Sashe 35
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Malam ya yi zugum, can ya ce, "Bakura ina mafita? Ya ya zan yi da rayuwata? Yaya zan yi da Sajida? Muddin Sajida na zaune a gidana duk dabarata sai ta yi yadda zata hadu da Abdul majid, so yake ya cuci yarinyar nan ya bata mata rayuwa, Bakura babu amfanin zama da Sajida a gidana, tunda Sajida ba makaranta take yi ba. Ba na barcin kirki, saboda gadinta."
Bakura ya miqawa Malam kudin nan, gami da cewa, "Ka yi min izinin ganin Sajida zan yi mata magana."
Malam ya zabura ya miqe da sauri ya ce da Bakura, "Bismillah mu shiga ciki."
Malam na gaba Bakura na biye da shi, har tsakar gida. Bakura na tafe yana waiwaye, yana duban kowacce kusurwa ta cikin gidan. Babu abinda idanuwansa suke nuna masa, illa ragargajejjen bango da dakwalkwallallan fenti baqiqirin.
Su ka iske Umma Furera a zaune akan kujera a tsakar gida ta buga tagumi tana tunani, kallo daya za ka yi wa jemammun idanuwanta ka tabbatar ta narki kuka son ranta, har ta gaji.
Cikin nutsuwa da sanyin jiki Bakura ya yi mata sallama, gami da rusunawa don girmamawa. A tsorace ta dago ta dube shi, duba na ban mamaki. Ta sake wurga idonta gefe ta dubi maigidanta. Sai ta sadda kai qasa ta gyara lullubinta, gami da amsawa Bakura sallamar da ya yi mata.
Malam ya ce da ita. "Ki bawa baqo kujera mana ya zauna."
Ta yi sauri ta sauka daga kan kujerar da take zaune ta tura a gaban Bakura.
Ya ce, "A'a, babu komai yi zamanki ba zama zan yi ba."
Bakura ya durkusa a gaban Umma Furera ya gaishe ta, ta amsa cike da fara'a mai hade da mamaki, tana yi masa duba inin na ban gane ka ba.
Babu abin da Bakura yake nanatawa a ransa sai "Allahu Akbar, na ga mahaifin Sajida, na ga mahaifiyarta, ammá babu hadin ta da Zuhuriyyarta."
Bai ma taba cin karo da mai kama da siffar Umma Furera ba, balle su hada dangantaka da Zuhuriyya.
Kalmar da ta fara fitowa daga bakin Bakura ita ce "Ina Sajida?"
Wannan tambaya tasa ita tasa Umma Furera dago da jajayen idanuwanta, ta dube shi. Ta tambayi zuciyarta."Wanene wannan? Daga ina yake? Mene ne dalilin zuwansa? A ina ya san Sajida? Menene dalilinsa da yake neman Sajida?"
Furta wadannan tambayoyi ba za su yiwu ba dan haka ta hada tambayoyinta ta kunshe a cikin zuciyarta.
Malam ya nuna dakin Sajida ya ce "Ta na ciki, tana baqin ranta da ta saba. Mu shiga ka ganta."
Malam a gaba, Bakura na biye da shi, har qofar dakin Sajida. Abin ka da dogo, ga 'yar gajeriyar qofa a rashin sani bai durqusa ba ya doke kai a jikin qofa, yayin da burbushin jar qasa suka kado a jikin fararen kayansa, har da idanuwansa.
"Subhanallahi, sannu ka buge kai ko? Qofar ce irin tamu ta al'majirai." In ji Malam.
Bakura ya murza ido ya ce, "Ba komai, na manta ban durqusa ba, ka san tsawo gare ni kamar dare masha Allah."
Shigarsu cikin dakin ke da wuya Bakura ya yi ido hudu da wani gaftareren hoton Sajida (Lamination) a kafe a jikin bango. Ta kuwa tsala kyau, kai ka ce ba ita ba ce. Ta yi dariya a hoton, yayin da siririyar wushiryarta ta hadu da fararen hakoranta, suka hade da hasken kyamara suka bada wani haske. Duk wancan ganin da ya yi wa Sajida bai kare mata kallo ba ma ashe, a dalilin kukan da take yi, sai yanzu a hoto ya qare mata kallo.Tashin farko da ya dubi hoton, sai ya dafe kirji, saboda mummunar faduwar gaban daya riske shi, ya ce a ansa "Ianalillahi wa'inna ilaihir raju'un." Saboda tsantsar kamar da Sajida ta yi da Zuhuriyyarsa. Kamarsu ma har ta baci kamar an tsaga kara, in ji Bahaushe.
