Sashe 37
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
Kwanakin Bakura uku a cikin gida baya fita ko qofar gida, yana nan yana gadin Samira. Ta tubure, ita sai ta fita an neme ta an rasa. Bakura ya damu, ya rasa yadda zai yi ya shawo kan wannan matsalar, daga qarshe ya buga waya ya sanarwa da babbar yayar Samira, mai suna Hajja Farida, da ke zaune da maigidanta a unguwar Janbulo. Ko awa guda ba ta yi ba ta diro cikin gidan su Bakura. Aka zauna ga Samira, ga Bakura, ga Hajjiya Farida aka mayar da magana. A tunanin Samira yayarta za ta bi bayanta, sai ta ji yayar ta bi bayan Bakura, har take yi mata fada cewar shashanci ne wannan. Ta nuna mata qara aure ga namiji ba wani abu ba ne, domin ita ma kishiyoyinta biyu, ita ce ta uku, kuma ita ce uwargida. Da yake 'yar kasuwa ce qasashe take zuwa tana kawo kaya, sai ta ce da Bakura ya ba ta kwangila ma ta hado masa lefen amarya da uwargida.
Cikin farin ciki Bakura ya amsa mata cewa. "ki yi min lissafin duk abinda ya kamata a saya musu, zan zo har gida mu zauna."
Wani kullutun bakin ciki ne ya kakare a wuyan Samira a halin yanzu ta fi jin haushin yayarta Hajjiya Farida a kan Bakura ma. Bakura ya yi wa Farida sallama ya dauki mukullin motarsa ya fice don ya ba su waje, ya san Farida za ta taimaka masa wajen bawa matarsa shawara mai kyau, dadin dadawa kuma Samira na matuqar jin tsoron Hajja Farida, kasancewar ita ce babba a dakinsu, ga ta mafadaciya ce, kuma mai kudi ce.
Bakura ya bude mota ya shiga ya zauna kenan, kafin ya jawo qofa ya rufe sai ya ji muryar Zahra. Ya yi sauri ya waiga, sai ya ga Zahra a durqushe jikinta a sanyaye kamar marar lafiya.
Cikin harshen turanci take magana ta fara da tambaya. Ta ce, "Abba, me yake faruwa ne tsakaninka da Mamanmu kwana biyu take kuka?"
Bakura ya rasa amsar da zai ba ta. Kafin ya gama kame-kamensa Zahra ta qara da cewa.
"Yanzu kuma da Hajjiya Farida ta zo Abubakar ya ce min yaji ana cewa za ka qara aure. Haka ne?"
Bakura ya gyada kai cikin sanyin jiki ya ce, "Haka ne Mamana."
Hawaye ya cika mata ido, sai ta yunqura ta miqe ta ce "Allah ya sanya alkhairi,"
Bakura ya ce da ita, "Zo nan, kin san wacce zan aura ne?"
Zahra ta girgiza kai alamar a'a.
Ya ce, "Yagana, ki yi hakuri da abinda zan fada miki, na san ba zai yi miki dadi ba. Kada ki girgiza, kada ki ga laifina ina da dalilin yin haka, wanda ba za ki gane ba sai nan gaba."
Zahra ta sharbe hawaye ta girgiza kai ta ce, "Ba zan damu ba Abba kowace ce.
Ya yi huci, wanda ya fitar da iska mai zafi ya ce, "Sajida zan aura."
Zahra da ke durkushe sai ta fadi zaune tubus. Can ta fara jan jiki kamar yaron da yake koyar rarrafe. Kafin mahaifinta ya ce wani abu Zahra ta fashe da kuka, ta miqe ta runtuma cikin gida da gudu. Ba ta tsaya a ko ina ba sai cikin đakinta, ta rufe kanta don takaici. Fiye da minti talatin Bakura na zaune a cikin mota ya kasa kunna motar ya tafi, saboda damuwa. Ya rasa madafa, ya rasa yadda zai yi da rayuwarsa. Hakika Bakura ya shiga tsaka-mai-wuya.
