Sashe 6
Kai Kafi Can Canta Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Na
JUT
0️⃣4️⃣
Bakura ya yi murmushi ya cewa yaron "yaya sunanka?"
Yaron ya ce "sunana Yahuza."
Sai Bakura ya ciro Naira dari biyar ya miqawa Yahuza. Ya ce "je ka ka sayi kunu kasha sadaka, sauran ka bawa almajirai 'yan uwanka."
Yahuza ya karba cike da murna ya na godiya.
Ya ce "ai gidanmu ne ni ba sai na saya ba sai dai in b'oye in yi dinkin sallah."
Bakura ya zabura ya ce "gidanku daya
Sajida kenan?"
Yahuza ya ce "yayata ce uwa daya, uba daya."
Sai Bakura ya yi turus, ya dubi Yahuza ya ga shi kamarsa daban, Sajida kamar ta daban.
Ya fada a ransa "to lallai kama ce kawai amma ba had'in Sajida da Zuhuriyya."
Bakura ya yi shiru can ya sake tunano fuskar Sajida ya taluna ta Zuhuriyya ya tabbatar sak kamarsu daya, sai ya girgiza kai.
Ya ce a ransa "ruwa baya tsami banza dole da wani boyayyen al' amari a nan."
Yahuza ya katse Bakura daga tunanin da yake yi, ya ce ga Babanmu nan ma ya fito."
Bakura ya dago da sauri ya dubi kofar gidansu Sajida sai ga wani tsoho a tsaye dauke da tafkekiyar dorina a hannunsa ta dukan almajirai. Daga ganin fuskarsa ba wasa, tsoho ne wanda baya son wargi.
Yahuza ya dubi Bakura ya ce "karka fada masa ka bani kudi dukana zai yi, zai ce ni na roqe ka, ya hana mu karbar kudi a hannun baqi."
Bakura ya yi murmushi ya ce "ba zan fada masa ba Yahuza."
Baban Yahuza ya kwalla masa kira, ya amsa ya tafi da sauri wajen mahaifinsa.
Mahaifin Yahuza yą dube shi cikin bacin rai da rashin sakin fuska, ya gyara dorinarsa tsaf tafka kawai yake so ya fara yi. Ya ce "ka san shi ne da za ka je ka naniqe masa, ko kiranka ya yi? Ba na hana ka zuwa wajen baqi kana yi musu surutun banza ba?"
Bakura ya qaraso da sauri ya ce "Baba ka da ka dake shi ba laifinsa ba ne, ni na kira shi na tambaye shi."
Baba ya dan saki fuskarsa ya cewa Yahuza "wuce gida."
Yahuza ya arta gida da gudu, dan har ya saddakar yau sai ya sha duka.
Baba tsoho har yanzu fuskarsa babu walwala ya dubi Bakura ya ce "yaro ina ka ke tambaya ne?"
Bakura ya ce "mahaifan Sajida na ke nema"
Wannan tambayar ta bawa Baba tsoho mamaki, ya dago da sauri ya dubi Bakura. Ya ce "kamar yaya mahaifan Sajida kake son gani, me ya faru?"
Ganin yadda tsohon nan ya razana, ya dimauta shine yasa Bakura ya kasa tambayar kwakwab din nan tasa.
Ya sosa qeya ya ce "an ce min kai ne Babanta ko?"
Baba ya ce "kwarai kuwa."
Bakura ya sake cewa "Babanta wanda ya haife ta ko?"
Baba ya tsuke fuska ya ce "kamar yaya?"
Bakura ya yi ajiyar zuciya ya ce "Baba abunda ya sa nake wannan tambayar ina da dalilina ka yi hakuri a hankali zaka ji komai. Shin mahaifiyar yarinyar nan Sajida ta na raye?"
Baba ya ce "ta na raye in dai ba wannan fitowar ta yanzu-yanzu ba rai yayi halinsa, dan yanzu na bar ta tana juya kunun kanwa. Me kake so ka ji ne yaro? Idan wani bayani ka ke da shi ka fada mana in ji, me ke tafe da kai?"
Bakura ya nisa sannan ya ce "Baba ba komai ba ne, sai dan ina son na sanar mu ku cewa ku na tufka ne wani ya na warwarewa. Ku na yiwa 'yarku tarbiyya wani ya na warware muku, magana na ke akan 'yarka Sajida da Abdul majid."
Sai tsoho ya dauki dogon salati ya ce "au, har yanzu Abdul majid bai rabu da yarinyar nan ba? Duk irin yaqin da mu ka yi da shi a baya. Lallai yau sai na lahira ya fita jin dadi."
Ya juya a fusace zai shiga gida.