A ce har wushiryar cikin baki da jerin haqora iri daya, dariyarsu iri daya, har da lobawar kuncinsu iri daya (beautiful point) idan sun yi dariya. Kai wannan kama tasu ta yi yawa, in dai babu dangantaka. Kallon hoton Sajida kawai Bakura yake bai ma kula da Sajida ba, tana maqale kanta a cikin gwiwoyinta a lungu, ga sarka a daure a hannu da qafa, kamar wata 'yar fashi.
Malam ya kula Bakura fa bai ga Sajida ba, saboda dan akurkin dakin ya fara duhu, kasancewar yamma ta yi, sai ya ce da Bakura. "Ga ta can fa a takure a lungu."
Bakura ya juyo da sauri ya dubi lungun. Bai ci sa'a ba dan bata dago da kanta ta dube shi ba, kasancewar kukan da take shararawa, amma idonsa ya nuna masa kafafuwanta da hannayenta suma sak irin na Zuhuryya, don haka su ya tsaya yana duba kawai, ba tare da ya iya furta kalma daya ba, don kidimewa. Zuciyarsa ta shiga aikin tantance masa wannan abin al'ajabi, kwakwalwarsa ma wannan aikin ta shiga gaba daya jini da tsokar jikinsa suka canja, saboda rikcewa. Gumi take yi tun karfi, jayayya ake tsakanin huhunsa da numfashin da yake shiga da fitar iske saboda dimaucewa. Idanuwansa suka yi jawur, yayin da yawun bakinsa ya qafe, don haka ba shi da wata kalma da zai iya fadawa Sajida. Ya juya ya sake duban hoton Sajida, kamar ya kira sunan Zuhuriyýa ta amsa, sai ya ji kansa ya fara sarawa saboda tunani ya yi masa yawa. Ya yankewa kansa hukuncin ficewa daga dakin, kafin ya shide ya suma. Wannan al'amari ya fi qarfin ace sai ya nemo kwakwab gara ya barwa Allah ikonsa.
Malam ya yi tsaye yana jiran Bakura ya wanke masa Sajida tas, ya so Bakura ya turance masa ita, don ta san ba ita kadai ba ce 'yar boko. Malam ya so Bakura ya fito mata da dara-daran idanuwansa, kamar yadda yake ritsa 'yarsa Zahra, amma sai ya ga Bakura ya fice daga dakin da sauri ba tare da ya ce uffan ba.
Malam ma ya biyo shi suką fito tsakar gida Umma Furera ta fashe da kuka, ta durqusa gwiwoyinta guda biyu a qasa ta dubi Bakura.
Ta ce "Yaro, ka roqi Malam ya cirewa 'yar nan sarqa a qafa. Na dauka ma kwance ta za ku yi. Sajida ta qi ci, ta qi sha, tunda safe fa take daure."
Bakura ya ji hankalinsa ya dada tashi, ya yi sauri ya ce da Umma Furera.
"Tashi Iya, ki daina durkusa min, ni danki ne, za a kwance ta ki daina damuwa."
Ta koma ta zauna tana sharbe hawaye.
Bakura ya dubi Malam ya ce, "Baba, ka taimaka ka kwance ta, ba inda za je."
Malam ya bude baki zai yi magana Bakura ya dakatar da shi, ya ci gaba da cewa, "Ka bani wuqa, ka ba ni nama, a kan Sajida da Abdul majid."
Malam da matarsa suka yi sororo su na duban Bakura, duba na rashin fahimta. Bakura ya gyara tsayuwarsa, gami da duban qasa. Ya fada cikin wata murya mai dauke da tsananin kulawa, hade da tausayawa.
Ya ce, "Na yarda, na amince, zan aure ta, ni na fi cancanta in auri Sajida."
Malam ya ji tamkar an zuba masa wani ruwa mai sanyi a cikin zuciyarsa. Ya ji kamar an masa albishir da gidan Aljanna. Ya ji tamkar Allah Ya yi masa Albishir da aljanna, Ya gasgata Allah Ya amshi adduarsa Ya aiko masa da bawanSa dan da ya zo ya fitar da shi daga cikin wata gagarumar matsala da take so ta zama ajalinsa. Ya ji a jikinsa ya yi sallama da matsalar Sajida a duniya. Daga qarshe sai ya ji hawayen farin ciki ya fara kwarara.