Namijin duniya da ya fita daga gidansa gidan su Sajida ya nufu, ita kuma ya je ya ga wanne gumurzun za a yi. Faduwar gaba asarar namiji, amma ya san za a yi gagarumar rigima da fetsararriyar yarinyar nan musamman idan suka hadu ta ganshi, mutumin da ya raba ta da rabin ranta Abdul majid kuma yanzu ya zo ya ce zai aure ta.
A kofar gida ya iske Malam, bayan sun gaisa, sun taba 'yar hira.
Malam ya dubi Bakura ya yi murmushi, ya ce, "Ka bar mu da rigima, Sajida tana da taurin kai, har yau ba ta haqura da yaron nan ba. Inda muka sami sauqin abun da muka ce mata kai dan
sanda ne, tuni kasa an kama Abdul majid an daure shi har sai ta daina tunanin guduwa wajensa sannan za' a sako shi. Ka san yaran yanzu marassa kunya, kullum roqar uwar take wai a ba ka hakuri ka sake shi ba za ta gudu ba."
Bakura ya yi dariya ya ce, "Allah Ya kyauta, ai mata kwakwalwarsu qarama ce, tunaninsu gajere ne. Nima kwanaki ukun nan ina gida muna gumurzu da uwargidana na sanar mata zan yi aure. Amma yanzu Alhamdulillahi rigimar ta lafa, shi yasa ma na samu na fito. Ai mata ba sa son kishiya."
Dadi ya rufe Malam ya ce, "Ikon Allah, har ka sanarwa uwargida, amma wannan abu ya yi min dadi. Nima a nan ni da almajiraina kullum sai mun yi saukar Kur'ani daya, an yi sadaka akan Allah Ya tabbatar da wannan abu, ya kawar da duk wasu fitintinu."
Bakura ya ce, "Amin Malam, ai kamata ya yi a dinga yin saukar nan sau uku a rana daya, zan dinga biyan masu karatun a qaro Malamai, domin abubuwan da yawa. Ka ga har yanzu Sajida ba ta san ko ni wanene ba, don ba ta daga ido ta ganni ba."
Malam ya ce, "Kar ka damu ta fara laushi, jikinta ya yi sanyi kamar ta saduda, saboda Furera tana ba ta baki kullum ba dare ba rana. Sama'ila ma na kira shi na ba shi haklquri, na nuna masa illar da na hango masa idan aka yi wa Sajida tilas ta aure shi. Yaron mai hankali ne bai damu ba, kuma ya fahimce ni. Mu shiga ciki ku gaisa da Sajidar mana."
Bakura ya zabura ya ce,
"Ah! Haba ai ba komai ba sai mun gaisa ba, idan aka yi auren ta ganni."
Malam ya yi dariya ya ce, "Haba, haba kamar a mutanen da, ai gara ku dinga gaisawa, ku san juna kafin lokacin, bari in turo ta ko a zaure ne ku tsaya ku gaisa."
Malam ya shiga cikin gida da sauri, yayin da Bakura ya je zaure ya tsaya, sai kai kawo yake daga wannan bango zuwa wancan, zuciyarsa cike da zullumi da fargabar abinda zai je ya zo. Kamar an wurgo ta haka ya ganta 'dif a gabansa sanye da wani zunbulelen hijabi ruwan toka. Ya ji gabansa ya yanke ya fadi, domin ganinta ya sake tono masa zafin rabuwa da mai kama da ita wato Zuhuriyyarsa. Kallon-kallo ake tsakanin Bakura da Sajida. Kallo irin na qeqe-da- qeqe, ido cikin ido ba tare da daya ya rusuna idonsa ba. Kowannensu ya na nasa tunanin a ransa. Shi al'ajabi yake yadda kamannin Sajida da Zuhuriyya suka zama daya. Ita kuwa kallo daya da ta yi masa ta tuno inda ta taba sanin fuskarsa. Tabbas wannan shi ne mutumin da ya taba musgunawa rayuwarta. Wannan shi ne mutumin da ta ji ta tsana a cikin qanqanin lokaci a ranar da ta fara ganinsa a rayuwarta. Nan da nan kwakwalwarta ta tuno mata da kamannin Zahra, ta hada fuskokinsu ta tabbatar kamanninsu daya. Ta sake tuno kalmar da ya fada mata cewar yana da 'yarsa sa'arta Zahra, wacce yake kwatanta ta da ita ce kwaryarsa ta gari da ya saqale ta a ragaya. Lallai akwai wani tuggu da mutumin nan ya hado mata na ya raba ta da abun qaunarta don shi ya aure ta.
