← Book details Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 142

Sashe 87

Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin fargaba, Arɗo Bani yace.
"Allah rene Lamiɗo wannan yaron bai iya duka da ƙarfi bane? Ko dai ba bulalin masarautarku bace!?".
Wani irin kallo mai cike da mamaki da kuma tuhuma Lamiɗo yayi mishi.
Sai kuma dai ya kauda kanshi.
Ɗanzagi ne yace.
"Hattara dai Arɗo , Masarauta Joɗa sun wuce aro, zuba ido kaga ikon Allah".
Bulala ta bakwai ne, Jabeer ya ɗago ya tsulala mishi ita a gadon bayanshi.
Da sauri Ba'ana ya rufe ƙwayar idanunshi sabida wani irin tashi da yaji tsikar jikinshi yayi.
Tsikar jikinshi bai gama konciya ba, yakuma jin Jabeer ya rausa mushi wata bulaliyar, da sauri ya buɗe idonshi sabida.
Wani irin Yar-yar da yaji tsikar jikinshi tana zubawa duk gashin jikinshi ya miƙe tsaye.
Bai gama dawowa nazarin meyasa yakejin hakaba ya kuma jin wata bulaliyar.
A hankali yaji zufa ya fara keto mishi duk ta inda hudan gashin jiki yake a fatarsa.
Murmushi yakeyi har yanzu sabida bawai zafi yakeji ba, sai dai fargaba ta rufeshi, sabida jin alamun sihirurrukan jikinshine ke fecewa.
A haka Jabeer yayi ta tsula mishi bulala har zuwa bulala ta goma sha ɗaya.
Ata goma sha biyu ne, da ya tsula mishi yayi wani irin gantsarewa sabida wani irin azabebben ƙaiƙayi da yaji wurin yanayi mishi.
Da sauri yasa hannunshin a bayanshi alamun zai sosa.
Ife-ife da sowan da matasa suka farayi ne da Muryar Barmuji na cewa.
"Dokar gasa banda susa".
Da sauri ya dawo da hannunshin tare da cewa.
"To ya dane karatun da yakeyi, bana so, ya dena kira min sunan Allah".
Wata bulalar Sheykh ya zabgawa shege tare da cewa.
"Sunan uwarka zan kira maka in ban kira sunan Allah ba?".
Arɗo Bani kuwa wani irin ajiyan zuciya mai ƙarfi yaja.
Shi kuwa Ba'ana wani irin masifeffen ƙaiƙayi ne yakeji a duk inda Jabeer ya zuba mushi bulala, a bulala ta goma sha biyar ne, da aka zuba mushi.
Yayi wani irin gantsarewan da yafi na ɗazu.
Wani irin azabebben zafi da raɗadine yakeji yana tsarga mishi jiki da zuciya.
Zuface ta ketomishi tako wanne sashi na jikinshi.
Cikin sauri Jabeer ya juya bulalar ya amshi ta biyu ya haɗa data forkon.
Ya damƙesu a hannun hagunshi.
Wanda dama shi badamene kuma bahagone duk abinda hannun damanshi kan iya yi to na hagun yana fi iyawa.
Sai dai kasamcewarshi mutun mai ilimi da sanin addini shiyasa yake amfani da hadinsin nan da Manzon Allah ke cewa.
A cikin dukkan abinda zamuyi mu wakilta dama a forko, har dai sai in shiga bayan gidane aka ware shiga da ƙafar hagu.
To juya hannun yayi da hannun hagunshi, kana ya riƙe mahaɗin al'kyabbar jikinshi da hannun damanshi.
Gyara tsayuwarshi yayi kana ya ɗaga bulalar da ƙarfi ya zubawa Ba'ana a tsakiyar bayanshi.

Wani irin azabebben ihu mai ƙarfin amo da karaji Ba'ana ya kurma tare da fara karkarwa kar-kar tamkar mai farfaɗiya.
Ihun da ya kurmane yayi masifar tada hankalin dukkan kafurai magoya mayanshi.
Arɗo Bani kuwa a gabansu Lamiɗo ya tashi tsaye ya juya ya fuskanci al'ƙibila yayi sujjada.
Bappa ma da kanshi wani irin murmushin jin daɗi yakeyi.