Ya ce da Bakura, "Allah Ya yi maka albarka, Allah Ya tabbatar da wannan al'amari. Allah Ya sa an hada alhairi"
Umma Furera kuwa daga dukkan alamu ta shiga sarqaqiya, ta bude baki tana duban Bakura da Malam.
Can ta tambaya ta ce, "Malam wacce Sajidar ku ke magana?"
Malam ya tsuke fuska ya ce, "Sajida nawa gare mu? Ki na ganin Sama'ila zai iya da Sajida ko Abdul majid? Bakura sunansa wannan shine wanda ya kai mu Abuja muka yi masa aikin addu'a. Ya yarda ya amince zai auri Sajidą saboda ya taya mu kula da tarbiyarta."
Kafin Malam ya rufe baki, Umma Furera ta rusa kukan dadi, gami da jawo albarka iri-iri ga Bakura.
Bakura ya fice da sauri ba tare da ya ce komai ba. Malam ne ke biye da shi a baya har bakin motarsa suka yi sallama Bakura ya ja mota ya tafi.
Malam ya dawo cikin gida suka ci gaba da tattaunawa da Umma Furera, game da wannan abin farin ciki da ya same su. Malam da matarsa ne suka shiga dakin Sajida har yanzu ta qi dago da kanta, balle ta dubi masu shigowa. Malam ya tsugunna ya kwance sarkar da ya yi mata dabaibayi, ya ce da matarsa.
To ki yi mata bayani."
Ya fice ya bar su a dakin, kasancewar magruba ta qarato. Umma Furera ta matsa kusa da Sajida ta zauna gami da rungumo ta jikinta, ta dago kanta tana mai murmushi ta ce da Sajida.
"Albishirinki, aure ke da Sama'ila babu."
Wannan kalamai sun sa Sajida tattara hankalinta gaba daya ga sauraron mahaifiyarta. A wani bangare na zuciyarta kuwa, wani haske ne gami da farin ciki suka rufto mata.
Umma Furera ta ci gaba da cewa, "Bakon da ya shigo dazu ya ce shi zai tsaya miki mu ba shi wuqa, mu ba shi nama."
Sajida ta ji wani farin ciki ya lullube ta, ta zabura ta rungume mahaifyarta, ta fada cikin farin ciki.
"Mutumin ya roqi Baba ya bari in auri Abdul majid ne?"
Umma Furera ta yi 'dumm'! Can ta ce, "Ina wani sabon aminin Babanki, wanda kwanaki ya kai Babanku da su Abashe almajiri Abuja, mai arzikin nan da yake da kamfanoni, to shine ya shigo har cikin dakinki, shi ne yasa Malam ya kwance miki sarkar nan ya ce bai kamata a daure ki ba. Kuma na lure Malam ya na daukar shawararsa, duk da yaro ne ba sa'an Malam ba ne. Ga kudi, ga kyau, ga nutsuwa, mai ilimi dan boko."
Sajida ta yi ajiyar zuciya ta gyara zama ta ce, "To Umma me ya ce? Ya bawa Baba shawara ya kyale ni in auri Abdul majid ne?"
Umma Furera ta ce, "Sajida ki nutsu, kin san Abdul majid ba sonki yake ba, ba kuma aurarki zai yi ba. Amma wannan babba mutum ne ya san darajarki."
Sajida ta tsuke fuska ta ce "Ban fahimce ki ba, kamar yaya?"
Umma Furera ta yi murmushi ta shafa gefen fuskar Sajida da bayan hannunta ta ce. "Shi ya fi cancánta ya aure ki."
Sajida ta zabura ta miqe tsaye, kai ka ce cinnaka ne ya galla mata cizo, ko in ce kunama, don firgici. Ta daki wani tebur inda kayan kwalliyar da ke kan teburin suka watse kasa. Hawaye marar kakkautawa ya fara shatata daga idanuwanta.
Ta ce "WallahI ba zan aure shi ba, ko shi wanene. Haka ba zan auri Sama'ila ba, ko da kuwa za a kashe ni a gidan nan. Har a je a kirawo wani wanda ban sani ba, ban taba gani ba, a ce in aura, saboda an tsane ni."