Sajida ta fada a ranta, "Sai dai a kai gawata ta zauna da wannan amma ba ni ba."
Bakura ne ya katse tunaninta ya ce, "Assalamu alaikum warahamatul lahi ta'ala wa barakatuh. Sajida mun hadu a kashi na biyu, sai dai wannan haduwar tamu ta sha bamban da ta farko. Sajida, da kin san irin girma da darajar wacce kike yi min kama da ita da baki shiga damuwa ba. Ba zan iya wulakanta ki ba, ba zan iya cutar da ke ba.."
Bai rufe bakinsa ba ta daka masa wata tsawa mai tsoratarwa, ta ce, "dakata Malam, rufe min baki, yi min shiru."
Dariya ce ta subuce masa, domin ya tuna
wasansu da Zuhuriyya, tabbas muryarsu da yanayin maganar Sajida da Zuhuriyya iri daya ce. Haka sak wannan kalmar Zuhuriyya take furtawa.
Dariyarsa ta sake hargitsawa Sajida fushinta, ta dada 6ata rai ta ce,
"Ka yi dariya mana tunda ka hada min tuggu, Zahra 'yarka ce ashe ka kawo ta ta shigo gidanmu ta ga abinda nake, don ku raba ni da Abdul dina, kai ka aure ni, to bari ka ji in fada maka da in aure ka gara in halaka kaina, kamar yadda Abdul majid ya rasa ni, kai ma ba za ka same ni ba Kada ka manta tun ranar da na fara haduwa da kai na ji na tsane ka, yanzu na qara tsanarka, kuma na tsani 'yar ka Zahra."
Kallonta kawai ya tsaya yana yi, tsiwa take yi tana murguda baki, ta gama cashe masa ta Juya ta shiga gida. Ya bi ta da kallo har da leqe. Ya fito jikin motarsa ya tsaya ya yi shiru, tamkar gunki. Ba baqaqen maganganun da ta fada masa ba ne suke yi masa reto a zuciya ba, a'a tsantsar kamar ta da Zuhuriyyarsa ce mamaki ya sake damqarsa.
Sajida na shiga tsakar gidansu ta yaye hijabi ta yi zaman 'yan bori 'dabas' ta rafsa wani uban ihu kamar wacce ake cirewa rai.
Ta ce, "Wallahi ba zan auri wannan mutumin ba gara in auri kuturu ko makahon da yake bara a titi."
Malam ya fito daga bandaki ya dire buta da sauri, yayin da matarsa ta fito daga daki a guje suka rintimo wajen Sajida suna tambayarta. "Lafiya? Me ya yi miki mutumin? Daman kin san shi?"
Cikin kuka ta ce,
"Shi ne Baban Zahrar nan da take hada min gulma. Ashe shi ne ya aiko ta, don a raba ni da Abdulmajid. To gara in auri kowa da in aure shi."
Umma Furera ta ce, "Ya aka yi ki ka san shi ne, wannan waçce irin magana ki ke yi?"