Hakama duk sauran dottawan.
Shi kuwa Ba'ana wani irin azabebben kuma masifeffen zafi yakeji a dukkan sashin jikinshi.
Wani irin tsalle ya buga da ƙarfi lokacin da aka kumayi mishi bulala ta ashirin.
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi hatta Ba'anansa miƙewa tayi tana karkarwa, wata tafasashiyar zuface ta sinƙo mishi, zafi yakeji har cikin ƙoƙon kanshi da zuciyarshi.
Bulala ta ashirin da biyu akayi mishine yasashi fashewa da wani irin kuka mai azaban ƙarfi wani irin masifeffen fitinenne fitsarin azaba ya fara kwaranyo mishi, ihu mai cike da azaba yayi.
Wanda gaba ɗaya rugar saida kowa ya jiyoshi.
Ƙabilar ɓachama kuwa gaba ɗaya suma kuka suka saka.
Shi kuwa Ba'ana da ƙarfi ya faɗi ƙasa yana burbuwa, tamkar wanda yayi al'janu.
faɗuwanshi ƙasane yasa Jabeer rusunowa ya rinƙa tabka mishi bulalar, ihu da burbuwa da rarrafe alamun guduwa Ba'ana yakeyi cikin azaba da karaɗi da kuka yake cewa.
"Wayyo! Wayyo!! Wayyo Bonon!!! Ka ceceni zan mutu zai kasheni.
Wayyo Bononnnnnn! Yau bakayi min ranaba, ga bulalin karin sihirina sun iso gareni wayyoooooooo Bonon meyasa baka gaya minba na hudu tun kan wannan malamin ya kasheni ya karya min komai na jikina da sunan Allah."
Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da miƙewa tsaye ya fuskanci kudu. Ya ɗiba a guje ya ari ta kare ya nausa a guje.
Wani irin taku Jabeer yayi tare da biyoshi baya da sassarfa abunka da dogon mutun sai gashi ya isoshi a gigice ya fara kai mishi bulalin hagu da dama,
Jin azabar ta zarce azabar da yake zatone, yasa Ba'ana kurma ihu da kururuwan da yasa kab mutane suka nufosu.
Gudu yakeyi Jabeer na binshi yana zaneshi har ya fiddashi cikin taron gaba ɗaya.
Barmuji ne ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa.
"A dokar gasa Shaɗi in dai ya gudu ka bishi ka korashi cikin farfajiyar shike nan ya faɗi a gasa kaci.
Kuma bazai sake samun damar shiga gasarba bazai kuma sake zama a garinba."
Wani irin busar sarewa da al'gaita kana da kiɗe-kiɗen tsantsar farin ciki, al'ummar Rugar Bani suka farayi.
Sunayi suna zagaye Jabeer. Haroon kuwa da Arɗo Bani da Galadima miƙewa sukayi cikin farin ciki suka ruggumeshi.
Jamil, Jalal, Imran, Hashim, Sulaiman. Suma kab farin cikine ya cika musu zuƙata.
Laminu kuwa ji yakeyi tamkar ya shaƙo Jabeer ya karshi sai dai tabbas dama ya zaci aha dan shi mari ɗaya nema Sheykh ya masa ya kusan suma, shiyasa ya tausayawa Ba'ana.
Lamiɗo kuwa jinjina kai yakeyi yana tattausan murmushi.

Koda su Galadima suka ruggumeshi, Arɗo Bani kuwa kama hannunshi yayi ya ɗaga sama alamun yaci gasar Shaɗin.

A haka suka iso gaban Lamiɗo hannunshi yasa ya dafa kan Jabeer tare da sanya mushi al'barka.

Mutane kuwa duk an kacame da farin ciki.
Ya Salmanu kuwa kusan suma yayi tsabar masifar jin daɗi.
Alhamdulillah yau dai burinshi ya cika ya samu konciyar hankalin duniya an ɗauka musu fansa, shida masoyan Shatu na baya, harma da yayanshi.

Jan gefe makaɗan suka sabi, da sauran zugar jamar gari.

Jabeer kuwa mamaki yakeyi yadda yaga.
Fulani nata shigowa garin tako ina wasu bisa dawakai wasuma ƙan raƙuma.
Lamiɗo kuwa waya yakeyi da amalun a sirrance yake mgnar sabida ko Jabeer ɗin dake kusa dashi baya jinshi.

Bisa umarnin Arɗo Bani ne aka rinƙa fito da ƙwaran nono da fura da dambu da ƙwaran zuma,
Ana kawowa su Lamiɗo.

Wanda fadawa da dogarai ne sukasha.