Umma Furera ta ce, "Za ki gan shi zai zo, daga kin ganshi za ki so shi, har ya fi Abdul majid kyawun gani,"
Ho ho hoo! Tamkar Umma Furera ta zubawa zuciyar Sajida wuta, haka ta ji wani zazzafan baqin ciki. Ta kufula ta fice daga dakin ta fito tsakar gida tana huci, don takaici. Ji take tamkar ta hadiyi zuciya ta mutu, kar ta kai gobe.
Bakura ya miqawa Malam kudin nan, gami da cewa, "Ka yi min izinin ganin Sajida zan yi mata magana."
Malam ya zabura ya miqe da sauri ya ce da Bakura, "Bismillah mu shiga ciki."
Malam na gaba Bakura na biye da shi, har tsakar gida. Bakura na tafe yana waiwaye, yana duban kowacce kusurwa ta cikin gidan. Babu abinda idanuwansa suke nuna masa, illa ragargajejjen bango da dakwalkwallallan fenti baqiqirin.
Su ka iske Umma Furera a zaune akan kujera a tsakar gida ta buga tagumi tana tunani, kallo daya za ka yi wa jemammun idanuwanta ka tabbatar ta narki kuka son ranta, har ta gaji.
Cikin nutsuwa da sanyin jiki Bakura ya yi mata sallama, gami da rusunawa don girmamawa. A tsorace ta dago ta dube shi, duba na ban mamaki. Ta sake wurga idonta gefe ta dubi maigidanta. Sai ta sadda kai qasa ta gyara lullubinta, gami da amsawa Bakura sallamar da ya yi mata.
Malam ya ce da ita. "Ki bawa baqo kujera mana ya zauna."
Ta yi sauri ta sauka daga kan kujerar da take zaune ta tura a gaban Bakura.
Ya ce, "A'a, babu komai yi zamanki ba zama zan yi ba."
Bakura ya durkusa a gaban Umma Furera ya gaishe ta, ta amsa cike da fara'a mai hade da mamaki, tana yi masa duba inin na ban gane ka ba.
Babu abin da Bakura yake nanatawa a ransa sai "Allahu Akbar, na ga mahaifin Sajida, na ga mahaifiyarta, ammá babu hadin ta da Zuhuriyyarta."
Bai ma taba cin karo da mai kama da siffar Umma Furera ba, balle su hada dangantaka da Zuhuriyya.
Kalmar da ta fara fitowa daga bakin Bakura ita ce "Ina Sajida?"
Wannan tambaya tasa ita tasa Umma Furera dago da jajayen idanuwanta, ta dube shi. Ta tambayi zuciyarta."Wanene wannan? Daga ina yake? Mene ne dalilin zuwansa? A ina ya san Sajida? Menene dalilinsa da yake neman Sajida?"
Furta wadannan tambayoyi ba za su yiwu ba dan haka ta hada tambayoyinta ta kunshe a cikin zuciyarta.
Malam ya nuna dakin Sajida ya ce "Ta na ciki, tana baqin ranta da ta saba. Mu shiga ka ganta."
Malam a gaba, Bakura na biye da shi, har qofar dakin Sajida. Abin ka da dogo, ga 'yar gajeriyar qofa a rashin sani bai durqusa ba ya doke kai a jikin qofa, yayin da burbushin jar qasa suka kado a jikin fararen kayansa, har da idanuwansa.
"Subhanallahi, sannu ka buge kai ko? Qofar ce irin tamu ta al'majirai." In ji Malam.
Bakura ya murza ido ya ce, "Ba komai, na manta ban durqusa ba, ka san tsawo gare ni kamar dare masha Allah."
Shigarsu cikin dakin ke da wuya Bakura ya yi ido hudu da wani gaftareren hoton Sajida (Lamination) a kafe a jikin bango. Ta kuwa tsala kyau, kai ka ce ba ita ba ce. Ta yi dariya a hoton, yayin da siririyar wushiryarta ta hadu da fararen hakoranta, suka hade da hasken kyamara suka bada wani haske. Duk wancan ganin da ya yi wa Sajida bai kare mata kallo ba ma ashe, a dalilin kukan da take yi, sai yanzu a hoto ya qare mata kallo.Tashin farko da ya dubi hoton, sai ya dafe kirji, saboda mummunar faduwar gaban daya riske shi, ya ce a ansa "Ianalillahi wa'inna ilaihir raju'un." Saboda tsantsar kamar da Sajida ta yi da Zuhuriyyarsa. Kamarsu ma har ta baci kamar an tsaga kara, in ji Bahaushe.