Malam ya ja dogon tsaki ya ce, "Ai kin aure shi kin gama da izinin Ubangiji, zancen banza. Har kin isa ma ki zabi abinda kike so? Ai mutunci da lallashi a tsakanina da ke ya wuce."
Ya fice ya bar Umma Furera riqe da Sajida. Da alama
Umma Furera ta shiga tabarbarewar tunani ta rasa kan zancen. Tana zanowa kanta tambayoyi. "A ina Sajida ta san wannan mutumin? Ya aka yi ta san mahaifin Zahra ne?"
Malam ya qaraso wajen motar Bakura, Bakura ya yi sauri ya saki ransa ya hau murmushin qarfin hali.
Ya ce da Malam, "Zan koma gida sai gobe idan Allah Ya kai mu."
Malam ya ce "Kun gaisa da Sajida ko? Bakura sai haquri fa, ka qara hakuri da Sajida."
Bakura ya katse Malam da cewa, "Kai haba, ai ba komai yarinta ke damun Sajida."
Malam ya ce, "Har ina tunanin in ce maka kar ka dauki fasagurbin kwai ka hada shi da kwayayenka masu kyau. Ma'ana kada ka dauki Sajida ka kai gidanka ta 6ata maka tsarin gida. Ni da Allah Ya bawa in ci gaba da hakurin zama da ita."
Bakura ya yi sauri ya ce da Malam "Ka daina fadar haka, haba Malam wadannan kalamai su daina fitowa daga bakinka a kan Sajida saboda karfin bakin iyaye a kan 'ya'yansu agar ka dinga furta alkhairi. Halin da Sajida ke ciki ba wani abu ba ne na daban, a kowanne gida yana faruwa. Bai kamata ka dauki Sajida kangararriya, ta gagari jama'a ba, har ana daure ta a sarka. Ka ci gaba da ba ta baki ku lallashe ta,a qarshe ku yi tayi mata addu'a."
A haka dai suka rabu da Malam, Bakura ya nufi gida. Gidan Bakura tamkar ana zaman makoki. Samira da 'ya'yan jugum-jugum, haka Bakura ya samu waje ya zauna ya yi jugum. Duk da ya na daurewa yana jan su da hira, amma shi ma hirar bata kai har zuciya ba, saboda tashin hankalin da yake ciki ta bangarori guda biyu, ko ina ba dadi. Sai ya ji a zuciyarsa kamar ya fasa auren kasancewar damuwar da iyalansa suke ciki, sai ya tuno kamannin Sajida da Zuhuriyya, sai ya ji ba zai iya fasa aurenta ba, komai runtsi.
Cikin farin ciki Bakura ya amsa mata cewa. "ki yi min lissafin duk abinda ya kamata a saya musu, zan zo har gida mu zauna."
Wani kullutun bakin ciki ne ya kakare a wuyan Samira a halin yanzu ta fi jin haushin yayarta Hajjiya Farida a kan Bakura ma. Bakura ya yi wa Farida sallama ya dauki mukullin motarsa ya fice don ya ba su waje, ya san Farida za ta taimaka masa wajen bawa matarsa shawara mai kyau, dadin dadawa kuma Samira na matuqar jin tsoron Hajja Farida, kasancewar ita ce babba a dakinsu, ga ta mafadaciya ce, kuma mai kudi ce.
Bakura ya bude mota ya shiga ya zauna kenan, kafin ya jawo qofa ya rufe sai ya ji muryar Zahra. Ya yi sauri ya waiga, sai ya ga Zahra a durqushe jikinta a sanyaye kamar marar lafiya.
Cikin harshen turanci take magana ta fara da tambaya. Ta ce, "Abba, me yake faruwa ne tsakaninka da Mamanmu kwana biyu take kuka?"
Bakura ya rasa amsar da zai ba ta. Kafin ya gama kame-kamensa Zahra ta qara da cewa.
"Yanzu kuma da Hajjiya Farida ta zo Abubakar ya ce min yaji ana cewa za ka qara aure. Haka ne?"