Bakura ya tsayar da shi ya ce "na fada maka badan hankalinka ya tashi ba, haka kuma ba dan ka daki Sajida ba, sai don ka sake saka ido ku raba su. Duka ko zagi ba shine a'ala ba, ku yi mata nasiha kuma a karbe wayar hannunta don idan an hana ta fita ai ga waya. Ina da zafin rai kamar ka amma ban cika duka ba ko kuma ince ban taba dukan 'ya'yana ba, ina da tsoratarwa, ina yawan yi musu nasiha da wa'azi cewar su ji tsoron Allah su san duk inda suka shiga suka labe Allah na ganinsu, idan ni bana ganinsu."
Baba ya dubi Bakura ya ce "yaro na ji abinda ka ce, kuma na gode."
Ya juya ya shiga gida da sauri, Bakura ya shiga motarsa ya tafi gida.
*** *** ***
Ya na isa gida Auwalu mai gadinsa ne ya taso a guje ya wangale tafkeken get din shiga farfajivar gidan. Sanyin ni'ima da qamshin fulawoyi ne za su daki hancinka. Yayin da korayen fulawoyi da jajaye da ruwan dorawa da fararen furanni ne zasu dinga haskake kwayar idonka. A tsakiyar farfajiyar gidan wani round about aká yi shi da tiles amma an dankara fulawoyi a tsakiyarsa don haka akwai wani ruwa da yake bululowa ta ciki ya na tashi sama yana ban ruwa. Ga filin ajiyar motoci nan fiye da mota goma za su iya tsayawa a lokaci guda, gefe kuwa liluka ne a jejjere na wasan yara kai ka ce a 'Wander land Abuja' kake ( wajen wasan yara).
Tsuntsaye ne masu kyawun gaske suke kai kawo a farfajiyar gidan, kamar dawisu, talo-talo, jimina, aku, da 'yan qananun tsuntsaye masu launuka daban-daban, gefe kuwa qaton fili ne aka kewaye da birirruka da maguna da burguza-burguzan Karnuka irin na turawa masu gashi buzu- buzu gidan kowananansu akwai bangarensu akwai masu kula da su. Masu kula da filawowi dabam masu wanki da guga daban, direbobi daban-daban. A cikin gida kuwa mata masu aiki kala-kala, akwai makekiyar boy's quarter a bayan gidan akwai dakunan masu aiki burjik. sauke kunun da zafinsa."Kai ka fi cancanta 1
JUT
Paid book
0️⃣5️⃣
JUT
0️⃣4️⃣
Bakura ya yi murmushi ya cewa yaron "yaya sunanka?"
Yaron ya ce "sunana Yahuza."
Sai Bakura ya ciro Naira dari biyar ya miqawa Yahuza. Ya ce "je ka ka sayi kunu kasha sadaka, sauran ka bawa almajirai 'yan uwanka."
Yahuza ya karba cike da murna ya na godiya.
Ya ce "ai gidanmu ne ni ba sai na saya ba sai dai in b'oye in yi dinkin sallah."
Bakura ya zabura ya ce "gidanku daya
Sajida kenan?"
Yahuza ya ce "yayata ce uwa daya, uba daya."
Sai Bakura ya yi turus, ya dubi Yahuza ya ga shi kamarsa daban, Sajida kamar ta daban.
Ya fada a ransa "to lallai kama ce kawai amma ba had'in Sajida da Zuhuriyya."
Bakura ya yi shiru can ya sake tunano fuskar Sajida ya taluna ta Zuhuriyya ya tabbatar sak kamarsu daya, sai ya girgiza kai.
Ya ce a ransa "ruwa baya tsami banza dole da wani boyayyen al' amari a nan."
Yahuza ya katse Bakura daga tunanin da yake yi, ya ce ga Babanmu nan ma ya fito."
Bakura ya dago da sauri ya dubi kofar gidansu Sajida sai ga wani tsoho a tsaye dauke da tafkekiyar dorina a hannunsa ta dukan almajirai. Daga ganin fuskarsa ba wasa, tsoho ne wanda baya son wargi.
Yahuza ya dubi Bakura ya ce "karka fada masa ka bani kudi dukana zai yi, zai ce ni na roqe ka, ya hana mu karbar kudi a hannun baqi."
Bakura ya yi murmushi ya ce "ba zan fada masa ba Yahuza."
Baban Yahuza ya kwalla masa kira, ya amsa ya tafi da sauri wajen mahaifinsa.
Mahaifin Yahuza yą dube shi cikin bacin rai da rashin sakin fuska, ya gyara dorinarsa tsaf tafka kawai yake so ya fara yi. Ya ce "ka san shi ne da za ka je ka naniqe masa, ko kiranka ya yi? Ba na hana ka zuwa wajen baqi kana yi musu surutun banza ba?"