A ce har wushiryar cikin baki da jerin haqora iri daya, dariyarsu iri daya, har da lobawar kuncinsu iri daya (beautiful point) idan sun yi dariya. Kai wannan kama tasu ta yi yawa, in dai babu dangantaka. Kallon hoton Sajida kawai Bakura yake bai ma kula da Sajida ba, tana maqale kanta a cikin gwiwoyinta a lungu, ga sarka a daure a hannu da qafa, kamar wata 'yar fashi.
Malam ya kula Bakura fa bai ga Sajida ba, saboda dan akurkin dakin ya fara duhu, kasancewar yamma ta yi, sai ya ce da Bakura. "Ga ta can fa a takure a lungu."
Bakura ya juyo da sauri ya dubi lungun. Bai ci sa'a ba dan bata dago da kanta ta dube shi ba, kasancewar kukan da take shararawa, amma idonsa ya nuna masa kafafuwanta da hannayenta suma sak irin na Zuhuryya, don haka su ya tsaya yana duba kawai, ba tare da ya iya furta kalma daya ba, don kidimewa. Zuciyarsa ta shiga aikin tantance masa wannan abin al'ajabi, kwakwalwarsa ma wannan aikin ta shiga gaba daya jini da tsokar jikinsa suka canja, saboda rikcewa. Gumi take yi tun karfi, jayayya ake tsakanin huhunsa da numfashin da yake shiga da fitar iske saboda dimaucewa. Idanuwansa suka yi jawur, yayin da yawun bakinsa ya qafe, don haka ba shi da wata kalma da zai iya fadawa Sajida. Ya juya ya sake duban hoton Sajida, kamar ya kira sunan Zuhuriyýa ta amsa, sai ya ji kansa ya fara sarawa saboda tunani ya yi masa yawa. Ya yankewa kansa hukuncin ficewa daga dakin, kafin ya shide ya suma. Wannan al'amari ya fi qarfin ace sai ya nemo kwakwab gara ya barwa Allah ikonsa.
Malam ya yi tsaye yana jiran Bakura ya wanke masa Sajida tas, ya so Bakura ya turance masa ita, don ta san ba ita kadai ba ce 'yar boko. Malam ya so Bakura ya fito mata da dara-daran idanuwansa, kamar yadda yake ritsa 'yarsa Zahra, amma sai ya ga Bakura ya fice daga dakin da sauri ba tare da ya ce uffan ba.
Malam ma ya biyo shi suką fito tsakar gida Umma Furera ta fashe da kuka, ta durqusa gwiwoyinta guda biyu a qasa ta dubi Bakura.
Ta ce "Yaro, ka roqi Malam ya cirewa 'yar nan sarqa a qafa. Na dauka ma kwance ta za ku yi. Sajida ta qi ci, ta qi sha, tunda safe fa take daure."
Bakura ya ji hankalinsa ya dada tashi, ya yi sauri ya ce da Umma Furera.
"Tashi Iya, ki daina durkusa min, ni danki ne, za a kwance ta ki daina damuwa."
Ta koma ta zauna tana sharbe hawaye.
Bakura ya dubi Malam ya ce, "Baba, ka taimaka ka kwance ta, ba inda za je."
Malam ya bude baki zai yi magana Bakura ya dakatar da shi, ya ci gaba da cewa, "Ka bani wuqa, ka ba ni nama, a kan Sajida da Abdul majid."
Malam da matarsa suka yi sororo su na duban Bakura, duba na rashin fahimta. Bakura ya gyara tsayuwarsa, gami da duban qasa. Ya fada cikin wata murya mai dauke da tsananin kulawa, hade da tausayawa.
Ya ce, "Na yarda, na amince, zan aure ta, ni na fi cancanta in auri Sajida."
Malam ya ji tamkar an zuba masa wani ruwa mai sanyi a cikin zuciyarsa. Ya ji kamar an masa albishir da gidan Aljanna. Ya ji tamkar Allah Ya yi masa Albishir da aljanna, Ya gasgata Allah Ya amshi adduarsa Ya aiko masa da bawanSa dan da ya zo ya fitar da shi daga cikin wata gagarumar matsala da take so ta zama ajalinsa. Ya ji a jikinsa ya yi sallama da matsalar Sajida a duniya. Daga qarshe sai ya ji hawayen farin ciki ya fara kwarara.
Ya ce da Bakura, "Allah Ya yi maka albarka, Allah Ya tabbatar da wannan al'amari. Allah Ya sa an hada alhairi"
Umma Furera kuwa daga dukkan alamu ta shiga sarqaqiya, ta bude baki tana duban Bakura da Malam.