Bakura ya gyada kai cikin sanyin jiki ya ce, "Haka ne Mamana."
Hawaye ya cika mata ido, sai ta yunqura ta miqe ta ce "Allah ya sanya alkhairi,"
Bakura ya ce da ita, "Zo nan, kin san wacce zan aura ne?"
Zahra ta girgiza kai alamar a'a.
Ya ce, "Yagana, ki yi hakuri da abinda zan fada miki, na san ba zai yi miki dadi ba. Kada ki girgiza, kada ki ga laifina ina da dalilin yin haka, wanda ba za ki gane ba sai nan gaba."
Zahra ta sharbe hawaye ta girgiza kai ta ce, "Ba zan damu ba Abba kowace ce.
Ya yi huci, wanda ya fitar da iska mai zafi ya ce, "Sajida zan aura."
Zahra da ke durkushe sai ta fadi zaune tubus. Can ta fara jan jiki kamar yaron da yake koyar rarrafe. Kafin mahaifinta ya ce wani abu Zahra ta fashe da kuka, ta miqe ta runtuma cikin gida da gudu. Ba ta tsaya a ko ina ba sai cikin đakinta, ta rufe kanta don takaici. Fiye da minti talatin Bakura na zaune a cikin mota ya kasa kunna motar ya tafi, saboda damuwa. Ya rasa madafa, ya rasa yadda zai yi da rayuwarsa. Hakika Bakura ya shiga tsaka-mai-wuya.
Namijin duniya da ya fita daga gidansa gidan su Sajida ya nufu, ita kuma ya je ya ga wanne gumurzun za a yi. Faduwar gaba asarar namiji, amma ya san za a yi gagarumar rigima da fetsararriyar yarinyar nan musamman idan suka hadu ta ganshi, mutumin da ya raba ta da rabin ranta Abdul majid kuma yanzu ya zo ya ce zai aure ta.
A kofar gida ya iske Malam, bayan sun gaisa, sun taba 'yar hira.
Malam ya dubi Bakura ya yi murmushi, ya ce, "Ka bar mu da rigima, Sajida tana da taurin kai, har yau ba ta haqura da yaron nan ba. Inda muka sami sauqin abun da muka ce mata kai dan
sanda ne, tuni kasa an kama Abdul majid an daure shi har sai ta daina tunanin guduwa wajensa sannan za' a sako shi. Ka san yaran yanzu marassa kunya, kullum roqar uwar take wai a ba ka hakuri ka sake shi ba za ta gudu ba."
Bakura ya yi dariya ya ce, "Allah Ya kyauta, ai mata kwakwalwarsu qarama ce, tunaninsu gajere ne. Nima kwanaki ukun nan ina gida muna gumurzu da uwargidana na sanar mata zan yi aure. Amma yanzu Alhamdulillahi rigimar ta lafa, shi yasa ma na samu na fito. Ai mata ba sa son kishiya."
Dadi ya rufe Malam ya ce, "Ikon Allah, har ka sanarwa uwargida, amma wannan abu ya yi min dadi. Nima a nan ni da almajiraina kullum sai mun yi saukar Kur'ani daya, an yi sadaka akan Allah Ya tabbatar da wannan abu, ya kawar da duk wasu fitintinu."
Bakura ya ce, "Amin Malam, ai kamata ya yi a dinga yin saukar nan sau uku a rana daya, zan dinga biyan masu karatun a qaro Malamai, domin abubuwan da yawa. Ka ga har yanzu Sajida ba ta san ko ni wanene ba, don ba ta daga ido ta ganni ba."
Malam ya ce, "Kar ka damu ta fara laushi, jikinta ya yi sanyi kamar ta saduda, saboda Furera tana ba ta baki kullum ba dare ba rana. Sama'ila ma na kira shi na ba shi haklquri, na nuna masa illar da na hango masa idan aka yi wa Sajida tilas ta aure shi. Yaron mai hankali ne bai damu ba, kuma ya fahimce ni. Mu shiga ciki ku gaisa da Sajidar mana."