A hankali Jabeer ya kalli Lamiɗo cikin gajiya yace.
"To ai sai ku tashi mu tafi ko!".
Shiru Lamiɗo yayi mishi, ganin hakane, ya gyara hiramin kanshi kana ya kuma cewa.
"Mu tafi ko".
Galadima ne yace.
"Ai bamu gamaba".
Cikin sauri Haroon yace.
"To meya rage kuma?".
Galadima ya buɗe bakin zai bashi amsa kenan. Sai kuma duk suka juyo suna kallon wasu tsala-tsalan motocine masu masifar kyau da tsada, suna shigowa Rugar Bani a jere-a jere. Cikin fidda numfashi Haroon ya ɗan kalli motocine da mamaki yace.
"Ha Jabeer kalli wannan kamar tawagar motocin Uncle Abdulkarim da Abudulfata kalli kamarfa harda Jadda". (Sarki Jalaluddin suke cewa Jadda)
Sai kuwa ya juyo ya kalli Lamiɗo cikin nitsuwa yace.
"Lamiɗo lfy kuwa?".
Kanshi ya gyaɗa mishi alamar eh Lfy kau.
Shi kuwa Sheykh Jabeer cikin nitsuwa yake kallon ayarin motocin a fakaice tabbas.
Su Jalaluddin ne da yaranshi. Kana ga kuma Baban Haroon, ga kuma su Dr Aliyu da Barrister Kamal da su Baba Basiru Baba Nasiru dama duk sauran manyan masarautarsu.
Da sauri ya juyo ya kalli Lamiɗo da nufin yin tambaya sai kuma yayi shiru ganin Lamiɗo na mgna da Galadima da kuma wani amintaccen bafadanshi.
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
"To wannan ƙus-ƙus du na menene, ku duk abinda babu kyau kuna jin daɗin yinshi."
Shiru yayi ganin motoci sama da talatin ne suka shigo Rugar.
Kana duk manyan mutanene kuma sun fito cikin motocin sun nufo inda suke zazzaune.
Wanda tuni Arɗo Bani yasa an kuma firfito da taburman cikin masallacin su.
Kana yasa an fito da sauran dardumai da kilisai anzo an shimfiɗa.

Suna isowa sarki Jalaluddin da Abba suka dafa kafaɗun Jabeer tare da sanya mushi al'barka kana suka zauna gefenshi ya zama sun sakashi a tsakiya.
Kusa dashi Abbanshi ya zauna,
Kana Jalaluddin ya zauna kusa da Abban.
Lamiɗo kuwa na kusa dashi shida Galadima.

Da sauri Haroon dasu Jamil kan sukabi bayan fadawan da suka nufi motocin da sukazo yanzu da ido.

Shi kuwa Sheykh Jabeer ido kawai ya zubawa wayarshi.
Yana wasu aiyukanshi a ciki.

A hankali ya ɗago kanshi ya kalli Haroon dake taɓashi.
Da yatsa Haroon ya nuna mishi gabanshi.
A hankali ya juya kanshi ya kalli inda Haroon ke nuna mishi.
Fadawane da hadimansu keta jido katon-katon ɗin sweet ga kuma fufun goro shima sunata jidowa suna ajiyewa a gabansu Arɗo Bani.

Cikin mamaki ya kalli Lamiɗo tare da cewa.
"Me za'ayi da wannan kuma? Kamar wanda suka zo ɗaurin aure!".
Da sauri Galadima yace.
"Eh ashe ka gane ai ɗaurkin auren ne".
Cikin mamaki Haroon yace.
"Aure kuma? To auren waye?".
Lamiɗo ne ya kalleshi cikin isa yace.
"Auren Muhammad Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa!".
Wani irin yunƙura Jabeer yayi zai miƙe, cikin tsananin haɗe fuskarnan tamkar zatayi aman jini ya kalli Lamiɗo tare da yunƙurin miƙewa yace.
"Zancen banza kenan a wurin banza, ai wlh baka isaba, wlh Lamiɗo kafa kiyayeni kanafa shigemin rayuwa, ka fita hanyata ka fice min a ido kar in rintsa da kai fa kadafa ka bari in juyo kanka".
Ya ƙarishe mgnar da miƙewa tsaye. Sai kuma ya juyo jin an kamo hannunshi an medashi zaune, a fusace ya kalli inda yaji anja hannun nashi ganin Sarki Jalaluddin ne ya riƙo hannunshi ya sashi kuma tsuke fuskarsa cikin faɗa yace.
"Jadda sakarmin hannu bana so! Bana son abinda kuke min da rayuwata, wlh gwarama kun tashi mun tafi, dan babu ruwana dan Ni bazanyi aure ba".
Da sauri ya juyo jin muryar Abbanshi yana cewa.
"...!
Chapter 87 · 0% Book details