Can ta tambaya ta ce, "Malam wacce Sajidar ku ke magana?"
Malam ya tsuke fuska ya ce, "Sajida nawa gare mu? Ki na ganin Sama'ila zai iya da Sajida ko Abdul majid? Bakura sunansa wannan shine wanda ya kai mu Abuja muka yi masa aikin addu'a. Ya yarda ya amince zai auri Sajidą saboda ya taya mu kula da tarbiyarta."
Kafin Malam ya rufe baki, Umma Furera ta rusa kukan dadi, gami da jawo albarka iri-iri ga Bakura.
Bakura ya fice da sauri ba tare da ya ce komai ba. Malam ne ke biye da shi a baya har bakin motarsa suka yi sallama Bakura ya ja mota ya tafi.
Malam ya dawo cikin gida suka ci gaba da tattaunawa da Umma Furera, game da wannan abin farin ciki da ya same su. Malam da matarsa ne suka shiga dakin Sajida har yanzu ta qi dago da kanta, balle ta dubi masu shigowa. Malam ya tsugunna ya kwance sarkar da ya yi mata dabaibayi, ya ce da matarsa.
To ki yi mata bayani."
Ya fice ya bar su a dakin, kasancewar magruba ta qarato. Umma Furera ta matsa kusa da Sajida ta zauna gami da rungumo ta jikinta, ta dago kanta tana mai murmushi ta ce da Sajida.
"Albishirinki, aure ke da Sama'ila babu."
Wannan kalamai sun sa Sajida tattara hankalinta gaba daya ga sauraron mahaifiyarta. A wani bangare na zuciyarta kuwa, wani haske ne gami da farin ciki suka rufto mata.
Umma Furera ta ci gaba da cewa, "Bakon da ya shigo dazu ya ce shi zai tsaya miki mu ba shi wuqa, mu ba shi nama."
Sajida ta ji wani farin ciki ya lullube ta, ta zabura ta rungume mahaifyarta, ta fada cikin farin ciki.
"Mutumin ya roqi Baba ya bari in auri Abdul majid ne?"
Umma Furera ta yi 'dumm'! Can ta ce, "Ina wani sabon aminin Babanki, wanda kwanaki ya kai Babanku da su Abashe almajiri Abuja, mai arzikin nan da yake da kamfanoni, to shine ya shigo har cikin dakinki, shi ne yasa Malam ya kwance miki sarkar nan ya ce bai kamata a daure ki ba. Kuma na lure Malam ya na daukar shawararsa, duk da yaro ne ba sa'an Malam ba ne. Ga kudi, ga kyau, ga nutsuwa, mai ilimi dan boko."
Sajida ta yi ajiyar zuciya ta gyara zama ta ce, "To Umma me ya ce? Ya bawa Baba shawara ya kyale ni in auri Abdul majid ne?"
Umma Furera ta ce, "Sajida ki nutsu, kin san Abdul majid ba sonki yake ba, ba kuma aurarki zai yi ba. Amma wannan babba mutum ne ya san darajarki."
Sajida ta tsuke fuska ta ce "Ban fahimce ki ba, kamar yaya?"
Umma Furera ta yi murmushi ta shafa gefen fuskar Sajida da bayan hannunta ta ce. "Shi ya fi cancánta ya aure ki."
Sajida ta zabura ta miqe tsaye, kai ka ce cinnaka ne ya galla mata cizo, ko in ce kunama, don firgici. Ta daki wani tebur inda kayan kwalliyar da ke kan teburin suka watse kasa. Hawaye marar kakkautawa ya fara shatata daga idanuwanta.
Ta ce "WallahI ba zan aure shi ba, ko shi wanene. Haka ba zan auri Sama'ila ba, ko da kuwa za a kashe ni a gidan nan. Har a je a kirawo wani wanda ban sani ba, ban taba gani ba, a ce in aura, saboda an tsane ni."
Umma Furera ta ce, "Za ki gan shi zai zo, daga kin ganshi za ki so shi, har ya fi Abdul majid kyawun gani,"
Ho ho hoo! Tamkar Umma Furera ta zubawa zuciyar Sajida wuta, haka ta ji wani zazzafan baqin ciki. Ta kufula ta fice daga dakin ta fito tsakar gida tana huci, don takaici. Ji take tamkar ta hadiyi zuciya ta mutu, kar ta kai gobe.