Bakura ya zabura ya ce,
"Ah! Haba ai ba komai ba sai mun gaisa ba, idan aka yi auren ta ganni."
Malam ya yi dariya ya ce, "Haba, haba kamar a mutanen da, ai gara ku dinga gaisawa, ku san juna kafin lokacin, bari in turo ta ko a zaure ne ku tsaya ku gaisa."
Malam ya shiga cikin gida da sauri, yayin da Bakura ya je zaure ya tsaya, sai kai kawo yake daga wannan bango zuwa wancan, zuciyarsa cike da zullumi da fargabar abinda zai je ya zo. Kamar an wurgo ta haka ya ganta 'dif a gabansa sanye da wani zunbulelen hijabi ruwan toka. Ya ji gabansa ya yanke ya fadi, domin ganinta ya sake tono masa zafin rabuwa da mai kama da ita wato Zuhuriyyarsa. Kallon-kallo ake tsakanin Bakura da Sajida. Kallo irin na qeqe-da- qeqe, ido cikin ido ba tare da daya ya rusuna idonsa ba. Kowannensu ya na nasa tunanin a ransa. Shi al'ajabi yake yadda kamannin Sajida da Zuhuriyya suka zama daya. Ita kuwa kallo daya da ta yi masa ta tuno inda ta taba sanin fuskarsa. Tabbas wannan shi ne mutumin da ya taba musgunawa rayuwarta. Wannan shi ne mutumin da ta ji ta tsana a cikin qanqanin lokaci a ranar da ta fara ganinsa a rayuwarta. Nan da nan kwakwalwarta ta tuno mata da kamannin Zahra, ta hada fuskokinsu ta tabbatar kamanninsu daya. Ta sake tuno kalmar da ya fada mata cewar yana da 'yarsa sa'arta Zahra, wacce yake kwatanta ta da ita ce kwaryarsa ta gari da ya saqale ta a ragaya. Lallai akwai wani tuggu da mutumin nan ya hado mata na ya raba ta da abun qaunarta don shi ya aure ta.
Sajida ta fada a ranta, "Sai dai a kai gawata ta zauna da wannan amma ba ni ba."
Bakura ne ya katse tunaninta ya ce, "Assalamu alaikum warahamatul lahi ta'ala wa barakatuh. Sajida mun hadu a kashi na biyu, sai dai wannan haduwar tamu ta sha bamban da ta farko. Sajida, da kin san irin girma da darajar wacce kike yi min kama da ita da baki shiga damuwa ba. Ba zan iya wulakanta ki ba, ba zan iya cutar da ke ba.."
Bai rufe bakinsa ba ta daka masa wata tsawa mai tsoratarwa, ta ce, "dakata Malam, rufe min baki, yi min shiru."
Dariya ce ta subuce masa, domin ya tuna
wasansu da Zuhuriyya, tabbas muryarsu da yanayin maganar Sajida da Zuhuriyya iri daya ce. Haka sak wannan kalmar Zuhuriyya take furtawa.
Dariyarsa ta sake hargitsawa Sajida fushinta, ta dada 6ata rai ta ce,
"Ka yi dariya mana tunda ka hada min tuggu, Zahra 'yarka ce ashe ka kawo ta ta shigo gidanmu ta ga abinda nake, don ku raba ni da Abdul dina, kai ka aure ni, to bari ka ji in fada maka da in aure ka gara in halaka kaina, kamar yadda Abdul majid ya rasa ni, kai ma ba za ka same ni ba Kada ka manta tun ranar da na fara haduwa da kai na ji na tsane ka, yanzu na qara tsanarka, kuma na tsani 'yar ka Zahra."
