bara. Idan dare ya yi sai mu je bakin shagon kasuwa ko bakin tasha mu shimfida kwalaye mu kwanta, saboda an kore mu daga gidan haya. Hayar gidan kara dakin bukka ma talauci ya hana iyayena su biya kudin haya.
A lokacin duka-dukka shekarana uku kacal a duniya. Rigata daya ta wani yadi fari, saboda datti ya zama baqiqirin ko wando ba ni da shi, haka nake rayuwa. Bayan busasshiyar majina da hawaye a idanuwana sanoda ba a yi min wanke. Bakina kuwa dambar yake da busasshen koko, kamar yadda aka ba ni tarihi.
Ina cikin wannan hali na wahala da talauci, Allah (S.W.A) ya Jeho min mai agaza min, wacce ta zame min haske a lokacin duhu a cikin rayuwata, wacce ta kula da ni har na girma, wacce ta wanke min dattin da ya addabe ni, wacce ta kwantar da ni a daki na daina barcin bakin titi, wacce ta sadaukar da rayuwarta a kan ta ga na rayu. Ta saka ni a makarantar allo da boko, har na zama yadda nake a yanzu."
Sai Iya Azumi tą rushe da kuka kamar yadda Bakura ya fara kuka ya kasa ci gaba da magana. Kan ka ce kwabo idanuwan duk wanda yake wajen ya cika da hawaye, manyansu da yaransu.
Zahra ta sharbe hawaye ta ce "Wacece wannan Abba?"
Bakura ya ce "Wannan ita ce wacce nake baku labari, wato Zuhuriyya."
Malam ya ce "Oho, ita ce Zuhuriyyar da duk kadarorinka sunanta ne ka saka?"
Bakura ya gyada kai ya ce "Ita ce Zuhuriyya, yanzu za ku san kowace ce Zuhuriyya? Kuma me yasa nake ji da ita a rayuwata na kasa mantawa da ita."
Ya ce "Sunana Muhammad, sunan kakana ne wanda ya haifi Babana aka saka min don haka ake kirana da Bakura wato Babban Baba. Ni haifaffen garin Mangono ne a cikin kasar Maiduguri. Sunan mahaifiyata wacce ta haife ni sunanta Fatukamba, Mahaifina kuwa Usman ana kiransa da Bawa. Na taso cikin matsananciyar rayuwa marar gata, kasancewar iyayena talakawa ne liqis, talaucin da har ma ya kai mu da yin bara, don haka iyayena almajirai ne masu bara da roqo.
Dadin dadawa mahaifiyata tana da larurar tabin hankali , mahaifina kuma makaho ne, wanda bai taba ganin hasken rana ba. Dama a haka suka hadu suka yi aure, suka haife ni."
Malam ya gyada kai ya ce "Allahu Akbar, Allah mai girma, tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai."
Samiia da 'ya'yanta suka bude baki su na mamakin abinda Bakura yake zanowa. Saboda bai taba basu irin wannan tarihin ba. Haka Sajida ta tsura ido ta na kallonsa zuciyarta cike da zulumi.
Iya Azumi (Innono) sai gyada kai take ta na cewa "Haka ne, duk an yi haka."
Bakura ya matse hawaye ya ce "Saboda tsantsar talaucinmu har ba mu da takamaiman gidan zama, a bakin bola a cikin kasuwa muke yini ni da mahaifiyata, mahaifina kuma a bakin tasha yake zama yana bara. Idan dare ya yi sai mu je bakin shagon kasuwa ko bakin tasha mu shimfida kwalaye mu kwanta, saboda an kore mu daga gidan haya. Hayar gidan kara dakin bukka ma talauci ya hana iyayena su biya kudin haya.
A lokacin duka-dukka shekarana uku kacal a duniya. Rigata daya ta wani yadi fari, saboda datti ya zama baqiqirin ko wando ba ni da shi, haka nake rayuwa. Bayan busasshiyar majina da hawaye a idanuwana sanoda ba a yi min wanke. Bakina kuwa dambar yake da busasshen koko, kamar yadda aka ba ni tarihi.
Ina cikin wannan hali na wahala da talauci, Allah (S.W.A) ya Jeho min mai agaza min, wacce ta zame min haske a lokacin duhu a cikin rayuwata, wacce ta kula da ni har na girma, wacce ta wanke min dattin da ya addabe ni, wacce ta kwantar da ni a daki na daina barcin bakin titi, wacce ta sadaukar da rayuwarta a kan ta ga na rayu. Ta saka ni a makarantar allo da boko, har na zama yadda nake a yanzu."
Sai Iya Azumi tą rushe da kuka kamar yadda Bakura ya fara kuka ya kasa ci gaba da magana. Kan ka ce kwabo idanuwan duk wanda yake wajen ya cika da hawaye, manyansu da yaransu.
Zahra ta sharbe hawaye ta ce "Wacece wannan Abba?"
Bakura ya ce "Wannan ita ce wacce nake baku labari, wato Zuhuriyya."
Malam ya ce "Oho, ita ce Zuhuriyyar da duk kadarorinka sunanta ne ka saka?"
Bakura ya gyada kai ya ce "Ita ce Zuhuriyya, yanzu za ku san kowace ce Zuhuriyya? Kuma me yasa nake ji da ita a rayuwata na kasa mantawa da ita."