Bakura ya qaraso da sauri ya ce "Baba ka da ka dake shi ba laifinsa ba ne, ni na kira shi na tambaye shi."
Baba ya dan saki fuskarsa ya cewa Yahuza "wuce gida."
Yahuza ya arta gida da gudu, dan har ya saddakar yau sai ya sha duka.
Baba tsoho har yanzu fuskarsa babu walwala ya dubi Bakura ya ce "yaro ina ka ke tambaya ne?"
Bakura ya ce "mahaifan Sajida na ke nema"
Wannan tambayar ta bawa Baba tsoho mamaki, ya dago da sauri ya dubi Bakura. Ya ce "kamar yaya mahaifan Sajida kake son gani, me ya faru?"
Ganin yadda tsohon nan ya razana, ya dimauta shine yasa Bakura ya kasa tambayar kwakwab din nan tasa.
Ya sosa qeya ya ce "an ce min kai ne Babanta ko?"
Baba ya ce "kwarai kuwa."
Bakura ya sake cewa "Babanta wanda ya haife ta ko?"
Baba ya tsuke fuska ya ce "kamar yaya?"
Bakura ya yi ajiyar zuciya ya ce "Baba abunda ya sa nake wannan tambayar ina da dalilina ka yi hakuri a hankali zaka ji komai. Shin mahaifiyar yarinyar nan Sajida ta na raye?"
Baba ya ce "ta na raye in dai ba wannan fitowar ta yanzu-yanzu ba rai yayi halinsa, dan yanzu na bar ta tana juya kunun kanwa. Me kake so ka ji ne yaro? Idan wani bayani ka ke da shi ka fada mana in ji, me ke tafe da kai?"
Bakura ya nisa sannan ya ce "Baba ba komai ba ne, sai dan ina son na sanar mu ku cewa ku na tufka ne wani ya na warwarewa. Ku na yiwa 'yarku tarbiyya wani ya na warware muku, magana na ke akan 'yarka Sajida da Abdul majid."
Sai tsoho ya dauki dogon salati ya ce "au, har yanzu Abdul majid bai rabu da yarinyar nan ba? Duk irin yaqin da mu ka yi da shi a baya. Lallai yau sai na lahira ya fita jin dadi."
Ya juya a fusace zai shiga gida.
Bakura ya tsayar da shi ya ce "na fada maka badan hankalinka ya tashi ba, haka kuma ba dan ka daki Sajida ba, sai don ka sake saka ido ku raba su. Duka ko zagi ba shine a'ala ba, ku yi mata nasiha kuma a karbe wayar hannunta don idan an hana ta fita ai ga waya. Ina da zafin rai kamar ka amma ban cika duka ba ko kuma ince ban taba dukan 'ya'yana ba, ina da tsoratarwa, ina yawan yi musu nasiha da wa'azi cewar su ji tsoron Allah su san duk inda suka shiga suka labe Allah na ganinsu, idan ni bana ganinsu."
Baba ya dubi Bakura ya ce "yaro na ji abinda ka ce, kuma na gode."
Ya juya ya shiga gida da sauri, Bakura ya shiga motarsa ya tafi gida.
*** *** ***
Ya na isa gida Auwalu mai gadinsa ne ya taso a guje ya wangale tafkeken get din shiga farfajivar gidan. Sanyin ni'ima da qamshin fulawoyi ne za su daki hancinka. Yayin da korayen fulawoyi da jajaye da ruwan dorawa da fararen furanni ne zasu dinga haskake kwayar idonka. A tsakiyar farfajiyar gidan wani round about aká yi shi da tiles amma an dankara fulawoyi a tsakiyarsa don haka akwai wani ruwa da yake bululowa ta ciki ya na tashi sama yana ban ruwa. Ga filin ajiyar motoci nan fiye da mota goma za su iya tsayawa a lokaci guda, gefe kuwa liluka ne a jejjere na wasan yara kai ka ce a 'Wander land Abuja' kake ( wajen wasan yara).
Tsuntsaye ne masu kyawun gaske suke kai kawo a farfajiyar gidan, kamar dawisu, talo-talo, jimina, aku, da 'yan qananun tsuntsaye masu launuka daban-daban, gefe kuwa qaton fili ne aka kewaye da birirruka da maguna da burguza-burguzan Karnuka irin na turawa masu gashi buzu- buzu gidan kowananansu akwai bangarensu akwai masu kula da su. Masu kula da filawowi dabam masu wanki da guga daban, direbobi daban-daban. A cikin gida kuwa mata masu aiki kala-kala, akwai makekiyar boy's quarter a bayan gidan akwai dakunan masu aiki burjik. sauke kunun da zafinsa."Kai ka fi cancanta 1
JUT
Paid book
0️⃣5️⃣