Kallonta kawai ya tsaya yana yi, tsiwa take yi tana murguda baki, ta gama cashe masa ta Juya ta shiga gida. Ya bi ta da kallo har da leqe. Ya fito jikin motarsa ya tsaya ya yi shiru, tamkar gunki. Ba baqaqen maganganun da ta fada masa ba ne suke yi masa reto a zuciya ba, a'a tsantsar kamar ta da Zuhuriyyarsa ce mamaki ya sake damqarsa.
Sajida na shiga tsakar gidansu ta yaye hijabi ta yi zaman 'yan bori 'dabas' ta rafsa wani uban ihu kamar wacce ake cirewa rai.
Ta ce, "Wallahi ba zan auri wannan mutumin ba gara in auri kuturu ko makahon da yake bara a titi."
Malam ya fito daga bandaki ya dire buta da sauri, yayin da matarsa ta fito daga daki a guje suka rintimo wajen Sajida suna tambayarta. "Lafiya? Me ya yi miki mutumin? Daman kin san shi?"
Cikin kuka ta ce,
"Shi ne Baban Zahrar nan da take hada min gulma. Ashe shi ne ya aiko ta, don a raba ni da Abdulmajid. To gara in auri kowa da in aure shi."
Umma Furera ta ce, "Ya aka yi ki ka san shi ne, wannan waçce irin magana ki ke yi?"
Malam ya ja dogon tsaki ya ce, "Ai kin aure shi kin gama da izinin Ubangiji, zancen banza. Har kin isa ma ki zabi abinda kike so? Ai mutunci da lallashi a tsakanina da ke ya wuce."
Ya fice ya bar Umma Furera riqe da Sajida. Da alama
Umma Furera ta shiga tabarbarewar tunani ta rasa kan zancen. Tana zanowa kanta tambayoyi. "A ina Sajida ta san wannan mutumin? Ya aka yi ta san mahaifin Zahra ne?"
Malam ya qaraso wajen motar Bakura, Bakura ya yi sauri ya saki ransa ya hau murmushin qarfin hali.
Ya ce da Malam, "Zan koma gida sai gobe idan Allah Ya kai mu."
Malam ya ce "Kun gaisa da Sajida ko? Bakura sai haquri fa, ka qara hakuri da Sajida."
Bakura ya katse Malam da cewa, "Kai haba, ai ba komai yarinta ke damun Sajida."
Malam ya ce, "Har ina tunanin in ce maka kar ka dauki fasagurbin kwai ka hada shi da kwayayenka masu kyau. Ma'ana kada ka dauki Sajida ka kai gidanka ta 6ata maka tsarin gida. Ni da Allah Ya bawa in ci gaba da hakurin zama da ita."
Bakura ya yi sauri ya ce da Malam "Ka daina fadar haka, haba Malam wadannan kalamai su daina fitowa daga bakinka a kan Sajida saboda karfin bakin iyaye a kan 'ya'yansu agar ka dinga furta alkhairi. Halin da Sajida ke ciki ba wani abu ba ne na daban, a kowanne gida yana faruwa. Bai kamata ka dauki Sajida kangararriya, ta gagari jama'a ba, har ana daure ta a sarka. Ka ci gaba da ba ta baki ku lallashe ta,a qarshe ku yi tayi mata addu'a."
A haka dai suka rabu da Malam, Bakura ya nufi gida. Gidan Bakura tamkar ana zaman makoki. Samira da 'ya'yan jugum-jugum, haka Bakura ya samu waje ya zauna ya yi jugum. Duk da ya na daurewa yana jan su da hira, amma shi ma hirar bata kai har zuciya ba, saboda tashin hankalin da yake ciki ta bangarori guda biyu, ko ina ba dadi. Sai ya ji a zuciyarsa kamar ya fasa auren kasancewar damuwar da iyalansa suke ciki, sai ya tuno kamannin Sajida da Zuhuriyya, sai ya ji ba zai iya fasa aurenta ba, komai runtsi.